Sashe 52
Tsaka Mai Wuya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yana jin Amma na ta yi ma Sadiq tambayoyi yana amsa mata da cewa sun gama karatu suna Hidimar kasa ne a zariya d'in. Suna cikin mganar ne Likita ya shigo ya duba Amma ya na fad'ama Sadiq bayan sun gaisa cewa Amma zata kai sati anan suna Bukatar ta kara Hutawa ya ce bakomai.
Bai jima ba ya fita bayan ya yi ma Amma yan Tambayoyi. Bayan fitan likita ba su jima ba suka yi mana Sallama suka fita Amma na ta saka albarka da addu'o'i.
Har waje na rakasu Tahir haraban Asibitin ys fita ya na jiran Sadiq da Tarin mamakin da ke ransa.
Nima dai godiyar na sake masa bai amsa ba kai tsaye yace"Kannen ki nawa ne?
Cikin mamaki nace"Ni?
Sai ya gyad'amin kai cikin natsuwa nace"kanwata d'aya ce Habiba wacce kuka gani. Mu hud'u Amma ta Haifa Adda Rukayya baka ganta ba sai Adda Fati wacce ka gani jiya sai ni sai Habiba."
Kai ya jinjina kafin yace"Ashe ba yarinya bace. Da kallon yar ficika na ke yi miki."
Maganarsa sai ta sakani Dariya kafata ya bi da kallo. Nima sai na bi in da ya ke kallo sanye na ke flat shoe baki na Habiba ne ma ya yi min yawa Tunda Habiba ta fi ni cikar tsokar kafa.
Kai tsaye yace"Wannan takalmin ba naki ba ne ko??
Ina yar dariya nace"eh na Habiba ne. Ammh ya aka yi ka gane ba nawa ba ne?
Yana mirmishi yace"Saboda kafarki ba ta boye takalmin ki."
Dariya na yi har hakora suka bayyana waje. Shima sai naga ya yi dariyan sai na shagala da kallonsa ganin yadda ya yi kyau kamar wata Daran goma sha Hud'u.
Cewa ya yi na koma ciki bari ya tafi muka yi sallama sai da na juya yaga wucewa sannan shima ya tafi.
Ko da yaje Tahir ya cika saura kadan ya fashe ya na cewa"mu je.'
Tahir ya balla masa Harara ya na Fad'in"Wai son zabiyar yarinyar nan ka ke yi ne Sadiq?
Cikin mamaki Sadiq yace"Sunanta Hasiya ba Zabiya ba."
Tahir ya yi dariya kafin yace"Wai Hasiya. Juz imanging fa, Sadiq ka fara son wannan yarinyar ne?
Sadiq ya yi gaba ya na fadin"Wani irin so kuma? Tahir ka rika saka Tunani in zaka yi mgana pls"
Tahir ya bi bayanshi ya na fadi'n"To na rasa gane maka. Yadda ka rasa sukuni Saboda Mutanen nan da yadda ka ke washe ma yarinyar nan baki Sadiq Sannan har da karyan su Umma da Abba sun rasu fa! Duk saboda menene ka ke aikata haka?
Kamar bazai yi mgana ba sai dai ya juya ya na kallon Tahir suka Tsaya a bakin asibiti suna kallon juna kafin yace"Tahir kasan taimako dabi'ata ce ba su ne na farko ba. kuma baza su zama na karshe ba. Baka ga su na bukatar neman taimako ba ne?sannan da ka ke mganar so? Son wa? Wannan yarinyar ne zan so? Bata cikin Tsarin matan da ni ke so Tahir."
Tahir yace"Na ji ba sonta ka ke yi ba. Taimako ne. To kashe su Umma da kayi da ran su ba da karyan asalin da ka yi musu fa?
Sadiq yace"Ba karya na yi ba ni asalina dan Shinkafi ne tunda nan ne Tushena. Su Umma kuma ban san Dalili ba kai ma kasan ba kowa ya ke sanin hakikanin waye ni ba."
Daga haka ya wuce Tahir ya rike kugu ya na bin bayansa da kallo cikin mamaki. Haka kurun ya ke ji aransa Wani abu zai faru wanda ba Daidai ne ba shi fa mutanen ba su yi masa ba. Wasu kamar yan gudun Hijira ita kuma yarinya farinta ne baya so kamar wata Zabiya.
Bayansa ya bi ammh ba su kara tada mganar ba. Mashin suka samu zuwa gida kuma har suka kwanta Tahir bai kara yi ma Sadiq mgana ba sai dai ya na kallonsa ya na nazarinsa.
Yana fatan Allah yasa ba garin taimako Sadiq zai jajbo ma kansa Wahala ba.
Washegari kafin Sadiq ya tafi wajen aiki yaji yana jin cin Danwake kamar yadda aka saba da kansa yaje da karamar kularsa. Da datti ya ci karo tun kafin ya kirasa yazo da Sauri ya na Fad'in"Danwake zaka siya?
Ya gyada masa kai da Sauri Datti yace"Ba'a yi mai Danwaken mamanta ba ta da lafiya. Suna asibiti har yanzu ba su dawo ba."
Shuru ya yi ya na nazari kafin ya yi mirmishi ya Dafa kan Datti naira Dari ya zaro daga Aljihunsa ya bashi ya tafi ya na tsallen Murna.
Bai damu ba har ya juya zai tafi sai mganar yaron ta kara Dawo masa sai ya tsaya bayan ya juyo ya na kare ma gidan kallo kamar gidan kamar kuma ba nan ba ne.!
Domin kore mamaki ya ga Salihi na gara taya zai shiga gidan sai ya kwala masa kira sannan ya fitosa da Hannunsa. Saninsa ya na ba da kudi yasa Salihi ya zo da Sauri bakinsa washe yace"Ba'a Danwake yau."
Da Sauri yace"Na sani. Y
ya sunan mai yin danwaken?
Salihi yace"Adda Hasiya."
Sadiq ya maimaita"Hasiya."
Salihi yace"Eh mamanta ba ta da lafiya suna asibitin in ji mamanmu."
Sadiq ya cika da mamaki sai dai bai bari Salihi ya tafi haka ba shima darin ya ba shi ya tafi ya na ta murna.
Sadiq na tafiya a hanya ya na Mirmishi har da Dariya shi kad'ai.
"Hasiya mai danwake."
Tabdijam.
Daga alamunsu daman ba su da Hali Talakawa ne. Ammh ina mahaifin su? Me ya asalin su? Duk wad'anan amasoshin ba shi da mai amsa masa shi.
Ammh har ya koma dakin su yana Dariyan sunan Hasiya da ya maida mata da Hasiya mai Danwake.
*******
Sai da Amma tayi sati Cur sannan aka sallameta Lokacin ta samu sauki sosai ta na zuwa bayi da kanta. Sannan ta sallolinta a Tsaye ta samu karfin jiki.
Ba bu abunda zan ce ma Abubakar sai Godiya. Domin komai na laluran asibitin nan shi ya yi mana shi hatta kudin gado da sauran magungunan da aka sake rubutama Amma shi ya siya.
Sannan ya samo mana adaidaita ta Dauke damu da kayanmu har gida shi kuma yabi bayanmu a kan Babur.
Da farko ya ki shiga ciki sai da na matsa sannan ya shiga har daki ya Duka ya kara gaida Amma.
Amma ta rike hannuwansa ta na fadin"D'an nan ina ka samu kudade da ka yi ta mana wannan Hidimar?.
Kai tsaye yace"Amma ba na gaya miki ina Hidimar kasa ba? To ai gwammati na ba mu wasu kudi duk karshen wata."
Ina zai gayamusu Abba ne komai na shi tunda ya riga yace ba shi da iyaye shi maraya ne.
Amma ta shiga kwarara add'au tana ma iyayensa da suka rasu addu'a da samun salama.
Har sai da ta yi hawaye ganin haka yasa ya ce"Amma bakomai. Ki daina kuka."
Dole Amma ta yi shuru ta na ta saka masa albarka.
Da zai tafi ni na rakasa ina ganin Matan gidanmu kallo kamar zasu fad'i.
Sai da muka fito ya kalleni ya na Fad'in"Gidan ku kuna da yawa haka ne?
Kai tsaye nace"Gidan haya ne .mata goma sha uku ne aciki, Dogon gida kenan."
Sadiq ya jinjina kai kafin yace"Dogon gida kad'ai ake kiransa?
Na gyada masa kai ina fad'in"Eh."
Kai Tsaye ya na kallo na yace"ba'a cewa gidan su Hasiya mai Danwake."
Zaro ido na yi ina kallonsa shi kuma yana Dariya yace"Amma ta ji sauki a cigaba da yi ma na Danwaken mu"
Cikin mamaki nace"Ya aka yi kasan ina Danwake?
Kai Tsaye yace"Ina siya ne."
Cikin kura masa ido nace"Ka na siya?
Kai ya gyad'amin ya na mirmishi.
Kamar an tunamin na nuna sa ya na Fad'in"Kai ne daman me zuwa da kula da Dubu daya har ka ke barin min chanji."
Bai amsani ba sai da ya yi mirmishi da yasa na gane shi ne. Kallonsa na ke yi nima cikin jin dad'in kafin nace"ka ci sunan ka. Masu suna Abubakar Sadiq ma su tausayi ne da yakana ma su jinkai ne da Taimako."
Na fad'a kai na Tsaye ina kallonsa Idanuwana suna faman cika da kwallah da tuna wani bangare na Rayuwata.
Shi kuma sai ya tsaya ya na mamakin mganata cikin sigar tambaya yace"Kin san wani mai irin sunana ne?
Kai na gyad'a masa ina fadin"Sosai ma kuwa. Shima kamar ka ya ke ga Kirki ga Tausayi Fara'a sanin ya kamata yakana jin kai da Dattako. Duka ya na da shi shima."
Na fad'a hawaye sun cikamin kwarmin idanuwana ina son Abubakar ammh kaddara ta rabani da shi.
Kai tsaye yace"Saurayin ki ne?
Sai lokacin na dawo Tunanina da Sauri nace"A'a.."
Na kauda fuskata ganin yasa bai tsawaita mganar ba. Ya yi min sallama zai tafi nima kuma daman na kosa na koma gida an fara wucewa ana kallon mu.
Kuma nasan mamakin ganina da wani ake yi wasu har suna yi ma Abubakar kallon Tausayi.
Sun zata Saurayina ne.
Ko da na koma gida sai kuzarina ya Ragu bayi na shiga na ci kuka na kamar bazan daina. Ina kewar Abubakar kewa mai yawa sai dai ina yi masa Fatan alheri a duk inda ya samu kansa.
Tunda har Sadiq na son Danwake yasa na gayama Amma zan cigaba Saboda shi. Amma tace ko shi kad'ai sai a rika yi masa ya na zuwa ya karb'a ya Chanchanta.
Washegari kad'an na yi namu na gida da na shi ina ta Allah Allah yazo to bai dawo ba sai bayan kwana Biyu ya zo Duba Amma.
Amma da kanta ta fad'a masa na yi masa Danwake shekaranjiya bai zo ba.
Cikin natsuwarsa yace"wani uzuri ne ya hanani zuwa Amma."
Bai jima ba ya fita bayan ya yi ma Amma yan Tambayoyi. Bayan fitan likita ba su jima ba suka yi mana Sallama suka fita Amma na ta saka albarka da addu'o'i.
Har waje na rakasu Tahir haraban Asibitin ys fita ya na jiran Sadiq da Tarin mamakin da ke ransa.
Nima dai godiyar na sake masa bai amsa ba kai tsaye yace"Kannen ki nawa ne?
Cikin mamaki nace"Ni?
Sai ya gyad'amin kai cikin natsuwa nace"kanwata d'aya ce Habiba wacce kuka gani. Mu hud'u Amma ta Haifa Adda Rukayya baka ganta ba sai Adda Fati wacce ka gani jiya sai ni sai Habiba."
Kai ya jinjina kafin yace"Ashe ba yarinya bace. Da kallon yar ficika na ke yi miki."
Maganarsa sai ta sakani Dariya kafata ya bi da kallo. Nima sai na bi in da ya ke kallo sanye na ke flat shoe baki na Habiba ne ma ya yi min yawa Tunda Habiba ta fi ni cikar tsokar kafa.
Kai tsaye yace"Wannan takalmin ba naki ba ne ko??
Ina yar dariya nace"eh na Habiba ne. Ammh ya aka yi ka gane ba nawa ba ne?
Yana mirmishi yace"Saboda kafarki ba ta boye takalmin ki."
Dariya na yi har hakora suka bayyana waje. Shima sai naga ya yi dariyan sai na shagala da kallonsa ganin yadda ya yi kyau kamar wata Daran goma sha Hud'u.
Cewa ya yi na koma ciki bari ya tafi muka yi sallama sai da na juya yaga wucewa sannan shima ya tafi.
Ko da yaje Tahir ya cika saura kadan ya fashe ya na cewa"mu je.'
Tahir ya balla masa Harara ya na Fad'in"Wai son zabiyar yarinyar nan ka ke yi ne Sadiq?
Cikin mamaki Sadiq yace"Sunanta Hasiya ba Zabiya ba."
Tahir ya yi dariya kafin yace"Wai Hasiya. Juz imanging fa, Sadiq ka fara son wannan yarinyar ne?
Sadiq ya yi gaba ya na fadin"Wani irin so kuma? Tahir ka rika saka Tunani in zaka yi mgana pls"
Tahir ya bi bayanshi ya na fadi'n"To na rasa gane maka. Yadda ka rasa sukuni Saboda Mutanen nan da yadda ka ke washe ma yarinyar nan baki Sadiq Sannan har da karyan su Umma da Abba sun rasu fa! Duk saboda menene ka ke aikata haka?
Kamar bazai yi mgana ba sai dai ya juya ya na kallon Tahir suka Tsaya a bakin asibiti suna kallon juna kafin yace"Tahir kasan taimako dabi'ata ce ba su ne na farko ba. kuma baza su zama na karshe ba. Baka ga su na bukatar neman taimako ba ne?sannan da ka ke mganar so? Son wa? Wannan yarinyar ne zan so? Bata cikin Tsarin matan da ni ke so Tahir."
Tahir yace"Na ji ba sonta ka ke yi ba. Taimako ne. To kashe su Umma da kayi da ran su ba da karyan asalin da ka yi musu fa?
Sadiq yace"Ba karya na yi ba ni asalina dan Shinkafi ne tunda nan ne Tushena. Su Umma kuma ban san Dalili ba kai ma kasan ba kowa ya ke sanin hakikanin waye ni ba."
Daga haka ya wuce Tahir ya rike kugu ya na bin bayansa da kallo cikin mamaki. Haka kurun ya ke ji aransa Wani abu zai faru wanda ba Daidai ne ba shi fa mutanen ba su yi masa ba. Wasu kamar yan gudun Hijira ita kuma yarinya farinta ne baya so kamar wata Zabiya.
Bayansa ya bi ammh ba su kara tada mganar ba. Mashin suka samu zuwa gida kuma har suka kwanta Tahir bai kara yi ma Sadiq mgana ba sai dai ya na kallonsa ya na nazarinsa.
Yana fatan Allah yasa ba garin taimako Sadiq zai jajbo ma kansa Wahala ba.
Washegari kafin Sadiq ya tafi wajen aiki yaji yana jin cin Danwake kamar yadda aka saba da kansa yaje da karamar kularsa. Da datti ya ci karo tun kafin ya kirasa yazo da Sauri ya na Fad'in"Danwake zaka siya?
Ya gyada masa kai da Sauri Datti yace"Ba'a yi mai Danwaken mamanta ba ta da lafiya. Suna asibiti har yanzu ba su dawo ba."
Shuru ya yi ya na nazari kafin ya yi mirmishi ya Dafa kan Datti naira Dari ya zaro daga Aljihunsa ya bashi ya tafi ya na tsallen Murna.
Bai damu ba har ya juya zai tafi sai mganar yaron ta kara Dawo masa sai ya tsaya bayan ya juyo ya na kare ma gidan kallo kamar gidan kamar kuma ba nan ba ne.!
Domin kore mamaki ya ga Salihi na gara taya zai shiga gidan sai ya kwala masa kira sannan ya fitosa da Hannunsa. Saninsa ya na ba da kudi yasa Salihi ya zo da Sauri bakinsa washe yace"Ba'a Danwake yau."
Da Sauri yace"Na sani. Y
ya sunan mai yin danwaken?
Salihi yace"Adda Hasiya."
Sadiq ya maimaita"Hasiya."
Salihi yace"Eh mamanta ba ta da lafiya suna asibitin in ji mamanmu."
Sadiq ya cika da mamaki sai dai bai bari Salihi ya tafi haka ba shima darin ya ba shi ya tafi ya na ta murna.
Sadiq na tafiya a hanya ya na Mirmishi har da Dariya shi kad'ai.
"Hasiya mai danwake."
Tabdijam.
Daga alamunsu daman ba su da Hali Talakawa ne. Ammh ina mahaifin su? Me ya asalin su? Duk wad'anan amasoshin ba shi da mai amsa masa shi.
Ammh har ya koma dakin su yana Dariyan sunan Hasiya da ya maida mata da Hasiya mai Danwake.
*******
Sai da Amma tayi sati Cur sannan aka sallameta Lokacin ta samu sauki sosai ta na zuwa bayi da kanta. Sannan ta sallolinta a Tsaye ta samu karfin jiki.
Ba bu abunda zan ce ma Abubakar sai Godiya. Domin komai na laluran asibitin nan shi ya yi mana shi hatta kudin gado da sauran magungunan da aka sake rubutama Amma shi ya siya.
Sannan ya samo mana adaidaita ta Dauke damu da kayanmu har gida shi kuma yabi bayanmu a kan Babur.
Da farko ya ki shiga ciki sai da na matsa sannan ya shiga har daki ya Duka ya kara gaida Amma.
Amma ta rike hannuwansa ta na fadin"D'an nan ina ka samu kudade da ka yi ta mana wannan Hidimar?.
Kai tsaye yace"Amma ba na gaya miki ina Hidimar kasa ba? To ai gwammati na ba mu wasu kudi duk karshen wata."
Ina zai gayamusu Abba ne komai na shi tunda ya riga yace ba shi da iyaye shi maraya ne.
Amma ta shiga kwarara add'au tana ma iyayensa da suka rasu addu'a da samun salama.
Har sai da ta yi hawaye ganin haka yasa ya ce"Amma bakomai. Ki daina kuka."
Dole Amma ta yi shuru ta na ta saka masa albarka.
Da zai tafi ni na rakasa ina ganin Matan gidanmu kallo kamar zasu fad'i.
Sai da muka fito ya kalleni ya na Fad'in"Gidan ku kuna da yawa haka ne?
Kai tsaye nace"Gidan haya ne .mata goma sha uku ne aciki, Dogon gida kenan."
Sadiq ya jinjina kai kafin yace"Dogon gida kad'ai ake kiransa?
Na gyada masa kai ina fad'in"Eh."
Kai Tsaye ya na kallo na yace"ba'a cewa gidan su Hasiya mai Danwake."
Zaro ido na yi ina kallonsa shi kuma yana Dariya yace"Amma ta ji sauki a cigaba da yi ma na Danwaken mu"
Cikin mamaki nace"Ya aka yi kasan ina Danwake?
Kai Tsaye yace"Ina siya ne."
Cikin kura masa ido nace"Ka na siya?
Kai ya gyad'amin ya na mirmishi.
Kamar an tunamin na nuna sa ya na Fad'in"Kai ne daman me zuwa da kula da Dubu daya har ka ke barin min chanji."
Bai amsani ba sai da ya yi mirmishi da yasa na gane shi ne. Kallonsa na ke yi nima cikin jin dad'in kafin nace"ka ci sunan ka. Masu suna Abubakar Sadiq ma su tausayi ne da yakana ma su jinkai ne da Taimako."
Na fad'a kai na Tsaye ina kallonsa Idanuwana suna faman cika da kwallah da tuna wani bangare na Rayuwata.
Shi kuma sai ya tsaya ya na mamakin mganata cikin sigar tambaya yace"Kin san wani mai irin sunana ne?
Kai na gyad'a masa ina fadin"Sosai ma kuwa. Shima kamar ka ya ke ga Kirki ga Tausayi Fara'a sanin ya kamata yakana jin kai da Dattako. Duka ya na da shi shima."
Na fad'a hawaye sun cikamin kwarmin idanuwana ina son Abubakar ammh kaddara ta rabani da shi.
Kai tsaye yace"Saurayin ki ne?
Sai lokacin na dawo Tunanina da Sauri nace"A'a.."
Na kauda fuskata ganin yasa bai tsawaita mganar ba. Ya yi min sallama zai tafi nima kuma daman na kosa na koma gida an fara wucewa ana kallon mu.
Kuma nasan mamakin ganina da wani ake yi wasu har suna yi ma Abubakar kallon Tausayi.
Sun zata Saurayina ne.
Ko da na koma gida sai kuzarina ya Ragu bayi na shiga na ci kuka na kamar bazan daina. Ina kewar Abubakar kewa mai yawa sai dai ina yi masa Fatan alheri a duk inda ya samu kansa.
Tunda har Sadiq na son Danwake yasa na gayama Amma zan cigaba Saboda shi. Amma tace ko shi kad'ai sai a rika yi masa ya na zuwa ya karb'a ya Chanchanta.
Washegari kad'an na yi namu na gida da na shi ina ta Allah Allah yazo to bai dawo ba sai bayan kwana Biyu ya zo Duba Amma.
Amma da kanta ta fad'a masa na yi masa Danwake shekaranjiya bai zo ba.
Cikin natsuwarsa yace"wani uzuri ne ya hanani zuwa Amma."