Sashe 51
Tsaka Mai Wuya Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Ina komawa gida na iske dakin sakayashi kawai akayi, Gawayi na fara Hurawa na saka ruwan zafi sannan na gyara dakin na Share.
Matan gidanmu sai fad'a min su ke yi an yi ta zuwa neman Danwake babu. Ya ke kawai na yi musu ana ta rai wa ke ta wani Danwake.
Sai da na yi wanka na cire kayan jikina na saka wata atamfa Riga da Sikat na siya kamu na Dama na sha, sannan na Dorama Amma ajug zan kai mata asibiti na kuma Daukan mata zannuwa da Hijabi nima na Dauki kaya kala d'aya da Hijabi sai abunda zan gyara jikina Tunda ba na Sallah.
Sai yammah na Rufe Dakin Amma da makulli na koma asibiti. Adda kad'ai na iske Ramatu ta tafi, itama ina Dawowa ba Dadewa ta tafi akan sai gobe zata dawo. Ni na kwana da Amma wacce ta ji sauki sosai likita ya zo ya dubata sannan Nurse suna zuwa bata mgani da saka mata ruwa.
Washegari na yi ma Amma wanka Tunda ga bayi sannan akwai Ruwa. Da ya ke na Tsaftace makewayin yasa nima na shiga na yi wanka na gyara jikina.
Har rana ba wanda ya zo. na zo da kudi a hannuna na fita waje na siyo ruwan zafi da kayan tea na zo muka had'a tea ni da Amma muka sha ni kuma sai na had'a da waina.
Nazo da magunguna nima na balla na sha Amma ta na yawan yin barci Saboda inaga allurai da magunguna da suke bata tunda sun ce Hutu ta ke Bukata.
Wani abun mamaki da na ji karan Bude kofa sai na juyo da Sauri na zata ko Shine sai naga bashi ba ne.
Har Adda Fati ta zo da rana, zuwa la'asar sai ga Adda Rukayya da Habiba sai bani Hakuri ta ke yi da abunda ya Faru ta na gayamana ta yi ma Babansu Amna Hauka da yasa Dole sai da yaje ya ja ma yan'uwansa kunne.
Ban ce komai ba sai da ta Dafani ta na Fad'in"Ki yi hakuri don Allah Hasiya."
Sai na girgiza kai kafin nace"Bakomai Adda."
Amma na barci sai daga baya ta tashi. Maltina na bata tasha na rakata bayi tunda sun cire mata karin ruwa alwala ta Dauro.
Tazo ta yi sallolinta daga zaune daman da Safe haka ta yi ammh Alhamdulillah jiki da sauki.
Adda Fati ne tace"Amma ko na kira Adda na fad'a mata?
Amma tace''A'a kada ki tada mata Hankali kyaleta kawai."
Daman nasan haka Amma zata ce, ko ciwo ta ke yi bata son a kira mata Adda kada wai a tada mata Hankali.
Adda Fati da Adda Rukayya tare suka tafi sai aka bar min Habiba tare da ni.
Ba matsalan abinci Adda Fati ta zo min da Fanten doya da allayahu.
Har na cire rai da zuwansa sai ga shi da Daddare bayan isha'i sun zo da abokinsa mara sakewa da Mutane sai akaci sa'a Amma na farke ba ta koma barcinta na fama.
Sanda suka shigo ina bayi sai Habiba kadai suka iske kallon rashin sani Sadiq ya yi mata. Ita ma haka ta yi masa sai dai ya ga kamarta da Amma da Adda Fati su suna da jan fata ba irin Fari na garesu ba.
Habiba ta gaishesu suka amsa suna tambaya ya mai jiki?
Habiba tace ta samu sauki gata nan ma ba ta koma barcin ba.
Tahir dai na daga baya Sadiq ne ya karisa gaban gadon Amma.
Sanye ya ke da kananun kaya Riga da wando. Rigar mai kalan Ruwan kasa da layi layi ta na da Dogon Hannu. Wandon kuma mai ruwan kasa ne kafarsa cikin Rufaffen takalmi.
Amma tunda ta gansa jikinta ya bata Bawan nan ne Allah da ya kawota asibiti.
Daman tun dazu ta ke ma Hasiya mgana sai tace mata bai zo ba.
Yana gaisheta ta amsa cikin Sakewa lokaci d'aya tace"Abubakar ne?
Cikin mamaki ya ce"Eh ni ne Mama."
Amma ta muskuta ta na son mikewa da Sauri ya kamata ya na kara mata Filo ta baya.
Amma ta kallesa haka kurum taji Saurayin ya shiga ranta.
Cikin Mirmishi da muryan ciwo tace"Nagode Allah ya yi maka albarka."
Ya amsa da Ameen sai lokacin Tahir ya kariso ya na mata sannu ta amsa masa shima cikin sakewa.
Sadiq yace"Abokina ne."
Amma ta jinjina kai kafin tace"Allah Sarki nagode sosai Hasiya ta ba ni labarin irin taimakon da kayi mana. Allah ya ba ka lada. Allah ya biya ka da gidan Aljannah"
Da Ameen Ameen ya ke ta amsawa.
Tahir ko na gefe ya na bin ko'ina da kallo fuskar nan dihim.
Ya rasa dalilin Sadiq na matsa masa sai ya rakosa asibitin nan. Ka taimaki mutane to ba sai ka rabu da su ba ina laifi? Ammh lamarin Sadiq sai Allah kawai da ya Hallicesa game da maida lalura da Damuwan Mutane na shi.
Amma ta kalli Habiba ta na fad'in"Habi Hasiyan ba ta fito ba ne?
Habiba tace"Ba ta fito ba Amma."
Sai Amma ta kallesu ta na Fad'in"Hasiyan ta shiga makewayi ne."
Sadiq ne ya gyad'a mata kai, Suna Tsaye dai daga gefe ledan da Sadiq ya shigo da ita a hannun ya mikama Habiba ta karb'a ta na fadin"Angode."
Sai ta duba abunda ke ciki Taga Tsire ne mai yawa da Sauri tace"Amma nama ne."
Ta fad'a cikin jin dadi. Daman Habi da son Nama kamar wata kura. Amma ta yi mirmishi kafin tace"Allah ya ba da Lada. Allah ya yi shi albarka"
Dukkansu ba su amsa ba Tahir sai danna wayarsa ya ke yi shi kuma Sadiq ya harde hannayensa saman Kirjinsa.
Kai tsaye na fito daga makewayin. Tabbas na ji mganganu ammh ban Dauka shi ba ne. Na zata nurses ne ko Likita sai da na fito dagani sai Doguwar rigar jikina da Dankwali.
Kuma ta facing dinsa na fito daidai ya Dago nima na Dago mu ka had'a ido.
Wlh sai na ji kunya. na dukar da kaina kafafunawa na rawa na fara takowa cikin Dakin.
Amma ta tareni da Fadi'n "Sun zo tun dazu Hasiya."
Tahir a ransa ya maimaita Sunan Hasiya a ranshi.
Tabe baki ya yi yace daman ai daga ganinsu kauyawa ne.
Kuma ta dace da sunan nata Hasiya.
Ban samu natsuwa ba sai da na Rarumi Hijabina na zura sannan na gaishesu Abubakar ne kad'ai ya amsa cikin Sakewa Tahir daga lafiya shikenan bai kara ba.
Habiba ta nuna min Naman da suka zo da shi,godiya na yi masa bai amsa ni ba illah cewa da ya yi"Kuka ya kare ko? Tunda naga jikin Maama ya yi Sauki ko?
Ban ce komai ba sai dai na Rufe Fuskata da Tafin hannayena.
Amma ce ta amsashi da cewa"Hasiya ai sarkin kuka ce. Ita dai in dai ta ganni ina ciwo bata kara sukuni sai ta ganni na warke tukunnah."
Sadiq yace"Allah sarki. To ta kwantar da Hankalinta kin samu lafiya."
Amma tace"Ah Alhamdulillah. Jikina ne kawai ba karfi."
Sadiq yace"Shima a hankali zaki ji ki warware."
Amma tace"In sha Allahu."
Shuru na wani lokaci ba wanda ya yi mgana Tahir na kuncin ya gaji da Tsayuwa Sadiq kuma na Tunanin Jikin Hasiya da yanayinta ya boye Shekarunta. In dai ya canka daidai Yarinyar nan kanwarta ce kenan ta girmi Sultana sai dai kila sa'ar Salima.
Amma ce ta katse masa da Tunani da Fad'in"A nan garin ku ke ne?
Sadiq yace"A'a Mama karatu mu ke yi anan d'in."
Amma tace"Allah Sarki Allah ya taimaka."
Sadiq ya amsa mata.
AMMA bata gaji ba ta kara kallonsu ta na Fad'in"To a wani gari ku ke ne?
Tahir ya kallesa shima ya kallesa ganin Haka yasa Amma tace"ku yi hakuri ina son sani ne saboda taimakon da ka yi mana."
Sadiq ya jinjina kai kafin yace"Ni d'an kauyen Shinkafi ne da ke zamfara. Abokina kuma mutumin Daura ne."
Tahir ya kura masa ido ya na mamakin meyasa Sadiq ke son boye kansa.
Bai gama mamaki ba yaji Amma na tambayan akwai iyaye ko babu?
Bude ido ya yi da hanci ya na kallon Sadiq sanda yaji ya na fad'in"Ba bu Mama a kauyen mu na taso hannun Dangin mahaifina"
Amma cikin Tausayawa tace"Allah sarki.Allah ya jikansu da Rahma kada ka damu ni ka Dauke ni a matsayin uwa kaji ko?
Sadiq ya jinjina kai ya na fadin"Nagode Mama."
Tahir mamaki bai barsa ya yi mgana ba.
Matan gidanmu sai fad'a min su ke yi an yi ta zuwa neman Danwake babu. Ya ke kawai na yi musu ana ta rai wa ke ta wani Danwake.
Sai da na yi wanka na cire kayan jikina na saka wata atamfa Riga da Sikat na siya kamu na Dama na sha, sannan na Dorama Amma ajug zan kai mata asibiti na kuma Daukan mata zannuwa da Hijabi nima na Dauki kaya kala d'aya da Hijabi sai abunda zan gyara jikina Tunda ba na Sallah.
Sai yammah na Rufe Dakin Amma da makulli na koma asibiti. Adda kad'ai na iske Ramatu ta tafi, itama ina Dawowa ba Dadewa ta tafi akan sai gobe zata dawo. Ni na kwana da Amma wacce ta ji sauki sosai likita ya zo ya dubata sannan Nurse suna zuwa bata mgani da saka mata ruwa.
Washegari na yi ma Amma wanka Tunda ga bayi sannan akwai Ruwa. Da ya ke na Tsaftace makewayin yasa nima na shiga na yi wanka na gyara jikina.
Har rana ba wanda ya zo. na zo da kudi a hannuna na fita waje na siyo ruwan zafi da kayan tea na zo muka had'a tea ni da Amma muka sha ni kuma sai na had'a da waina.
Nazo da magunguna nima na balla na sha Amma ta na yawan yin barci Saboda inaga allurai da magunguna da suke bata tunda sun ce Hutu ta ke Bukata.
Wani abun mamaki da na ji karan Bude kofa sai na juyo da Sauri na zata ko Shine sai naga bashi ba ne.
Har Adda Fati ta zo da rana, zuwa la'asar sai ga Adda Rukayya da Habiba sai bani Hakuri ta ke yi da abunda ya Faru ta na gayamana ta yi ma Babansu Amna Hauka da yasa Dole sai da yaje ya ja ma yan'uwansa kunne.
Ban ce komai ba sai da ta Dafani ta na Fad'in"Ki yi hakuri don Allah Hasiya."
Sai na girgiza kai kafin nace"Bakomai Adda."
Amma na barci sai daga baya ta tashi. Maltina na bata tasha na rakata bayi tunda sun cire mata karin ruwa alwala ta Dauro.
Tazo ta yi sallolinta daga zaune daman da Safe haka ta yi ammh Alhamdulillah jiki da sauki.
Adda Fati ne tace"Amma ko na kira Adda na fad'a mata?
Amma tace''A'a kada ki tada mata Hankali kyaleta kawai."
Daman nasan haka Amma zata ce, ko ciwo ta ke yi bata son a kira mata Adda kada wai a tada mata Hankali.
Adda Fati da Adda Rukayya tare suka tafi sai aka bar min Habiba tare da ni.
Ba matsalan abinci Adda Fati ta zo min da Fanten doya da allayahu.
Har na cire rai da zuwansa sai ga shi da Daddare bayan isha'i sun zo da abokinsa mara sakewa da Mutane sai akaci sa'a Amma na farke ba ta koma barcinta na fama.
Sanda suka shigo ina bayi sai Habiba kadai suka iske kallon rashin sani Sadiq ya yi mata. Ita ma haka ta yi masa sai dai ya ga kamarta da Amma da Adda Fati su suna da jan fata ba irin Fari na garesu ba.
Habiba ta gaishesu suka amsa suna tambaya ya mai jiki?
Habiba tace ta samu sauki gata nan ma ba ta koma barcin ba.
Tahir dai na daga baya Sadiq ne ya karisa gaban gadon Amma.
Sanye ya ke da kananun kaya Riga da wando. Rigar mai kalan Ruwan kasa da layi layi ta na da Dogon Hannu. Wandon kuma mai ruwan kasa ne kafarsa cikin Rufaffen takalmi.
Amma tunda ta gansa jikinta ya bata Bawan nan ne Allah da ya kawota asibiti.
Daman tun dazu ta ke ma Hasiya mgana sai tace mata bai zo ba.
Yana gaisheta ta amsa cikin Sakewa lokaci d'aya tace"Abubakar ne?
Cikin mamaki ya ce"Eh ni ne Mama."
Amma ta muskuta ta na son mikewa da Sauri ya kamata ya na kara mata Filo ta baya.
Amma ta kallesa haka kurum taji Saurayin ya shiga ranta.
Cikin Mirmishi da muryan ciwo tace"Nagode Allah ya yi maka albarka."
Ya amsa da Ameen sai lokacin Tahir ya kariso ya na mata sannu ta amsa masa shima cikin sakewa.
Sadiq yace"Abokina ne."
Amma ta jinjina kai kafin tace"Allah Sarki nagode sosai Hasiya ta ba ni labarin irin taimakon da kayi mana. Allah ya ba ka lada. Allah ya biya ka da gidan Aljannah"
Da Ameen Ameen ya ke ta amsawa.
Tahir ko na gefe ya na bin ko'ina da kallo fuskar nan dihim.
Ya rasa dalilin Sadiq na matsa masa sai ya rakosa asibitin nan. Ka taimaki mutane to ba sai ka rabu da su ba ina laifi? Ammh lamarin Sadiq sai Allah kawai da ya Hallicesa game da maida lalura da Damuwan Mutane na shi.
Amma ta kalli Habiba ta na fad'in"Habi Hasiyan ba ta fito ba ne?
Habiba tace"Ba ta fito ba Amma."
Sai Amma ta kallesu ta na Fad'in"Hasiyan ta shiga makewayi ne."
Sadiq ne ya gyad'a mata kai, Suna Tsaye dai daga gefe ledan da Sadiq ya shigo da ita a hannun ya mikama Habiba ta karb'a ta na fadin"Angode."
Sai ta duba abunda ke ciki Taga Tsire ne mai yawa da Sauri tace"Amma nama ne."
Ta fad'a cikin jin dadi. Daman Habi da son Nama kamar wata kura. Amma ta yi mirmishi kafin tace"Allah ya ba da Lada. Allah ya yi shi albarka"
Dukkansu ba su amsa ba Tahir sai danna wayarsa ya ke yi shi kuma Sadiq ya harde hannayensa saman Kirjinsa.
Kai tsaye na fito daga makewayin. Tabbas na ji mganganu ammh ban Dauka shi ba ne. Na zata nurses ne ko Likita sai da na fito dagani sai Doguwar rigar jikina da Dankwali.
Kuma ta facing dinsa na fito daidai ya Dago nima na Dago mu ka had'a ido.
Wlh sai na ji kunya. na dukar da kaina kafafunawa na rawa na fara takowa cikin Dakin.
Amma ta tareni da Fadi'n "Sun zo tun dazu Hasiya."
Tahir a ransa ya maimaita Sunan Hasiya a ranshi.
Tabe baki ya yi yace daman ai daga ganinsu kauyawa ne.
Kuma ta dace da sunan nata Hasiya.
Ban samu natsuwa ba sai da na Rarumi Hijabina na zura sannan na gaishesu Abubakar ne kad'ai ya amsa cikin Sakewa Tahir daga lafiya shikenan bai kara ba.
Habiba ta nuna min Naman da suka zo da shi,godiya na yi masa bai amsa ni ba illah cewa da ya yi"Kuka ya kare ko? Tunda naga jikin Maama ya yi Sauki ko?
Ban ce komai ba sai dai na Rufe Fuskata da Tafin hannayena.
Amma ce ta amsashi da cewa"Hasiya ai sarkin kuka ce. Ita dai in dai ta ganni ina ciwo bata kara sukuni sai ta ganni na warke tukunnah."
Sadiq yace"Allah sarki. To ta kwantar da Hankalinta kin samu lafiya."
Amma tace"Ah Alhamdulillah. Jikina ne kawai ba karfi."
Sadiq yace"Shima a hankali zaki ji ki warware."
Amma tace"In sha Allahu."
Shuru na wani lokaci ba wanda ya yi mgana Tahir na kuncin ya gaji da Tsayuwa Sadiq kuma na Tunanin Jikin Hasiya da yanayinta ya boye Shekarunta. In dai ya canka daidai Yarinyar nan kanwarta ce kenan ta girmi Sultana sai dai kila sa'ar Salima.
Amma ce ta katse masa da Tunani da Fad'in"A nan garin ku ke ne?
Sadiq yace"A'a Mama karatu mu ke yi anan d'in."
Amma tace"Allah Sarki Allah ya taimaka."
Sadiq ya amsa mata.
AMMA bata gaji ba ta kara kallonsu ta na Fad'in"To a wani gari ku ke ne?
Tahir ya kallesa shima ya kallesa ganin Haka yasa Amma tace"ku yi hakuri ina son sani ne saboda taimakon da ka yi mana."
Sadiq ya jinjina kai kafin yace"Ni d'an kauyen Shinkafi ne da ke zamfara. Abokina kuma mutumin Daura ne."
Tahir ya kura masa ido ya na mamakin meyasa Sadiq ke son boye kansa.
Bai gama mamaki ba yaji Amma na tambayan akwai iyaye ko babu?
Bude ido ya yi da hanci ya na kallon Sadiq sanda yaji ya na fad'in"Ba bu Mama a kauyen mu na taso hannun Dangin mahaifina"
Amma cikin Tausayawa tace"Allah sarki.Allah ya jikansu da Rahma kada ka damu ni ka Dauke ni a matsayin uwa kaji ko?
Sadiq ya jinjina kai ya na fadin"Nagode Mama."
Tahir mamaki bai barsa ya yi mgana ba.