Sashe 68
Tsaka Mai Wuya Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Ya jima Tsaye a wajen ya na sauke Numfashi kamar mai ciwon Asthma.
Wata zuciyar tace"Anya Sadiq abunda zaka aikata daidai ne? Baka ganin cin Amanar yardan iyayenka ne?
To ammh ya zai yi? Tausayi ne ya cikamasa Kirjin da ya kasa tankwafar da wannan Rokon sai dai yana da nashi lTsarin da Sharadin har ya yi wannan abun ya gama shi babu wanda zai sani daga cikin wani Ahalinsa sai Tahir shi kuma yasan in ba shi yace ya yi mgana ba Tahir bazai taba cema kowa komai ba.
Da haka ya gangara ya koma ya na zuwa ya ga Tahir har ya fito shima cikin Shigan manyan kaya. Kofar su suka kule sannan suka fara Tafiya
Tahir ya dauka bakin Titi suka nufa ammah sai yaga sun nufi cikin anguwa.
Kai Tsaye yace"Ya na ga haka? Ba abun hawa zamu hau ba?
Sadiq na cin mgani yace"A'a."
Tahir ya kallesa bai samu zarafin mgana ba yaga Sadiq ya ciro wani bakin glass mai Duhuwa ya kwafa a Fuskarsa saboda batar da k'wayan idanuwansa da zasu bayyana asirin yanayin da ya ke ciki.
Tahir ya saki baki kafin yace"Wannan bakin Gilashin fa?
Sadiq ya yi kamar bai ji sa ba ya cigaba da Tafiya, shi dai Tahir yaga an zo wajen Taron jama'a bai gani ba sai da yaga sun tsaya a kofar wani Rubabben gida Dagargajajje.
Cikin mamaki ya kara kallon Sadiq kafin yace"Ina ne nan?
Kai Tsaye Sadiq yace"In da zamu zo mana."
Tahir ya bude baki kafin yace"Nan ne wajen daurin auren?
Sadiq ya gyad'aa masa kai lokaci d'aya ya na kwalama Salihi kira da ya gansu suna wasa a kofar gida ganin shi yasa har da Datti suka Rugo da gudu Sanin ya na ba da kudi.
Suna Rige rigen gaisheshi ya amsa ba Sakewa kai tsaye yace"Ku shiga ciki ku fad'ama Maman Hasiya Abubakar na mgana a waje."
Yaran suka kwashi gudu zuwa cikin gida Tahir ko mamaki ya sandarar da shi jin sunan da ya ambata kara bin gidan ya yi da kallo kafin ya Dawo da kallon kan Sadiq da baya ganin kwayar idanuwanshi saboda gilashin da ya saka.
Cikin mamakinsa Tahir yace"Nan ne gidan su Hasiyan kenan?
Sadiq ya gyad'a masa kai Tahir ya yi kwafa kafin yace"Tsakani ga Allah mu da zamu Daurin aure me ya kawo mu nan?
Sadiq ya yi shuru kafin yace"Nan ne wajen Daurin aure"
Tahir yace"Nan ne wajen Daurin auran? Ya fad'a cikin Sigan Tambaya again kuma Sadiq ya gyad'a masa kai.
Mamaki dai ko takaici zan ce ya kusa kashe Tahir a tsaye.
Cikin karin mamaki ya kara cewa"To waye zai yi aure?
Sadiq na kallon kasa muryansa ta yi kasa kafin yace
"NI.."
A Firgice Tahir ya Dago ya na kallonsa Daidai Lokacin da Amma ta fito ba ko Hijabi sai zaninta da tayi lullubi da shi Domin ta na zaune ne daman tana zaman jiran Tsammani sai ga su Salihi da sako.
Duk muna zaune adakin Amma Sakon yazo abunda ya bamu mamaki tashin Amma da Sauri da fitan ta batare da ta jira cewar komai ba yasa ta fita ta barmu baki sake cikin zullumi da Tunanin lafiya.
Ni kuma Tunda naji sunan wanda aka ambata gabbaina suka saki a tare. Abunda bai saba gani ba ne na gani yau ya saba indai yazo sai dai yace a kirani ammh yau Amma yace a kira kai Tsaye kenan tabbas akwai wani abu a kasa wanda ban sani ba.
Achan waje kuwa Amma na fita Taga Sadiq ba ta ko tsaya lura da Tahir ba ta karisa gabanshi ta na fad"in"Daman na sani. Ina da kyakyawan tabbacin zaka Dawo Abubakar"
Ta fad'a Lokaci d'aya ta na mirmishi.
Dagowa ya yi ya na kallonta sai dai Rauni da kukan UWA shi ne suka Dawo da shi sai kuma Tausayinsu gabadaya.
Cikin wani irin yanayi yace"Nazo da abunda kika bukata Amma meye abu na gaba?
Amma ta daga hannuwanta sama tace"Alhamdulillah. Alhamdulillah.! Allah na gode maka"
Sai kawai ta fashe da kuka ta na neman zubewa a kasa da Sauri Sadiq ya riketa kafin ta kai kasa kada ta tara masa Mutane.
Cikin kukan ta ke fad'in"Nagode Allah ya yi maka albarka. Yadda kaji kaima kaima Allah ya jikan ka, Allah ya haskaka Rayuwarka da Alheri Allah ya baka abunda kake nema Duniya da Lahira Allah ya tsareka a duk in da ka ke Allah ya sanya albarka acikin Niyyar ka ta Alheri."
Amma ta ke fad'a ta na kuka ga hawaye Shabe shabe Sadiq yasa Hannu ya share mata hawaye ya na fadin"Bakomai Amma."
Amma ta rike Hannuwansa ta jimke ta na fadin"Yadda ka share ma wannan UWAR hawayenta Allah ya share maka naka. Yadda ka sanyaya ma wannan Uwar zuciya kai ma Allah ya sanyaya maka taka zuciyar, Yadda ka duba lamarin wannan Uwar kai ma Ina Rokon Allah ya cigaba da Duba Lamarinka har Abada."
Sadiq na ta amsawa da Ameen Tahir ko ga shi nan Tsaye ya na ji kuma ya na gani ammh ya rasa gane ina aka dosa.
Amma ta na share hawayenta ta juya ta na fadin"Ina zuwa."
Cikin gida ta koma da Sauri duk muma Daki ta daga labule ta na kiran Sunan Adda Fati, ta mike ta na Fadin"Na zo ne Amma?
Kai ta gyada mata da Sauri ta mike ta fita ni da Ramatu muka kalli juna bamu da amsar da tambayar da ke zuciyarmu.
Suna Fita Gefe Amma taja Adda Fati tace ta yi maza ta kira mata Babammu Tanko ta na so ta yi mgana da shi.
Ba musu Adda fati ta latso lambarsa ta kirasa daman wayar na Hannunta sai da ta kira kusan sau uku sannan ya Dauka daman ita ta na da lambobin su ta na kiran su ta na gaishe su ko da su sun yada mu suna da Hakki muma mu bi mu yi zumumci da su.
Bayan sun gaisa tace masa Amma ke son mgana da shi nan da nan ya bata rai duk da ya jima rabon da yaji ta nemesa yasan kila wani abu take Bukata sai dai zencen ya sha Bambam ta na karban wayar ta yi ma Adda mgana da Hannu alamun ta bata waje.
A gurguje suka gaisa har ya fara Tsumewa ya zata ko wani taimako ta ke nema sai yaji ta fara rattaba masa wani jawabin da yasa ya d'an Saki Fuska cikin Sauri yace"Ina gida za su iya karisowa Aisha."
Daga haka Amma ta yi masa godiya suka yi sallama.
Abun mamaki Amma ta shigo Dakin nan bakinta a washe Adda Fati ta mikama wayarta Lokaci daya ta na Fadin"Fati ta shi ki shirya akwai baki a waje gidan Babanku Tanko zaki raka su yanzu."
Ni da Adda Rukayya muka had'a baki wajen fad'in"Gidan Baba Tanko kuma?
Cikin Alamun Sigar Tambaya. Amma ta gyada kai fuskarta na bayyanar da Annuri Adda Fati ba musu ta mike ta na Saka Hijabinta Hanifa na Hannuna ta yi barci sai tace na riketa bari ta Dawo Ta na fita Inna Talatu ta kalli Amma ta na fadin"Lafiya dai ko?
Amma na mirmishi tace"Sai Alheri in sha Allahu."
Adda Rukayya tace"Amma ko an fasa Tafiyar ne?
Amma ta kalleta kafin tace"A'a ban fasa ba sai dai kila tafiyar ne zata sauya daga ni da Hasiya zuwa ni kad'ai."
A tare muka kalleta ni dai sai da gabana ya amsa Ramatu ta washe baki kafin tace"Yauwa Amma ki bar mana Hasiya tare damu"
Amma na mirmishi tace"In sha Allahu Ramatu."
Amma fa ta bama kowa mamaki kudi tace na bata naira Dubu biyu na Dauko na bata ita kuma ta aiki Habiba shago ta siyo mata Cimgam da Minti.
Inna talatu ne sai da ta maganta cikin mamaki tace"Tashin ne har da rabon su Minti?
Amma tace"Wannan na Dabam ne Talatu."
Ni dai zaune na ke rike da Hanifa ammh ba na cikin Hayyacina.
Ina jin Ramatu na fad'in"Kawata nan Amma zata bar min ke"
Ta fad'a cikin Farimciki da Annushuwa kallonta kawai na yi ammh ni nasan a raina ba abunda take tunanina ba ne.
Abun mamaki me yasa Amma tace a raka su Assadiq wajen Baba Tanko?
*******
Ita kanta Adda Fati ta yi mamakin ganin Sadiq sai dai ba ta samu zarafin jin ba'asi ba gaisawa kawai suka yi tace su je Amma tace ta yi musu jagora zuwa gidan Babansu Tanko.
Sadiq sai da ya riko hannun Tahir da ya tsaya ya kasa bin su saboda ya na neman karin bayani.
Adaidaita suka samu suka hau har Babban Dodo. Ita ta fara shiga cikin gidan zuwa wani Lokaci sai ga Baba Tankon ya fito da kanshi.
Sadiq bai tsaya ma kallonsa ba yadai san Datiijo ne Hannu ya ba su suka yi musabaha kafin ya jazasu zuwa cikin Falon gidansa da ke da kofa ta waje.
Suna shiga ya fita ya barsu Tahir ya juyo ya na kallon Sadiq kafin yace"Zaka yi min bayanin meke faruwa ne ko zaka cigaba da barina cikin Duhu.?
Sadiq Kai tsaye yace"An kusa zuwa gabar da zaka san komai."
Shuru suka Cigaba da zama sai chan kuma sai ga shi ya dawo da wasu mutane kamar goma haka.
Wata zuciyar tace"Anya Sadiq abunda zaka aikata daidai ne? Baka ganin cin Amanar yardan iyayenka ne?
To ammh ya zai yi? Tausayi ne ya cikamasa Kirjin da ya kasa tankwafar da wannan Rokon sai dai yana da nashi lTsarin da Sharadin har ya yi wannan abun ya gama shi babu wanda zai sani daga cikin wani Ahalinsa sai Tahir shi kuma yasan in ba shi yace ya yi mgana ba Tahir bazai taba cema kowa komai ba.
Da haka ya gangara ya koma ya na zuwa ya ga Tahir har ya fito shima cikin Shigan manyan kaya. Kofar su suka kule sannan suka fara Tafiya
Tahir ya dauka bakin Titi suka nufa ammah sai yaga sun nufi cikin anguwa.
Kai Tsaye yace"Ya na ga haka? Ba abun hawa zamu hau ba?
Sadiq na cin mgani yace"A'a."
Tahir ya kallesa bai samu zarafin mgana ba yaga Sadiq ya ciro wani bakin glass mai Duhuwa ya kwafa a Fuskarsa saboda batar da k'wayan idanuwansa da zasu bayyana asirin yanayin da ya ke ciki.
Tahir ya saki baki kafin yace"Wannan bakin Gilashin fa?
Sadiq ya yi kamar bai ji sa ba ya cigaba da Tafiya, shi dai Tahir yaga an zo wajen Taron jama'a bai gani ba sai da yaga sun tsaya a kofar wani Rubabben gida Dagargajajje.
Cikin mamaki ya kara kallon Sadiq kafin yace"Ina ne nan?
Kai Tsaye Sadiq yace"In da zamu zo mana."
Tahir ya bude baki kafin yace"Nan ne wajen daurin auren?
Sadiq ya gyad'aa masa kai lokaci d'aya ya na kwalama Salihi kira da ya gansu suna wasa a kofar gida ganin shi yasa har da Datti suka Rugo da gudu Sanin ya na ba da kudi.
Suna Rige rigen gaisheshi ya amsa ba Sakewa kai tsaye yace"Ku shiga ciki ku fad'ama Maman Hasiya Abubakar na mgana a waje."
Yaran suka kwashi gudu zuwa cikin gida Tahir ko mamaki ya sandarar da shi jin sunan da ya ambata kara bin gidan ya yi da kallo kafin ya Dawo da kallon kan Sadiq da baya ganin kwayar idanuwanshi saboda gilashin da ya saka.
Cikin mamakinsa Tahir yace"Nan ne gidan su Hasiyan kenan?
Sadiq ya gyad'a masa kai Tahir ya yi kwafa kafin yace"Tsakani ga Allah mu da zamu Daurin aure me ya kawo mu nan?
Sadiq ya yi shuru kafin yace"Nan ne wajen Daurin aure"
Tahir yace"Nan ne wajen Daurin auran? Ya fad'a cikin Sigan Tambaya again kuma Sadiq ya gyad'a masa kai.
Mamaki dai ko takaici zan ce ya kusa kashe Tahir a tsaye.
Cikin karin mamaki ya kara cewa"To waye zai yi aure?
Sadiq na kallon kasa muryansa ta yi kasa kafin yace
"NI.."
A Firgice Tahir ya Dago ya na kallonsa Daidai Lokacin da Amma ta fito ba ko Hijabi sai zaninta da tayi lullubi da shi Domin ta na zaune ne daman tana zaman jiran Tsammani sai ga su Salihi da sako.
Duk muna zaune adakin Amma Sakon yazo abunda ya bamu mamaki tashin Amma da Sauri da fitan ta batare da ta jira cewar komai ba yasa ta fita ta barmu baki sake cikin zullumi da Tunanin lafiya.
Ni kuma Tunda naji sunan wanda aka ambata gabbaina suka saki a tare. Abunda bai saba gani ba ne na gani yau ya saba indai yazo sai dai yace a kirani ammh yau Amma yace a kira kai Tsaye kenan tabbas akwai wani abu a kasa wanda ban sani ba.
Achan waje kuwa Amma na fita Taga Sadiq ba ta ko tsaya lura da Tahir ba ta karisa gabanshi ta na fad"in"Daman na sani. Ina da kyakyawan tabbacin zaka Dawo Abubakar"
Ta fad'a Lokaci d'aya ta na mirmishi.
Dagowa ya yi ya na kallonta sai dai Rauni da kukan UWA shi ne suka Dawo da shi sai kuma Tausayinsu gabadaya.
Cikin wani irin yanayi yace"Nazo da abunda kika bukata Amma meye abu na gaba?
Amma ta daga hannuwanta sama tace"Alhamdulillah. Alhamdulillah.! Allah na gode maka"
Sai kawai ta fashe da kuka ta na neman zubewa a kasa da Sauri Sadiq ya riketa kafin ta kai kasa kada ta tara masa Mutane.
Cikin kukan ta ke fad'in"Nagode Allah ya yi maka albarka. Yadda kaji kaima kaima Allah ya jikan ka, Allah ya haskaka Rayuwarka da Alheri Allah ya baka abunda kake nema Duniya da Lahira Allah ya tsareka a duk in da ka ke Allah ya sanya albarka acikin Niyyar ka ta Alheri."
Amma ta ke fad'a ta na kuka ga hawaye Shabe shabe Sadiq yasa Hannu ya share mata hawaye ya na fadin"Bakomai Amma."
Amma ta rike Hannuwansa ta jimke ta na fadin"Yadda ka share ma wannan UWAR hawayenta Allah ya share maka naka. Yadda ka sanyaya ma wannan Uwar zuciya kai ma Allah ya sanyaya maka taka zuciyar, Yadda ka duba lamarin wannan Uwar kai ma Ina Rokon Allah ya cigaba da Duba Lamarinka har Abada."
Sadiq na ta amsawa da Ameen Tahir ko ga shi nan Tsaye ya na ji kuma ya na gani ammh ya rasa gane ina aka dosa.
Amma ta na share hawayenta ta juya ta na fadin"Ina zuwa."
Cikin gida ta koma da Sauri duk muma Daki ta daga labule ta na kiran Sunan Adda Fati, ta mike ta na Fadin"Na zo ne Amma?
Kai ta gyada mata da Sauri ta mike ta fita ni da Ramatu muka kalli juna bamu da amsar da tambayar da ke zuciyarmu.
Suna Fita Gefe Amma taja Adda Fati tace ta yi maza ta kira mata Babammu Tanko ta na so ta yi mgana da shi.
Ba musu Adda fati ta latso lambarsa ta kirasa daman wayar na Hannunta sai da ta kira kusan sau uku sannan ya Dauka daman ita ta na da lambobin su ta na kiran su ta na gaishe su ko da su sun yada mu suna da Hakki muma mu bi mu yi zumumci da su.
Bayan sun gaisa tace masa Amma ke son mgana da shi nan da nan ya bata rai duk da ya jima rabon da yaji ta nemesa yasan kila wani abu take Bukata sai dai zencen ya sha Bambam ta na karban wayar ta yi ma Adda mgana da Hannu alamun ta bata waje.
A gurguje suka gaisa har ya fara Tsumewa ya zata ko wani taimako ta ke nema sai yaji ta fara rattaba masa wani jawabin da yasa ya d'an Saki Fuska cikin Sauri yace"Ina gida za su iya karisowa Aisha."
Daga haka Amma ta yi masa godiya suka yi sallama.
Abun mamaki Amma ta shigo Dakin nan bakinta a washe Adda Fati ta mikama wayarta Lokaci daya ta na Fadin"Fati ta shi ki shirya akwai baki a waje gidan Babanku Tanko zaki raka su yanzu."
Ni da Adda Rukayya muka had'a baki wajen fad'in"Gidan Baba Tanko kuma?
Cikin Alamun Sigar Tambaya. Amma ta gyada kai fuskarta na bayyanar da Annuri Adda Fati ba musu ta mike ta na Saka Hijabinta Hanifa na Hannuna ta yi barci sai tace na riketa bari ta Dawo Ta na fita Inna Talatu ta kalli Amma ta na fadin"Lafiya dai ko?
Amma na mirmishi tace"Sai Alheri in sha Allahu."
Adda Rukayya tace"Amma ko an fasa Tafiyar ne?
Amma ta kalleta kafin tace"A'a ban fasa ba sai dai kila tafiyar ne zata sauya daga ni da Hasiya zuwa ni kad'ai."
A tare muka kalleta ni dai sai da gabana ya amsa Ramatu ta washe baki kafin tace"Yauwa Amma ki bar mana Hasiya tare damu"
Amma na mirmishi tace"In sha Allahu Ramatu."
Amma fa ta bama kowa mamaki kudi tace na bata naira Dubu biyu na Dauko na bata ita kuma ta aiki Habiba shago ta siyo mata Cimgam da Minti.
Inna talatu ne sai da ta maganta cikin mamaki tace"Tashin ne har da rabon su Minti?
Amma tace"Wannan na Dabam ne Talatu."
Ni dai zaune na ke rike da Hanifa ammh ba na cikin Hayyacina.
Ina jin Ramatu na fad'in"Kawata nan Amma zata bar min ke"
Ta fad'a cikin Farimciki da Annushuwa kallonta kawai na yi ammh ni nasan a raina ba abunda take tunanina ba ne.
Abun mamaki me yasa Amma tace a raka su Assadiq wajen Baba Tanko?
*******
Ita kanta Adda Fati ta yi mamakin ganin Sadiq sai dai ba ta samu zarafin jin ba'asi ba gaisawa kawai suka yi tace su je Amma tace ta yi musu jagora zuwa gidan Babansu Tanko.
Sadiq sai da ya riko hannun Tahir da ya tsaya ya kasa bin su saboda ya na neman karin bayani.
Adaidaita suka samu suka hau har Babban Dodo. Ita ta fara shiga cikin gidan zuwa wani Lokaci sai ga Baba Tankon ya fito da kanshi.
Sadiq bai tsaya ma kallonsa ba yadai san Datiijo ne Hannu ya ba su suka yi musabaha kafin ya jazasu zuwa cikin Falon gidansa da ke da kofa ta waje.
Suna shiga ya fita ya barsu Tahir ya juyo ya na kallon Sadiq kafin yace"Zaka yi min bayanin meke faruwa ne ko zaka cigaba da barina cikin Duhu.?
Sadiq Kai tsaye yace"An kusa zuwa gabar da zaka san komai."
Shuru suka Cigaba da zama sai chan kuma sai ga shi ya dawo da wasu mutane kamar goma haka.