Sashe 38
Tsaka Mai Wuya Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Dakin Maman Boy muka shige na saki Labule na san su da Dabi'an labe.
Daman mun shige mun bar su da mgana a bakinsu.
Zama muka yi a kujera d'aya ina ta kallon Ramatu ta yi kiba kamar ba ita ba Taga kallon ya yi yawa ta Zungureni ta na fad'in"Kallon fa kinga na sauya miki ne?
Kai Tsaye nace"Kin yi kiba Ramatu kin yi fari sosai ma sha Allah."
Ramatu tace"Alhamdulillah. Ammh kinsan har da Jego ko?
Ina Hararanta nace"Wani jegon? Mata kina neman wata biyar da Haihuwa kina kiran Jego kawai dai yayana ya iya kiwo ga Noor ma ta yi bulbul ta yi yawo."
Ramatu tace"Gaskiya kam baza'a raina ma yayanki ba. Yana ji damu sannan ya na kula damu yace na gaisheki ma sosai."
Ina mirmishin jin dadi nace mata ina amsawa. Nan muka shiga Hira har da Shewa sallah kadai ya tadamu girki ma Adda tace na bari zata girka.
Me zata Dafa? Nace muna da Sauran Taliya ta Dafa mana Amma na son ta da wake ta manja.
Tace to kafin ma ta Dora Biyu tayi sai ga Habiba ita ta karbi girkin. Cikin lokaci ta gama sai da muka ci muka natsa Noor ma Habiba ta karbeta mayya yara ne ina ta mata Fad'an ina zata kai yara har Biyu ga Hanifa ga Noor ta na Dariya tace"Kai Adda na iya fa renon yara kema ki bari ki Haihu ni zan renan miki ya'yan ki."
Mirmishi kawai na yi kafin nace"Habi ni ai bazan haihu ba ballatana ma ki renin ya'ya na ammh dai ga na su Adda da su Ramatu sun isheki Reno."
Ba Ramatu kadai ba Hatta Habiba sai da ta tsaya ta na kallona.
Ramatu ne tace taje kawai ta na Fita ta juya kaina ta na min Fad'a cikin Masifanta tace"Haba Hasiya. Shikenan sai ki cire rai da Rahmar Allah? Wa ya fada miki bazaki yi aure ba? Sannan wa ya fad'a miki ke ma bazaki Haihu ba?
Kai Tsaye nace"Komai a bayyane ya ke Ramatu kada ki yi kokarin Lullube abunda bazai taba lullubuwa Saboda ina taki ba. na sani kin sani, Ba bu wani Namijin da zai so ya aure ni ya auri Bala'i masifa da shiga uku da kudinsa ba Ramatu, ba bu wannan Namijin"
Kai Tsaye Ramatu tace"Akwai shi. akwai shi Hasiya."
Cikin Idanuwana da suka cika da kwallah na kalleta kafin nace"Akwai shi fa kika ce? To in akwai shi yana ina?
Shuru ta yi cikin wani yanayi kafin tace"Ya nan a inda Allah ya ijiyesa Hasiya. Kila kusa dake ko kuma nesa da Duniyarki. Ammh tabbas nasan akwai wannan Namijin. Namiji irin Salisu sannan wanda ya fi Abubakar Jarumta da Tausayi namijin da yasan Babu mai yi sai Allah ya kuma san Kaddara ce ke bibiyan Rayuwarki ba Canfi ba"
Kalamanta suka sakani sai da na Murmusa kai tsaye nace"Kada mu yaudari kanmu Ramatu ba bu wannan Namijin. ko zai amince da ni Ahalinsa bazasu taba bari D'ansu ya auro Jaraba da kudinsa ba."
Ramatu tace"ni kuma ina ji ajikina Hasiya bazaki Dauwama ahaka ba. Namijin da na Fada miki koma waye zai zo. Zai zo in sha Allahu"
Cikin Sauri nace"Zai zo? Yaushe..?
Ramatu ta kalleni cikin Rauni kafin tace"Bansani ba Hasiya.. ammh nasan Allah zai kawo sa."
Ina jin kalamanta sai nima nawa kalaman bakin suka kare cigaba da bani baki tayi ta na ta faman Lallashina.
Shine ma na sake har na gayamata mafarkin da nayi na Salisu. Kai Tsaye tace"Kada ki damu Salisu bazai taba Zargin ki ba ai yasan abubuwan da suka Faru ya tabbata ke ma kina kokarin kokuwa da Kaddaran ki ne."
Sai na gyad'a mata kai alamun gamsuwa shiyasa ta cigaba da Fad'in"Saboda haka ki kwantar da Hankalin ki Salisu zai warke kamar wani abu bai taba samunsa ba."
Da Sauri nace"In sha Allah.."
Muna nan muna mgana sai da aka kira la'asar muka koma Dakin Amma muka yi sallah mun idar kenan sai ga Kiran Adda Rukayya ta wayar Adda Fati bayan sun yi mgana aka bama Amma suka gaisa suka yi mganan da za su yi sannan suka yi sallama.
Sai alokacin Adda Fati ke fad'amana Ranat asabar Adda Rukayya zasu tare a Sabon gidan da Mijinta ya gida anan Gaskiya. Sannan tare da Birthday din Cikar Amna shekara Shidda Shine ta ke fad'ama Adda Fati tace ta fad'amana jin ma tana gidan sai tace ta bama Amma ta yi mata mganar Habiba tazo Ranar Jumma'a ta tayata parking.
Dukkanmu mun yi mata Murna. Adda Fati tace"Ramatu ki fad'ama Inna Talatu Ranar sati sai mu je mata Murna."
Ramatu tace"Zan fad'a mata Hasiya ki shirya muje.."
Zan yi mgana kenan in ce bazan je ba Amma ta yi saurin cewa"Zaki je mana Hasiya. Yanzu ma sai da tace na fad'a miki tana jiran ki."
Na sha mamakin wai Adda Rukkaya na jira na, matar da Tsoron fad'an mijinta ta ke yi sama da ni yar'uwanta.
Ganin yadda na yi ne yasa Adda Fati da Ramatu suka rika Tausana da kada na Damu yar'uwata ce Rukayya ban isa na sauya ma wannan alakar tamu suma ba jinina ce.
Da kalaman bakinsu yasa nace na amince zan ce batare da Tunanin wani irin Tozarci ke jirana in na shiga cikin sha'anin da ban saba shiga ba.
Sai Yamma Adda Fati ta tafi, Ramatu ta riga ta tafiya tunda ita gida zata koma.
Naji dadin zuwan Ramatu ko banza ta Debemin kewa tare da Shawarwarinta masu amfani.
****
Tahir bai dawo ba sai Ranar Jumma'a Da Safe ya je wajen aiki ko da ya dawo ya iske shi.
Ya san muhimmamcin sallama a musulunci an kuma ce in kai kaje to kayi ma wanda ka iske sallama. Shiyasa ya yi masa sallama ya kuma ba shi Hannu suka yi musabaaha. Yadda Tahir bai sakar masa Fuska ba shima haka ya yi masa gim da ransa.
Abu d'aya ya Kudurta ko kwashe kayansa Tahir ya yi zai sauya wajen zama bazai taba ce masa don me ba? Saboda sanda ya zo suka zauna Tare ba shi ya Kirasa ba Ra'ayinsa ne yanzu ma in yace zai sauya wajen zama bazai taba zama Takura ga Ra'ayin Tahir ba. Shi dai hakkin zaman tare ya Cire sannan ba zai fasa gayama Tahir gaskiya ba.
Duk da yasan shakuwa da Amintar da ke Tsakaninsu bazai saka su yi nesa da juna ba. Dole daya zai nemi daya kuma ya na Tabbacin ko kwashe kayansa Tahir ya yi ya na da tabbacin sai ya Dawo Domin bai saba da kowa ba sama da shi shiyasa bai damu ba ya shiga Harkan gabansa.
Yau da Danwakensa yaje wajen aiki ya ci a chan bai dawo da Saura ba Duka ya cinye. Ya ji kimar mai Danwaken nan ta karu a idonsa Matar mai mutumci ne tasan Daraja Costumominta tunda har ta iya lura da ya yi kwanaki bai zo siyan Danwake ba har ga Allah abun ya yi mishi dadi a ranshi.
Wata zuciyar ta fad'a masa ka sani ko itama ta na da manyan ya'ya dole ta damu da ya'yan wasu. Kawai Tunaninsa ya fi ba shi mai Danwaken nan Dattijuwa ce uwa kuma Rayuwa da yanayin da ake ciki ballatana ga ire iren anguwan nan sai a hankali zaka ga kowa na sana'a domin Dogara da kansa.
Kuma a tunanin Sadiq a irin su Sana'an Danwake, Kuli abinci haka na Dattijai ne yara kuma sai dai in su awara, Dankali da Sauransu. Bai taba kawo ma kansa matashiyace ke Danwaken da ke siya ya na jin Dadinsa ba.
Daman mun shige mun bar su da mgana a bakinsu.
Zama muka yi a kujera d'aya ina ta kallon Ramatu ta yi kiba kamar ba ita ba Taga kallon ya yi yawa ta Zungureni ta na fad'in"Kallon fa kinga na sauya miki ne?
Kai Tsaye nace"Kin yi kiba Ramatu kin yi fari sosai ma sha Allah."
Ramatu tace"Alhamdulillah. Ammh kinsan har da Jego ko?
Ina Hararanta nace"Wani jegon? Mata kina neman wata biyar da Haihuwa kina kiran Jego kawai dai yayana ya iya kiwo ga Noor ma ta yi bulbul ta yi yawo."
Ramatu tace"Gaskiya kam baza'a raina ma yayanki ba. Yana ji damu sannan ya na kula damu yace na gaisheki ma sosai."
Ina mirmishin jin dadi nace mata ina amsawa. Nan muka shiga Hira har da Shewa sallah kadai ya tadamu girki ma Adda tace na bari zata girka.
Me zata Dafa? Nace muna da Sauran Taliya ta Dafa mana Amma na son ta da wake ta manja.
Tace to kafin ma ta Dora Biyu tayi sai ga Habiba ita ta karbi girkin. Cikin lokaci ta gama sai da muka ci muka natsa Noor ma Habiba ta karbeta mayya yara ne ina ta mata Fad'an ina zata kai yara har Biyu ga Hanifa ga Noor ta na Dariya tace"Kai Adda na iya fa renon yara kema ki bari ki Haihu ni zan renan miki ya'yan ki."
Mirmishi kawai na yi kafin nace"Habi ni ai bazan haihu ba ballatana ma ki renin ya'ya na ammh dai ga na su Adda da su Ramatu sun isheki Reno."
Ba Ramatu kadai ba Hatta Habiba sai da ta tsaya ta na kallona.
Ramatu ne tace taje kawai ta na Fita ta juya kaina ta na min Fad'a cikin Masifanta tace"Haba Hasiya. Shikenan sai ki cire rai da Rahmar Allah? Wa ya fada miki bazaki yi aure ba? Sannan wa ya fad'a miki ke ma bazaki Haihu ba?
Kai Tsaye nace"Komai a bayyane ya ke Ramatu kada ki yi kokarin Lullube abunda bazai taba lullubuwa Saboda ina taki ba. na sani kin sani, Ba bu wani Namijin da zai so ya aure ni ya auri Bala'i masifa da shiga uku da kudinsa ba Ramatu, ba bu wannan Namijin"
Kai Tsaye Ramatu tace"Akwai shi. akwai shi Hasiya."
Cikin Idanuwana da suka cika da kwallah na kalleta kafin nace"Akwai shi fa kika ce? To in akwai shi yana ina?
Shuru ta yi cikin wani yanayi kafin tace"Ya nan a inda Allah ya ijiyesa Hasiya. Kila kusa dake ko kuma nesa da Duniyarki. Ammh tabbas nasan akwai wannan Namijin. Namiji irin Salisu sannan wanda ya fi Abubakar Jarumta da Tausayi namijin da yasan Babu mai yi sai Allah ya kuma san Kaddara ce ke bibiyan Rayuwarki ba Canfi ba"
Kalamanta suka sakani sai da na Murmusa kai tsaye nace"Kada mu yaudari kanmu Ramatu ba bu wannan Namijin. ko zai amince da ni Ahalinsa bazasu taba bari D'ansu ya auro Jaraba da kudinsa ba."
Ramatu tace"ni kuma ina ji ajikina Hasiya bazaki Dauwama ahaka ba. Namijin da na Fada miki koma waye zai zo. Zai zo in sha Allahu"
Cikin Sauri nace"Zai zo? Yaushe..?
Ramatu ta kalleni cikin Rauni kafin tace"Bansani ba Hasiya.. ammh nasan Allah zai kawo sa."
Ina jin kalamanta sai nima nawa kalaman bakin suka kare cigaba da bani baki tayi ta na ta faman Lallashina.
Shine ma na sake har na gayamata mafarkin da nayi na Salisu. Kai Tsaye tace"Kada ki damu Salisu bazai taba Zargin ki ba ai yasan abubuwan da suka Faru ya tabbata ke ma kina kokarin kokuwa da Kaddaran ki ne."
Sai na gyad'a mata kai alamun gamsuwa shiyasa ta cigaba da Fad'in"Saboda haka ki kwantar da Hankalin ki Salisu zai warke kamar wani abu bai taba samunsa ba."
Da Sauri nace"In sha Allah.."
Muna nan muna mgana sai da aka kira la'asar muka koma Dakin Amma muka yi sallah mun idar kenan sai ga Kiran Adda Rukayya ta wayar Adda Fati bayan sun yi mgana aka bama Amma suka gaisa suka yi mganan da za su yi sannan suka yi sallama.
Sai alokacin Adda Fati ke fad'amana Ranat asabar Adda Rukayya zasu tare a Sabon gidan da Mijinta ya gida anan Gaskiya. Sannan tare da Birthday din Cikar Amna shekara Shidda Shine ta ke fad'ama Adda Fati tace ta fad'amana jin ma tana gidan sai tace ta bama Amma ta yi mata mganar Habiba tazo Ranar Jumma'a ta tayata parking.
Dukkanmu mun yi mata Murna. Adda Fati tace"Ramatu ki fad'ama Inna Talatu Ranar sati sai mu je mata Murna."
Ramatu tace"Zan fad'a mata Hasiya ki shirya muje.."
Zan yi mgana kenan in ce bazan je ba Amma ta yi saurin cewa"Zaki je mana Hasiya. Yanzu ma sai da tace na fad'a miki tana jiran ki."
Na sha mamakin wai Adda Rukkaya na jira na, matar da Tsoron fad'an mijinta ta ke yi sama da ni yar'uwanta.
Ganin yadda na yi ne yasa Adda Fati da Ramatu suka rika Tausana da kada na Damu yar'uwata ce Rukayya ban isa na sauya ma wannan alakar tamu suma ba jinina ce.
Da kalaman bakinsu yasa nace na amince zan ce batare da Tunanin wani irin Tozarci ke jirana in na shiga cikin sha'anin da ban saba shiga ba.
Sai Yamma Adda Fati ta tafi, Ramatu ta riga ta tafiya tunda ita gida zata koma.
Naji dadin zuwan Ramatu ko banza ta Debemin kewa tare da Shawarwarinta masu amfani.
****
Tahir bai dawo ba sai Ranar Jumma'a Da Safe ya je wajen aiki ko da ya dawo ya iske shi.
Ya san muhimmamcin sallama a musulunci an kuma ce in kai kaje to kayi ma wanda ka iske sallama. Shiyasa ya yi masa sallama ya kuma ba shi Hannu suka yi musabaaha. Yadda Tahir bai sakar masa Fuska ba shima haka ya yi masa gim da ransa.
Abu d'aya ya Kudurta ko kwashe kayansa Tahir ya yi zai sauya wajen zama bazai taba ce masa don me ba? Saboda sanda ya zo suka zauna Tare ba shi ya Kirasa ba Ra'ayinsa ne yanzu ma in yace zai sauya wajen zama bazai taba zama Takura ga Ra'ayin Tahir ba. Shi dai hakkin zaman tare ya Cire sannan ba zai fasa gayama Tahir gaskiya ba.
Duk da yasan shakuwa da Amintar da ke Tsakaninsu bazai saka su yi nesa da juna ba. Dole daya zai nemi daya kuma ya na Tabbacin ko kwashe kayansa Tahir ya yi ya na da tabbacin sai ya Dawo Domin bai saba da kowa ba sama da shi shiyasa bai damu ba ya shiga Harkan gabansa.
Yau da Danwakensa yaje wajen aiki ya ci a chan bai dawo da Saura ba Duka ya cinye. Ya ji kimar mai Danwaken nan ta karu a idonsa Matar mai mutumci ne tasan Daraja Costumominta tunda har ta iya lura da ya yi kwanaki bai zo siyan Danwake ba har ga Allah abun ya yi mishi dadi a ranshi.
Wata zuciyar ta fad'a masa ka sani ko itama ta na da manyan ya'ya dole ta damu da ya'yan wasu. Kawai Tunaninsa ya fi ba shi mai Danwaken nan Dattijuwa ce uwa kuma Rayuwa da yanayin da ake ciki ballatana ga ire iren anguwan nan sai a hankali zaka ga kowa na sana'a domin Dogara da kansa.
Kuma a tunanin Sadiq a irin su Sana'an Danwake, Kuli abinci haka na Dattijai ne yara kuma sai dai in su awara, Dankali da Sauransu. Bai taba kawo ma kansa matashiyace ke Danwaken da ke siya ya na jin Dadinsa ba.