← Book details Tsaka Mai Wuya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 37 OF 69

Sashe 37

Tsaka Mai Wuya Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Washegari saboda zuwan Ramatu sai ban kwab'a danwake da yawa ba. Tunda tace min sabon gari ta kwana kenan zata iso nan da wuri, shiyasa tun safe na tashi na fara aikin Habiba ta taimakamin da wura gawayi ni har ta sakamin tukunyar Farko.
Daga baya na amsheta ta shiga wanka Saboda tafiya makaranta.
Cikin ikon Allah yau sai ga Mutumin ya aiko Datti da gudunsa ya zo min da kular ya na washe baki ya ce"Adda Hasiya ga Mutumin nan ya zo"
Bansan dalili ba sai da naji wani sanyi a raina na karbi kular da Sauri tare da dubu d'ayan da ya ke ba ni.
Ga mutane na layi ammh sai da na saka masa sannaan na mika ma Datti ina Fad'in"Ka ce masa mai Danwake tace lafiya kwana biyu bai zo ba?
Sai Faman mirmishi na ke yi ni kadai Har sai da Datti ya Dawo yana cemin"Yace tafiya ya yi shiyasa."
Kad'a kaina na yi a fili nace"Haba shiyasa naji sa shuru ashe.."
Har Datti ya juya na sake kwalamasa kira ya dawo na kallesa kafin nace"Tambayarka zan yi. Mutumin nan da ke aiko ka yaro ne ko babba?
Da Sauri Datti yace"Kai Babba ne fa."
Ya fad'a cikin nuna yarintarsa.
Da gudu kuma ya fita ya barni ina mamakin kaina na miye nawa na son sanin yaro ne ko Babba?.
Yau cikin Nishad'i na cigaba da Saka Danwake na zuwa tara na gama komai na share wajen, sannan na wanke kwanukan da na taba girki zan yi saboda zuwan Ramatu. Ammh sai nace bari sai tazo kada na Dafa ya yi sanyi.
Amma na fara saka ma ruwan wanka na juye mata ta yi tunda jiya bata samu yi ba, kokon da na Dama mata na sha nima tunda ba shi da Tsami sai waken da na saka masa manja kadan naci saboda kumburin ciki.
Kafin ta fito wanka na gyara dakin na Share ta na fitowa nima na shiga na yi, koda na fito na isketa ta shirya ta na zaune ta na shafama kafafuwanta man zafi.
Cikin yanayin mganarta tace"Hasiya nace ki siya ko karamar waya ce. Ta na da amfani tunda ga shi ina ta son na kira Adda mu gaisa ba wayar da zan kirata."
Ina shafa ma jikina Vaselin nace"Amma zan siya. Ki bari riban ya kara taruwa ba na so na taba ne kuma mu shiga har uwar kudin"
Amma ta yi mirmishi kafin tace"Hasiya ina zaki kai wannan tattalin naki?
Dariya na kyalkyalce da shi kafin nace"Amma rayuwar nan sai mutum ya iya tattali ballatana yadda Tsadar rayuwa ya kara Hauhawa."
Amma ta jinjina kai kafin tace"Hakane ina miki Fatan watarana mijinki ya Mori wannan Tattalin naki da hangen nesan da Ubangiji ya mallaka miki su Hasiya."
Na ji add'aunta acikin raina na amsa da Ameen batare da na ji acikin raina hakan zai iya kasancewa ba.
Na riga na Sadakar na gama aure a Duniya baxan kara yarda na auri wani ba. Ballatana nazo na zame masa matsala a rayuwarsa. Iya bakin Fentin da shafa ma kaina Dalilin Aure ya isheni ba na kuma Bukatar karin wani Tozarcin.
Amma itama ta Fahimceni sai ta sauya Hirar zuwa ta Adda Fati ta na Fadin"Oh Fati shuru kwana biyu bata zo ta dubamu ba."
Ina Zura Doguwar riga a jikina nace"kinsan ta yi ta fama da Zazzabi ita da yara. Ta na samun Sarari zaki ganta, Adda Rukayyace ma naga kwana biyu yan ganin Damanta ba su turo ta zo ba."
Amma tace"Itama sai da nayi mganarta a raina. Allah yasa suna lafiya su da iyalansu"
Ina Daura Dankwali nace"Amma lafiya ke shuru fa. Suna nan lafiya da wani abu ya faru da mun sani."
Amma na shirin mgana mukaji sallamar Adda Fati suna gaisawa da su Maman Boy.
Na kalli Ammi ta kalleni kafin nace"Amma Muryan Adda Fati ce fa."
Amma tace"Baiwar Allah ina ta zencen ta sai ga ta"
Ta na ko dago labule ta shigo nace"Kinsan yanzu Amma ke mganar ta ji ku shuru ke da Adda Rukayya Allah yasa kuna lafiya"
Ta na Sauke goyon Hanifa da ke bayanta gefen Amma lokaci daya ta na Fadin"Zazzabin da muka sha ne da yara duk jikina ba Dadi. Babansu ma sai yau ya fara fita aiki. shi har da Basir ne ya tasar masa."
Ni da Amma muka had'a baki wajen fadin"Subhanallah." Na dauki Hanifa sai naga barci take yi na mikama Amma ina Fadin"Habi ai tace har Hanifa ta sha Zawon hakuri."
Adda Fati tace"Sosai ammh duk mun samu sauki su har sun tafi makaranta shima yau ya tafi na gaji da zaman gidan nace bari na biyosa ya saukeni agida kawai na duba ku."
Ledan da ta shigo da shi ta mikama Amma tana fadin"Sabulai ne da Manshafawa Amma. Ba kudi ne duk mun cinye a asibiti"
Amma tace"Bakomai Fati. Allah ya yi albarka ya azurta mijinki da kudin Halal ya shirya muku zuru'a."
Muka amsa da Ameen Ameen.
Kallona ta yi kafin tace"Hasiya wlh rashin wayarki na damuna kana son mgana da ku ammh sai ka kira makota."
Amma tace'Nima tsiyar da na ke mata ko da yaushe kenan. Kinsan ta da rashin son kashe kud'i ba Dalili."
Adda Fati tace"Kamar wata ma'aikaciyar gwammati ba. Komai ace sai an yi shi cikin Tsari."

Dariya kawai na yi bance komai ba.
Ina kusa da Amma ina kallon Hanifa da ke hannunta ta na barci.
Adda Fati ashe kallo na ta ke yi sai da na Dago muka had'a ido cikin ware mata ido nace"Na yi miki kyau ne wannan kallon fa Adda Fati"
Adda Fati tace"Kin kara fari ne sannan atamfar nan ta na yi miki kyau in kika sakata"
Na bi Atamfar jikina da kallo wata Bakar Atamfa ce Chiganvy baka da Fara ce tun ta akwatin aurena da Abubakar ne. Ba tun yau ba in dai na saka Atamfar ne sai mutane sun ce ta na yi mini kyau.
Dukkansu ni suka bi ni da kallo, ni kuma tuna Abubakar yasa yanayi na kawai ya sauya Amma ce ta ce"ki gayamata ta rage tunani baki ga ta na ta ramewa ba ne"
Adda tace"Amma Hasiya fa daman ka shi da rai ne. Tunanin rayuwa kuma Dole ne Amma. hasiya ki yi hakuri In sha Allahu Mijinki na Har Abada ya kusa zuwa. Wanda zaki Daura kayansa ki yi ta Daurawa har Abada."
Mirmishi kawai na yi ban yi mgana Ameen din ma wannan karon ban ce ba.
Hira Amma da Adda Fati suka cigaba da yi ni kuma sai na jingina da Bango na fada kogin Tunanin irin Rayuwar da muka shinfida da Abubakar. Sai ga shi cikin wattani uku komai ya zama Sai Tarihi. Tunanin da na lula yasa ko sallamar Ramatu ban ji ba sai da naji Challara kukan Noor sannan na san har ta iso. Na bita da kallo har ta zauna kusa da ni ta na gaida Amma Noor kuma na Hannun Adda Fati har ta fara kuka.
Cikin kasalan da ya Rufeni nace"Yaushe kika shigo.?
Tana mirmishi ta kalleni kafin tace"Lokacin da kika shiga kogin Tunani mana"
Sai kawai na yi mata mirmishi. Ta shi nayi na je na Debo musu ruwa. Na Dauki Dubu daya na fita tsakar gida ba yaran sai na leka waje Hamisu na gani yayan Salihi shi na ba ma wa nace ya siyomin lemun panta guda Biyu.
Ban dawo ba sai da na jirasa ya dawo sannan na Dawo Dakin. na ijiye mata a gabanta duka ta kalleni ta na fadn''Ji don Allah kamar wata bakuwa."
Ina Hararanta nace"Eh mana ke ai bakuwa ta ce mana ko Amma?
Amma tace"Ni ma Ramatu bakuwatace. Ammh kuma yar gida ce Tunda diyata ce"
Adda Fati tace"Kwarai kuwa. Hasiya karbi yarku mai kiyuya."
Ina Dariya na karbi Noor ina mata wasa. Fita na yi waje in da su Maman Salihi suke ganina da Noor yasa maman Boy ta karbeta tana Fadin"Yarinyar ta yi yawo fa".
Yake nayi kafin nace"In ba damuwa zamu zauna a dakin ki ni da Ramatu maman boy."
Cikim Fara'a tace"Haba Hasiya me zai hana? Na taba miki shamaki da Dakina ne?
Karaf Maman Salihi ta karbe da Fadin"Ballatana ni. Ko ya'yana ban muku shamaki da su ba, aike ko gaban anguwan nan ne ta aike su zasu je."
Mirmishi nayi kafin na karbi Noor ina Fadin"To nagode"
Na juya naji Kaltume da ke jajjagen kayan miya tace"Uhm ku dai bi a Hankali kada mu ji gobara ta fara bin Dakuna."
Ina mamakin meyasa Kaltume ta ke wasa da Kaddara ta? Ko don ita yarinyace domin ko haihuwa bata tabayi ba shekararta daya ne da wani abu a gidan bata wuce sa'ata ba ga rawan kai ga munafunci ga Gulma.
Ni dai shigewata daki nayi ban biye mata ba na iske Ramatu da Adda Fati na ta Hira. Zani na Dauka na goya Ramatu na Dauki mata lemonta nace tazo muje Dakin Maman Boy.
Ba musu ta taso ta na ce ma su Amma'"Adda bari mu je"
Suka amsa mana da Toh.
Chapter 37 · 0% Book details