Sashe 35
Tsaka Mai Wuya Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Bai cika son zama gidan su ba saboda anguwa ce da ba ta cika Hayaniya ba. Allah ma yasa yana da yayye mata kadaici bai cika Damunsa ba in dai yana gida to kowa Burinsa ya faranta masa.
Suna kaunarshi kamar yadda ya ke kaunarsu. Duk da Mama na taba kishi da Umma ganin Innani ta fi sonta sannan ita ce uwar Magajin gida ammh bata isa ta raba kan ya'yan gidan ba. Ba bambamci Tsakaninsu duk Daya suka Dauki junansu musamman Sadiq ko da ya ke karami a acikinsu yana da kyakyawan Tunani mai kyau tunda ya karanta kuma ya gani.
Bayan Sadiq Mama ta kara Haihuwan Salima da Siyama wacce itace karama daga ita aka rufe haihuwa agidan Siyama ta zama autan Gidan. Sadiq kuma ya kasance Autan Umma Shalelen Abba da Innani.
Dukkansu matan sun yi aure a garin Gusai, Suba'atu ke aure a kano sai Saddiqa da ke kebbi.
A dakin Mama kuwa Sa'ima da Sakeena suma suna Gusai ne suna aure. Sahida na aure a katsina ita kuma Saliha na auran yaron yayar Mama ce suna garin Ibadan da zama in da ya ke aiki a kamfanin Dangote.
Kuma kowacce ta na jin dadi agidan da mijinta sun kuma hayayyafa da ya'yen su turbarkallah masha Allah.
Lokacin da Sadiq ya kamallah makaranta cikin yan'uwan sa ba wacce ta so ya yi bautar kasa a zariya ammh kuma Tunda yace chan zai yi ba su da tacewa barin ma Surayya da suke kira Big sis taso yaje kasar waje ya yi karatun liktanci tare da kanin Mijinta Sadiq yace baya ra'ayin haka.
Da farko Har Abba da Umma sun Amince Innani ma ta samu ta shawo kanta ammh A'a din Sadiq kad'ai ya isa da ya Rusa komai.
Dole a kabarshi ya tafi zariya again Bautar kasa. A wannan karon ma Abba yaso ya siya masa gida yace shima baya Ra'ayi sai haya ya kama da Farko a Daura Tahir ya so ya yi nasa Hidimar kasar ammh Ganin Sadiq ya koma zariya shima ya nema ya koma Saboda Abotan da ke tsakaninsu ta yi nisan da har Ahalin juna sun sani.
Sadiq yadda ake son shi yasa ko Kashi ya kai gida ya ke da Daraja. Shiyasa Tahir ya ke kamar dan gida a gidan su Sadiq duk kuma abunda Sadiq yace ayi masa Abba ba gaddama ya ke yi masa. Ranar farko da Tahir yazo yaga irin gatan da Sadiq ke ciki bayan sun koma Zariya ya kallesa yace"kai ko wani irin abu ka ke samu a garin nan da ka zabi irin wannan Rayuwar Alhalin kai dan gata ne?
Sadiq mirmishi kawai ya yi masa bai ce komai ba, Sadiq ya je ya sauke Farali kafin su gama makaranta shi da Innani Umra kam ya sha zuwa tun yana matashinsa.
Shekaran da suka dawo ne Innani ta fara fama da matsalan idon da yasa aka kaita asibitin ido Makka na larabawa da ke kano. Aka yanka mata gilashi Tunda ganin nata ya koma sai hankali sannan ga tsufa ammh bazata bar Halinta ba.
A rayuwar Abba in da ace yau ba Sadiq da Tuni lamarinsa ya wuce Tunanin mai karatu abunda ya zama Dole kawai ya ke yi. Ko zakka baya Fitarwa sai tasowan Sadiq yasa duk Shekara sai an fitar da Zakka sannan kuma yasa yana taimaka ma su Baba Sammani da kudi duk Damina suna yin Noma domin ci da iyalansa sannan in zasu tafi sai an cika booth da kayan abinci.
Gidan Innani da ta gada Tun iyayenta Abba ya gyara nan suke sauka in sun zo garin ,Sadaka ko akai akai Sadiq kan saka Abba na yi, ko a masallaci yaji ana neman taimako zai ce Abba zamu ba da namu taimakon Abba bashi da mgana sai dai yace zamu taimaka musu magajin gida.
Shiyasa yadda Mutane ke ganin kima da Girman Magajin gida wlh Alhaji Sulaiman ba shi da wannan kimar.
Kannenshi Mata su Hassu dalilin Sadiq su kan sazo gidan su da iyalansa su yi kwanaki sai dai zasu sha Mgana da Habaici bakin Innani ta yi ta fadin Sulaimanu ba mai kudi ba ne Rufin asirin Allah ne.
Wayar Sadiq ko da yaushe cikin kiransa yan'uwa suke yi, Alhaji Sulaiman kuwa wani sai ya jima bai kirashi ba Ammh Sadiq sha yanzu ne kuma mganin yanzu.
Da ka kira shi ka gayamasa matsalan ka shikenan.
Ko'ina ka je addu'a ce da Fatan alheri ga Alhaji da iyalansa Sanadin Sadiq Magajin gida.
*Littafin TSAKA MAI WUYA paid book ne, iya Book 1 ne free Pay N500 For BOOK 2,3. Regular group or VIP GROUP N1000. Via 0552179550 Jamila Umar gt bank.*
*Shedar biya ta wad'anan lambobin 09069067488 or 08032773332.*
*SPECIAL GROUPS Follow@Jamilaumarjanafty On AREWABOOKS mutanen mu na Niger za su Tuntubi Kausar Aglan nissa +22796562223 Nagode*
*Janafty*
*TSAKA MAI WUYA.*
*Wattpad:Jamilaumar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*
*11*
*Zariya*
Laraba.
Abubuwa biyu ne suka min tsaye a kahon raina a kwanaki nan.
Na farko yau kwanaki biyar cur mutumin da ke siyan Danwaken Sannan kuma ya kuma bar min chanjin naira na gugan naira har Dari biyu ya daina zuwa.
ina lissafe tun Alhamis da ya aiko aka siya masa bai kara dawowa ba har ga shi yau talata. Tun safe na ke duban hanya ammh shuru har su datti na kira na tambaye su sukace suma sun daina ganinsa yana zuwa. Acikin raina na ke ta faman wasi wasin to lafiya?
Wata zuciyar kuma ta kwab'eni da cewa"Hasiya kada zak'ewar ki ta cika yawa fa."
Nima sai daga baya naga na zak'en gaskiya mutumin da ban taba sani ba me yasa zan damu kaina Saboda shi? Sai wata zuciyar tace min ko ban san shi ba Cinikayar ya had'amu kuma sanin Mu'malace ka yi cigiyar abokin Cinikaryar ka.
Tun Safe da na zauna kujeran saka Danwake a tsakar gida na ke ta faman duba kofar gida da naga yaro ya shigo sai na Dauka shine, ammh kuma rashin ganin yar kular da ya saba aikowa ke sakarmin da gwiwa.
Maganar gaskiya ina cikin zullumi Ajiyar rai na sauke lokacin da Goma ta gota na gama Saka Danwake gabadaya har ya kare iya wanda zan ci kad'ai na rage.
Suna kaunarshi kamar yadda ya ke kaunarsu. Duk da Mama na taba kishi da Umma ganin Innani ta fi sonta sannan ita ce uwar Magajin gida ammh bata isa ta raba kan ya'yan gidan ba. Ba bambamci Tsakaninsu duk Daya suka Dauki junansu musamman Sadiq ko da ya ke karami a acikinsu yana da kyakyawan Tunani mai kyau tunda ya karanta kuma ya gani.
Bayan Sadiq Mama ta kara Haihuwan Salima da Siyama wacce itace karama daga ita aka rufe haihuwa agidan Siyama ta zama autan Gidan. Sadiq kuma ya kasance Autan Umma Shalelen Abba da Innani.
Dukkansu matan sun yi aure a garin Gusai, Suba'atu ke aure a kano sai Saddiqa da ke kebbi.
A dakin Mama kuwa Sa'ima da Sakeena suma suna Gusai ne suna aure. Sahida na aure a katsina ita kuma Saliha na auran yaron yayar Mama ce suna garin Ibadan da zama in da ya ke aiki a kamfanin Dangote.
Kuma kowacce ta na jin dadi agidan da mijinta sun kuma hayayyafa da ya'yen su turbarkallah masha Allah.
Lokacin da Sadiq ya kamallah makaranta cikin yan'uwan sa ba wacce ta so ya yi bautar kasa a zariya ammh kuma Tunda yace chan zai yi ba su da tacewa barin ma Surayya da suke kira Big sis taso yaje kasar waje ya yi karatun liktanci tare da kanin Mijinta Sadiq yace baya ra'ayin haka.
Da farko Har Abba da Umma sun Amince Innani ma ta samu ta shawo kanta ammh A'a din Sadiq kad'ai ya isa da ya Rusa komai.
Dole a kabarshi ya tafi zariya again Bautar kasa. A wannan karon ma Abba yaso ya siya masa gida yace shima baya Ra'ayi sai haya ya kama da Farko a Daura Tahir ya so ya yi nasa Hidimar kasar ammh Ganin Sadiq ya koma zariya shima ya nema ya koma Saboda Abotan da ke tsakaninsu ta yi nisan da har Ahalin juna sun sani.
Sadiq yadda ake son shi yasa ko Kashi ya kai gida ya ke da Daraja. Shiyasa Tahir ya ke kamar dan gida a gidan su Sadiq duk kuma abunda Sadiq yace ayi masa Abba ba gaddama ya ke yi masa. Ranar farko da Tahir yazo yaga irin gatan da Sadiq ke ciki bayan sun koma Zariya ya kallesa yace"kai ko wani irin abu ka ke samu a garin nan da ka zabi irin wannan Rayuwar Alhalin kai dan gata ne?
Sadiq mirmishi kawai ya yi masa bai ce komai ba, Sadiq ya je ya sauke Farali kafin su gama makaranta shi da Innani Umra kam ya sha zuwa tun yana matashinsa.
Shekaran da suka dawo ne Innani ta fara fama da matsalan idon da yasa aka kaita asibitin ido Makka na larabawa da ke kano. Aka yanka mata gilashi Tunda ganin nata ya koma sai hankali sannan ga tsufa ammh bazata bar Halinta ba.
A rayuwar Abba in da ace yau ba Sadiq da Tuni lamarinsa ya wuce Tunanin mai karatu abunda ya zama Dole kawai ya ke yi. Ko zakka baya Fitarwa sai tasowan Sadiq yasa duk Shekara sai an fitar da Zakka sannan kuma yasa yana taimaka ma su Baba Sammani da kudi duk Damina suna yin Noma domin ci da iyalansa sannan in zasu tafi sai an cika booth da kayan abinci.
Gidan Innani da ta gada Tun iyayenta Abba ya gyara nan suke sauka in sun zo garin ,Sadaka ko akai akai Sadiq kan saka Abba na yi, ko a masallaci yaji ana neman taimako zai ce Abba zamu ba da namu taimakon Abba bashi da mgana sai dai yace zamu taimaka musu magajin gida.
Shiyasa yadda Mutane ke ganin kima da Girman Magajin gida wlh Alhaji Sulaiman ba shi da wannan kimar.
Kannenshi Mata su Hassu dalilin Sadiq su kan sazo gidan su da iyalansa su yi kwanaki sai dai zasu sha Mgana da Habaici bakin Innani ta yi ta fadin Sulaimanu ba mai kudi ba ne Rufin asirin Allah ne.
Wayar Sadiq ko da yaushe cikin kiransa yan'uwa suke yi, Alhaji Sulaiman kuwa wani sai ya jima bai kirashi ba Ammh Sadiq sha yanzu ne kuma mganin yanzu.
Da ka kira shi ka gayamasa matsalan ka shikenan.
Ko'ina ka je addu'a ce da Fatan alheri ga Alhaji da iyalansa Sanadin Sadiq Magajin gida.
*Littafin TSAKA MAI WUYA paid book ne, iya Book 1 ne free Pay N500 For BOOK 2,3. Regular group or VIP GROUP N1000. Via 0552179550 Jamila Umar gt bank.*
*Shedar biya ta wad'anan lambobin 09069067488 or 08032773332.*
*SPECIAL GROUPS Follow@Jamilaumarjanafty On AREWABOOKS mutanen mu na Niger za su Tuntubi Kausar Aglan nissa +22796562223 Nagode*
*Janafty*
*TSAKA MAI WUYA.*
*Wattpad:Jamilaumar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*
*11*
*Zariya*
Laraba.
Abubuwa biyu ne suka min tsaye a kahon raina a kwanaki nan.
Na farko yau kwanaki biyar cur mutumin da ke siyan Danwaken Sannan kuma ya kuma bar min chanjin naira na gugan naira har Dari biyu ya daina zuwa.
ina lissafe tun Alhamis da ya aiko aka siya masa bai kara dawowa ba har ga shi yau talata. Tun safe na ke duban hanya ammh shuru har su datti na kira na tambaye su sukace suma sun daina ganinsa yana zuwa. Acikin raina na ke ta faman wasi wasin to lafiya?
Wata zuciyar kuma ta kwab'eni da cewa"Hasiya kada zak'ewar ki ta cika yawa fa."
Nima sai daga baya naga na zak'en gaskiya mutumin da ban taba sani ba me yasa zan damu kaina Saboda shi? Sai wata zuciyar tace min ko ban san shi ba Cinikayar ya had'amu kuma sanin Mu'malace ka yi cigiyar abokin Cinikaryar ka.
Tun Safe da na zauna kujeran saka Danwake a tsakar gida na ke ta faman duba kofar gida da naga yaro ya shigo sai na Dauka shine, ammh kuma rashin ganin yar kular da ya saba aikowa ke sakarmin da gwiwa.
Maganar gaskiya ina cikin zullumi Ajiyar rai na sauke lokacin da Goma ta gota na gama Saka Danwake gabadaya har ya kare iya wanda zan ci kad'ai na rage.