← Book details Tsaka Mai Wuya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 56 OF 69

Sashe 56

Tsaka Mai Wuya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Innani haka ta tara su Abba akaro na Biyu tace mganar aure bata sai magajin gida ya yi masta dinsa.
Haka yaran ma duk ta kirasu ta na fad'a musu sai magajin gida ya samu masta za'ayi auransa da Sulsana.
Kowa yaji sai ya Dara, Duk wanda yace aikin waye haka da Innani ta Sauya mgana."
Umma na dariya ta kan ce"Aikin waye kuwa ban da na magajin gida magajin kowa."
To in ba magajin gida ba, Waye ya isa ya sauya wannan mganar ai sai shi kad'ai ne wanda mganarsa ke saman ta Innani da ta Abba shi kan shi.

*****

Ya dawo a gajiye dalilin  da yasa bai leka gidan su Hasiya ba kenan.
Sai washegari litini bayan ya dawo daga in da ya ke hidimar kasar sa. Ya na jin Amma a ransa in ya ganta Umma ya ke gani Hasiya da Habiba kuwa tamkar Siyama da Salima ya ke kallonsu. Ya kuma san zasu damu da rashin ganinsa tunda bai fad'a musu zai yi tafiya ba.
Sanin Tahir baya son ya ji zai je gidan nan sai ya fara maganganu yasa bai fad'a masa ga in da za shi ba, ce masa kawai ya yi zai je ya dawo
Takaici suka saka Tahir ya kasa mgana Sadiq ya fita ba Dadewa sai ga wani Mutum ya zo ya na masa sallama a kofar dakinsa.

Ya ma zata abokan zaman su ne Tunda in suna bukatar wani abu suna yi musu mgana. Tun ballatana sun san Halin Sadiq abun sa na mutane ne.
Ya na fitowa sai ya ga bakuwar Fuska da bai taba gani ba mutumin zai kai shekara arba'in dattijon matashi ne.
Hannu  ya basa suka yi musabaha, cikin mamaki Tahir yace"Lafiya? Kamar ban gane ka ba?
Mirmishi ya yi masa kafin yace"Baka sanni ba shiyasa baka gane ni ba.?
Tahir yace"Oh to ko wani ka ke nema?
Da sauri yace"Ai naga wanda na ke nema dazu ya fita ko?
Tahir yace"Sadiq?
Cikin alamun tambaya kai ya gyad'a masa kafin yace"Abubakar Sadiq sunansa kenan shima."
Tahir duk bai gane ba yasa ya kankance idanuwana kafin yace"mallam wai lafiya?
Kai tsaye yace"Taimako ne yasa na zo gareka. na fahimci kai ne abokinsa da ku ke zama tare. To in dai har kana son abokin ka ya cigaba da Rayuwa ya kamata ka dakatar da shi da Rab'ar in da yarinyar nan ta ke."
Tahir ya saki hancinsa ya na shakan Iska kafin yace"Wata yarinya kenan.?
Kai Tsaye yace"Hasiya mai Danwake wata Fara farinta mai haske haka Siririya."
Tahir yace"Oh na ganeta lafiya? Da wani abu ne?
Mutumin yace"Sosai ko da matsala dan Samari ganin ko ba yan garin nan ba ne kada a cutar da ku ba ku sani ba. Kada ka bari abokin ka ya auri wannan yarinya ta na da bakin jini da bakin kashi mai kashe rai da asaran Dukiya."
Tahir ya ware ido kafin yace"Bawan Allah ban ga ne ba? Wa ya fad'a maka Sadiq auran wannan yarinyar zai yi? Taimakon su kawai ya yi shikenan ba wata mgana."
Shima kai tsayen yace"Duk da haka dai ya yi nesa da ita gudun matsala abu ne ya faru ba sau d'aya ba sau biyu ba kowa a anguwan nan yasan da labarinta gwara ka ba shi shawaran ya kiyaye domin tsira da Lafiyarsa."

Tahir ya gaji da jin mganar da ya kasa ganewa kai tsaye yace"Mallam ka tafi kai tsaye kan mganar ka. Ba na son wannan zagaye zagayen naka."
Jin haka yasa ya shiga warware ma Tahir komai da ya Dangancin Hasiya.
Har da mutuwar babanta ma itace cutar mahaifinta karayan arzikin su. Gujen su da Ahalin babansu suka yi. Auran ta da Abubakar da abunda ya faru da kuma na Salisu ya karishe da Fadin"yarinyar ba'a san mayya ba ce ko wani abu. Ammh tabbas duk wanda ya Rabe'ta akwai asaran rai ko Dukiya in ba'a Mutu ba za'a wahala sannan a rasa komai irin su zama da su bala'i ne da Masifa."
Har Mutumin nan ya tafi Tahir na Tsaye rike da kugu baki bude mamaki ya Rufe shi.
Lalle biri ya yi kama da Mutum yarinyar nan shiyasa farinta ya yi masa wani iri ashe ashe bakar daga ce Gobara daga kogi mganinta sai Allah.
Bari Sadiq ya dawo in yaji haka don Dolensa sai rabu da huld'ar da duk abunda ya shafi wannan yarinyar.

*Littafin TSAKA MAI WUYA paid book ne, iya Book 1 ne free Pay N500 For BOOK 2,3. Regular group or VIP GROUP N1000. Via 0552179550 Jamila Umar gt bank.*
*Shedar biya ta wad'anan lambobin 09069067488 or 08032773332.*
*SPECIAL GROUPS Follow@Jamilaumarjanafty On AREWABOOKS mutanen mu na Niger za su Tuntubi Kausar Aglan nissa +22796562223 Nagode*

*Janafty*
*TSAKA MAI WUYA.*

*Wattpad:Jamilaumar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*

https://chat.whatsapp.com/GoRzZ7ZgslV2alO5hYGAnj

*17*

Shi ko Sadiq gidan su Hasiya ya je. Daman ya saba in dai yaje a waje ya kan tsaya ya aika yara sai Hasiya ko Habiba su fito su shiga da shi ciki.
Saboda akwai mata a gidan sannan a tsarin addini shi balaggage ne babu tsari ya rika shiga gidan matan aure kai tsaye batare da izini ba.
Duk da matan gidan na su Hasiya kallo garesu ba wani abu ba ne, kamar ba matan aure ba. Shi dai har ya shiga ya fito kansa na kasa ba shi da dogon kallo a rayuwarsa koda da wanda ya sani ne, ko da akwai sabo a tsakaninsu.

Yau ma d'in Habiba ce ta fito ta shiga da shi ciki har dakin Amma ya na shigowa da Hasiya ya ci karo ta na ganinsa ta sakar masa mirmishinta shima sai ya maida mata martani cikin zolayar da ya fara mata kwanaki nan yace"Hasiya mai Danwake."
Baki ta tura kafin na juya ina kallon Amma lokaci d'aya ina  fad'in"Amma kin gan shi ko? Wai Hasiya mai Danwake ya ke kirana."
Amma na zaune ta na mirmishi na ganin Abubakar d'in, Allah ya sani haka kurum ta ji Allah ya Do'ra mata kaunar wannan bawan Allah, har cikin ranta komai na shi ya yi mata.
Cikin Annurin da kan bayyana saman Fuskarta in har ta ga Abubakar tace"Ke ma ba sai ki rama ba. Da ya kira ki Hasiya mai Danwake sai ke ma ki ce masa Habu mai siyan Danwake."
Gabadayan su suka fashe da Dariya Habiba na rufe bakinta tace"Amma Hamman ne Habu mai siyan Danwake.?
Da ya ke Hamma ta ke kiransa. da Ladabin Fulani yaya kenan.
Abubakar ya yi dariya har sai da Fararan Hakoransa suka bayyana awaje Hasiya ce tace,"Shikenan ko Amma ta kawo shawara."
Sai da ya zauna gaban Amma sannan yace"Hasiya mai danwake ya fi dad'in fad'a ko a baki Amma"
Amma ta yi dariya ba ta ce komai ba gaisawa su ka yi a mutunce kamar yadda suka saba.
Habiba ta kawo masa ruwa a jug. Hasiya kuma ta kallesa ta na fad'in" a kawo abinci..?
Kai ya girgiza Lokaci d'aya ya na Fad'in" na sha fura a wajen aiki. Cikina ya cika Sosai."
Amma tace"ko aikin ne ya hana ka zuwa kwana biyu Abubakar?
Ya na sosa kansa yace"A'a Amma kauye na je. kuma tafiyar ta gaggawace shiyasa ban Sanar da ku ba."
Amma tace"Ayya. Ka same su lafiya ko?
Ya ce"Eh duk sun ce suna gaishe ku Amma"
Amma ta amsa cikin sakewa. Kafin su cigaba da Hira kan rayuwa da sauran su.

Rabin Hiran duk na Amma ne shi na shi eh a'a ne sai ko in ta yi masa wata Tambayar.
Habiba islamiya ta shirya ta tafi ni kuma sai na fita waje na Hura gawayi na Dorama Amma ruwan wanka tunda ba ta yi ba.
Daman ban cika zama adakin ba in ya na nan saboda gudun zargin mutane.
Yan gidanmu sun ta bin kwakwafin ko saurayina ne to ganin ya na shiga har Daki kuma su jima su na mgana da Amma sai suka aminta da cewa da gasken dai kila d'aan uwan mu ne.
Kila kuma cikin Dangin Babanmu da suka watsar da mu ne.
A cikin raina na ke jin Abubakar a chan kasan raina na saka shi cikin Layin masu kaunar mu. Ina shiga Damuwa in bai zo ba, Saboda shi ma ina Fargaban kada watarana a rabamu da shi ina jin Tsoron faruwan hakan shiyasa in bai zo ba na rika shiga Damuwa kenan ina faman ce ma Amma" yau fa bai zo ba"
Amma kan tausheni da cewa"Zai zo Hasiya. A jikina na ke jin yaron nan ba irin sauran ba ne. Zai zo in sha Allahu."

Yau ma sun jima suna Hira da Ammah sai da yammah ta yi ana gabda kiran mangariba sannan ya yi ma Amma sallama ya tafi. Bayan ya ba ta dubu uku Amma ta ki karb'a ta na Fad'in"Kai da ka ke d'an makaranta Abubakar kuma ka ke Hidima damu? Ai sai abun ya yi maka yawa."
Haka ta ke fad'i duk sanda ya yi mata wani karamin kyauta.
Shi kuma kai tsaye ya ke cewa"Amma kin manta na fad'a miki ina Hidimar kasa ne? Suna biyan mu duk wata kuma Dubu uku ai ba Hidima bace."
Amma ta amsa lokaci d'aya ta na Fad'in"Allah ya yi albarka. Allah ya jikan iyayen ka, Allah ya haskaka makwancin su Allah yasa suna cikin Dausayin Aljannah. Nagode sosai Allah ya tsare ka duniya da Lahira."
Shi dai na shi amsawa da Ameen ne cikin jin dadi.
Ko da ya fito da niyyar tafiya samuna ya yi ina ta fama da fifitan gawayi ya ki kamawa saboda nayi rashin sa'a ya na da Sanyi a jikinsa.
Chapter 56 · 0% Book details