← Book details Tsaka Mai Wuya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 59 OF 69

Sashe 59

Tsaka Mai Wuya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ko alama Adda bata nuna ma Amma da mganar tafiya da ita tazo ba Jauro nan ya barta ya koma sai da ta kwana sannan ta zaunar da Amma da mu tare da Adda Fati da Adda Rukayya.
Domin Adda Fati na zuwa tace ta Kira mata Rukayya jin Adda ke kira yasa ta zo da sauri a tunanin ta ba lafiya.
Sai da taga kowa lafiya har Amma sannan ta kwantar da Hankalinta.
Maganar da Adda ke fad'i ne ta girgizamu ba Shawara ba ce wannan karon tace Umarni ne zata Dauki Amma su koma gida.
Adda Fati ta zaro ido kafin tace"Adda mu kuma fa? Mu kadai anan ba mu da kowa fa"
Adda tace"Ba ku kad'ai ba ne. Ku na da mazajen ku sannan nan ne Tushen ku ga kuma Dangin Uban ku duk suna garin nan, Aisha kuma aure ne daman ya kawota kuma wanda ya yi silan zuwanta ba shi Tuntuni ya dace na tafi da ita mu zauna tare saboda ku na kauda kai. Ammh yanzu komai ya zo karshe Da Aisha da Hasiya da Habiba duka zan iya rike su, na saka Tuni an gyara muku muhalli ci da sha bazai gagaremu ba in sha Allahu."
Ta fad'a kai tsaye ta na kallon mu.
Cikin mu sai aka rasa mai kara cewa wani abu tun bayan mganar Adda Fati.
Adda ta kalli Amma da ta dukar da kai kafin tace"Wannan karon ba karb'an uzuri. In Hasiya ki ke ji ki daina damuwa achan ma zata samu miji in sha Allahu."
Adda Rukayya tace"Ammh Adda rayuwar ce ba d'aya ba kina ganin akwai takurawa gareki kema ki na Fama da kanki.?
Da Sauri Adda Fati tace"Eh nima shi na ke Tunani."
Adda ta yi mirmishi kafin tace"Ni fa da Aisha muka taso tun bayan rasa iyayen mu. Kuna tunanin bazan iya rike ku ba ne? Kamar yadda na tara ku suma yarana haka na Tarasu kuma suka bani goyon bayan Tahowa da ku kuma in sha Allahu sun ce baza su gaza ba, Naga nan din da ta ke zaune ba wani mai kula da ita. Dangin babanku kuma sun yi butulci da Hankalina ke chan a tashe gwara na Dawo da ita a kusa da ni zai fi min kwanciyar Hankali. Ba shawartanku na ke yi ba Umarni ne.
Ke Hasiya ku fara shiri kin ji ko?
Cikin sanyin jiki nace"To Adda."
A baya na fi kowa Murna da komawar mu gadan mallam mamman.
Ammh abun mamaki yanzu sai naji kamar in na tafi zan bar wani abu mai Muhimmamci anan to menene shi wannan?
Wata zuciyar ta tunasar da ni shi.

"ASSADIQ."

shine na ke jin wani iri ya ya zai ji in ya dawo akace masa ga in da muka koma? Maimakon na yi murna sai naji na kasa yin farinciki ko kad'an.
Ammah kuma ba ta iya ma Adda Gaddama ba tace duk yadda tace haka za'ayi.
Su kan su su Adda jikinsu duk ya yi sanyi haka suka tafi.
Washegari mun tashi da had'a kaya duk da bamu gayama kowa ba sukola muka ta shi da shi Tun Safe ni da Habiba.
Sai da yammah sai ga Adda Fati da mijinta. na zata yazo gaida Adda ne sai bayan sun Fati Adda ta kalleni ta na fadin"Fati da mijinta sun roki a ba su Habiba ta zauna tare da su saboda karatun ta.  to ganin yadda ta damu yasa na amince sai ke ki shirya tare da ke zamu tafi."
Gabana sai da ya fad'i na kasa ma mgana Habiba na jin haka ta fara tsallen Murna, daman karatunta ta ke ji in ta koma chan ammh jin haka sai ta fara murna.
Amma ba ta ce komai ba sai dai a kasan ranta ni ta ke Tausayi.
tun jiya da Adda ta yi mganar nan ta ke ta nema min mafita  ammh bata samu ba.
Habiba ta samu nata mafita saura Hasiya. Ita da Rayuwarta ke cikin Tsaka mai wuya ta na bukatar Farinciki da jin dad'i.
Ta na bukatar wata rayuwar da ta fi wannan da ta ke ciki.

*Littafin TSAKA MAI WUYA paid book ne, iya Book 1 ne free Pay N500 For BOOK 2,3. Regular group or VIP GROUP N1000. Via 0552179550 Jamila Umar gt bank.*
*Shedar biya ta wad'anan lambobin 09069067488 or 08032773332.*
*SPECIAL GROUPS Follow@Jamilaumarjanafty On AREWABOOKS mutanen mu na Niger za su Tuntubi Kausar Aglan nissa +22796562223 Nagode*

*Janafty*
*TSAKA MAI WUYA.*

*Wattpad:Jamilaumar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*

https://chat.whatsapp.com/BARBh2begGc0KdlLEZDzhk

Ku zo ku yi sayayyarku tare da Yar Gidan Imam, inda za ku sami komai cikin sauki, tun daga kan kayan kicin, kayan yara,atamfofi da lesissika uwa uba da kayan gyaran jiki irin na manyan matan da suka San kan su,har counselling mu na yi yadda duk damuwar da ki ke ciki a game da aurenki da gyaran jikinki zaki samu solution. Ku dai ku shigo cikin wannan gidan na karamci kai tsaye domin more tagomashin da ke ciki.

*18*

Kamar wasa sai ga karamar magana ta zama babba, Adda ta dage tare da ni da Amma zata koma kafarta kafarmu tun ina ganin lamarin wasa har na sare na Saduda da cewa tafiya ta zama Dole.
Tuni har Amma ta sanar ma da matan gidanmu saboda rayuwa. An yi zaman Amana tun zamanin zaman mu acikin gidan nan ko cacar baki bata taba yi da kowa ba.
Mu ma haka babu ruwan mu tun ballatana ma da ba su cika Rab'ar mu ba, mu ma sai mu ka kama kan mu da Maraicin mu.
Adda Fati da Adda Rukayya matuka sun shiga damuwa. Adda Rukayya ta fi bani mamaki ita da ni ke ganinta ba ta damu da mu ba, sai ga shi ta nuna jimaminta sosai. Daman tun faruwar abunda ya faru a gidanta ta yi sanyi yanzu lafiya lau mu ke da ita sai dai duk da haka babu shakuwa Tsakanina da ita kamar yadda muka Shaku da Adda Fati.
Dukkansu ba su da mafita ne Gwara ma Mijin Adda Fati zai iya rike mu ni da Amma. Ammh mijin Adda Rukayya ba shi mutumci ko Habiban Adda ta ce zata rike wlh bazai rike ba. Mutumin da bai san kowa ba sai kan shi itama don ya na sonta ne shiyasa ya ke yi mata abunda ta ke so.
A baya ne na so na koma wajen Adda da abubuwa suka rikicemin ammh a yanzu kuma sai naji ba na son barin nan d'in. Amma ma ta gama iya nazarinta ta san ba mafita sai ta bar ma Allah duka zabinsa.
Adda Fati ta kira Ramatu ta sanar da ita ta kuma ce ta sanar da Inna Talatu. Washegari sai ga su sun zo Hankula ta she, Inna talatu ta ce"Yanzu shikenan kuma Amma zaki bar mu?
Kafin ma Amma ta ba ta amsa Adda ta karb'e da cewa"Ba ta bar ku ba. zumunci ai Allah ya riga ya had'a. In bukatar hakan ya ta so zamu zo. Kuma in wani sha'ani ya taso ko auran Hasiya duk za ku zo in sha Allahu."
Daganan Inna talatu tasan Adda ta riga ta yanke hukunci ba mai tada wannan mganar. daman ta dad'e ta na so ta Dauke Amma d'in ta koma wajenta.

Ni kuma Ramatu sai nanata tafiyarmu ta ke yi ta na fad'in"Yanzu Hasiya in kika tafi ya zan yi? Kinsan fa ba ni da wata kawa wacce ta wuce ki."
Cikin sanyin murya nace"Zamu rika waya Ramatu kada ki damu ba bu abunda zai sauya."
Ramatu ta yi tagumi ta na kallo na ina yi ma Noor rawa ta na bangala Dariya.
Cikin muryan kamar za ta yi kuka tace"Hasiya sai na ke ganin kamar rayuwar zata yi miki wahala.  nan aka haifeki kuma anan kika ta shi chan kuma bakon waje ne a wajen ki. Akwai chanjin Rayuwar da kafin ki saba sai kin sha wuya."
Mirmishi na yi kafin nace"Zan saba Ramatu. a yanzu dai banga irin rayuwar da Hasiya bazata iya zama acikin ta ba."
Ramatu tace"Ni da zaki amince da na yi ma Nura mgana tunda ina da Daki sai ki zauna tare da mu."
Ido na waro ina kallonta kafin nace"Ramatu anya ki na da Hankali kuwa.?
Ramatu tace"Ras na ke Hasiya. Allah da gaske na ke in kin amince na yi masa mgana sai ki saka baki mu lallashi Adda da Amma"
Dariya na yi kafin yace"A'a ba da ni za'ayi wannan aika aikar ba. Bazai yu yu ba Ramatu ai ba mutuwa zan yi ba,  Wajen zama kawai zan sauya kuma zumuncin mu na nan har Abadan"
Ramatu sai ta kasa magana sai kallona ta ke yi cikin Rauni. Da alamun so ta ke yi ta yi kuka ni kuma sai naki kallonta na cigaba da yi ma Noor wasa ina fad'in"Kinga Noor ta kara wayau sosai."
Ramatu ba ta ce komai illah tagumin da ta zabga ta na kallo na.
Noor ce ta fara kuka na tashi na goyata na fara zagaye dakin Maman Boy da ita ina jijjigata.
Sai ji na yi Ramatu tace"Shikenan sana'ar Danwake ya tsaya?
Juyowa na yi ina fad'n"Ya jima da Tsayawa tun kafin zuwan Adda rabo na da yi."
Ramatu ta sauke ajiyar zuciya ganin yadda ta damu yasa na karisa na zauna gefenta ina Dafa kafad'arta Lokaci d'aya ina fad'in"Ki daina damuwa ba mutuwa fa zan yi ba."
Ramatu ta kalleni kafin tace"Ko ba mutuwa zaki yi ba. Zaki yi nesa da ni ko?
Sai na kasa mgana zuciyata sai naji ta matse ni kaina ba na son yin nesa da su musamman wani da zuciyata ta saba da shi.
Cikin fitan hayyaci nace"Ni kaina ba na so na yi nesa da shi Ramatu."
Ban san me na fad'a ba sai ji nayi Ramatu tace"Shi wa?
Kallonta na yi ina tunanin me na fad'a.
Ganin haka yasa Ramatu tace"Shi waye baki son ki yi nesa da shi?
Ajiyar zuciya na sauke Ramatu ce wacce ba abunda na ke boye mata ita D'in Sirrina ce kamar yadda na ke Sirrinta.
Cikin sanyin muryata da ta kara yin kasa nace

" ASSADDIQ..."
Chapter 59 · 0% Book details