Sashe 50
Tsaka Mai Wuya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hasiya suna ne?
Sai kuma yaji tana fad'in bata san sunan asibitin ba.
Sai ya kalleta nima daidai na juya ina kallomsa sai ya lumshe min ido kafin ya Bude kai Tsaye yace"Ba ni wayar na fad'a mata."
Ba musu na mikamasa baayan na ce ma Adda ga shi za'ayi mata kwantance.
Karban wayan ya yi, bayan ya yi sallama sun gaisa da Adda sannan ya Fad'a mata sunan asibitin sannan suka yi sallama.
Tun bayan gama wayar sai Dakin ya Dauki shuru sai da aka kirasa a waya ya fita ya jima bai dawo ba. Sai ga shi an bude kofa ina juyowa naga Adda Fati kan gaba sai Ramatu sai Inna Talatu sai maman boy da maman Salihi da kaltume.
Ni ba ta su na ke ba mikewa na yi ina musu maraba. Ina jin Maman boy na fadin'Sannu Hasiya."
Takaici yasa ban amsa ba sun san da Sannu ne ina neman taimakon su ba su taimakamin ba.
Duka suna Tsaye gaban gadon Amma na ce ma Adda"Wa ya nuna muku dakin?
Adda Fati tace"da wayar da kika kirani, na kira sai ga shi wani Saurayi ya fito ya shigo damu har nan likita ne?
Sai na girgiza kai kafin nace"Shi ne wanda ya taimakamin aka kawo Amma asibiti. Adda tare muka kwana sai da safe ya tafi dazu nan ya dawo shi ya kashe komai da a ke bukata."
Inna Talatu tace"Allah Sarki Allah ya biyasa."
Su Adda suka amsa da Ameen su Maman boy suka fara daidaiciyar mgana wai ba su ji bugun kofata ba sai daga baya.
Ramatu ko kusa da ni ta dawo ta na fadin"Hasiya kin ci abinci!?
Na gyada kai kafin nace"Ya siyamin waina yanzu kuma ya kawo wad'anan kaya da mgangunan Amma."
Ramatu tace"Angode masa. na zo da abinci fulas ne bamu yi tunanin Daukowa ba."
Adda tace"Sai na koma na Dauko ba matsala."
Inna Talatu ta kalleni tace"ba ta farka ba ne.?
Kai tsaye nace"Ta farka ta sha ruwa ta koma sun ce jininta ne ya yi kasa."
Suka jinjina kai suna mata fatan samun lafiya.
Ba mu ji turo kofarsa ba sai jin sallamarsa muka yi.
Gabadaya mu ka juya muna kallonsa.
*Littafin TSAKA MAI WUYA paid book ne, iya Book 1 ne free Pay N500 For BOOK 2,3. Regular group or VIP GROUP N1000. Via 0552179550 Jamila Umar gt bank.*
*Shedar biya ta wad'anan lambobin 09069067488 or 08032773332.*
*SPECIAL GROUPS Follow@Jamilaumarjanafty On AREWABOOKS mutanen mu na Niger za su Tuntubi Kausar Aglan nissa +22796562223 Nagode*
*Janafty*
*TSAKA MAI WUYA.*
*Wattpad:Jamilaumar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*
https://chat.whatsapp.com/GoRzZ7ZgslV2alO5hYGAnj
*15*
Cikin takun natsuwarsa ya karisa shigowa cikin D'akin.
Yadda muka zuba masa ido ne yasa ya da'n dukar da kansa ya na fad'in"Sannun ku. Ya mai jikin?
Sai suka amsa gabadaya da sauki kafin su shiga gaishe shi ya amsa cikin sakewa Adda da Inna talatu ne suka fara masa godiya.
Kansa na kasa yace"Bakomai.."
Ni ya kallah nima daidai lokacin na Dago ina kallonsa da Sauri nace"Uhm wannan yayata ce Adda Fati. Sauran yan gidanmu ce wannan kuma kawata ce."
Na fad'a ina nuna Masa Ramatu kallonta ya yi lokaci d'aya ya na fadin"Sannun ku zuwa."
Suka amsa masa sai dakin ya dauki Shuru Adda Fati sai ta katse shurun da Fad'in"A nan garin ka ke?
Kai tsaye ya kalleta kafin yace"A'a."
Daga haka bai kara cewa komai ba.
Inna talatu tace"Angode sosai Allah ya saka maka da alheri."
Bai amsa ba kansa na kasa sai dai ya na ta faman mirmishi.
Karisawa ya yi ya duba Amma na d'an lokaci kafin yace min zai tafi.
Adda ta fara jero masa addu'o'i ita da Inna Talatu.
Baya amsawa sai dai yace bakomai kawai ammh da Inna Talatu tace"Allah ya jikan magabata. In iyayenka na raye Allah yasa su gama lafiya. In kuma ba sa raye Allah ya ba su Aljannah."
Ya na gabda zai fita ya juyo cikin mirmishi sannan ya amsa da"Ameen Ameen Nagode."
Daga haka ya fice Ramatu ta zungureni ta na fad'in"Ki raka shi mana"
Kallonta na yi sai ta gyad'a min kai daidai Lokacin da Adda ke kara fad'in"Hasiya bi shi mana. Ki kara masa godiya."
Maman boy da gulma tace"Wlh kuma daga gani asibitin akwai cacan kudi. Tunda ba ta gwamnati ba ne"
Jin haka yasa na bisa da Sauri har ya kai Haraban asibitin ya na tafiya. Sai na kasa kiran sunansa illah sauri sauri da na rika yi har na cimmasa.
Tsayawa ya yi ya na kallona kafin yace" Me yasa ki ka fito?
Kaina na kasa nace"Na zo ne na kara maka godiya."
Mirmishi ya yi kafin yace"Godiyar nan ta isa hakanan HASIYA.."
Kallonsa na yi cikin mamakin kiran sunana da ya yi sai ya ware min ido ya na fad'in"Ko ba sunan ki kenan ba?
Kai na gyad'a masa cikin kunya alamun hakane cikin yar mamaki ya kalleni ya na fad'in"Hasiya sunane? Sunan ba Asiya ba ne?
Kai na girgiza masa kafin nace"Hasiya ne sunan."
Shima cikin girgizamin kai yace"To ko dai sunan Fulani ne?
Kallonsa na yi kai tsaye kamar yadda ya ke kallona. Ya ga mahaifiyarmu da zanen Fulani a gefen bakinta, Da kuma gefe da gefen fuskarta.
Sannan yaga Adda Fati da nace yayata ce itama sai yaga yanayinta kamar na Fulani ko buzaye so ya ke ya tabbatar.
Na rasa me zan ce masa ne yasa nace"Amma ce bafullatana. Baba kuma bazazzagi ne, Sunan Hasiya kuma kanwar Baba ce da ta rasu, sai ya maida min sunanta."
Kai tsaye yace"Kenan ki na jin Fullanci.?
Kai Tsaye nace"ba na ji fa sai abunda ba'a rasa ba."
Mirmishi ya yi kafin yace"Na sha kina ji ne nace ki koyamin. ni ban iya kowani yare ba."
Baki na bude kafin nace"Wlh ni ma ban iya ba."
Yadda na yi saurin rantsewa yasa ya yi mirmishi kafin yace"Ban ce ki rantse ba. Yanzu ammh gida zaki koma ki yi wanka ki huta ko?
Ni ban yi wannan Tunanin ba sai da ya fad'a sai na kara bin kaina da kallo yarkace yarkace kamar yar gudun Hijira.
Sai naji kunya na dukar da kaina ina wasa da gefen zanin Amma da na yi Lullubi da shi.
Shi ko bai damu ba kai tsaye yace"Gaskiya ya kamata ki je gida ki Huta."
Da toh na amsa shi har mun yi sallama akan gobe zai dawo ya kara Duba Amma da jiki. Na juya zan koma cikin asibitin sai ya kawai naji muryansa cikin kaushi ya kira sunana.
"Hasiya.."
Da sauri na juyo ina fad'in"Na'am.."
Ya na daga in da ya ke yace"Ki kwantar da Hankali zata warke kin ji ko?
Sai na gyada masa kai. Mirmishi ya yi ya juya ya fara tafiya sai ga shi na Tsaya har sai da ya bace ma ganina.
Mirmishi na yi acikin raina nace"Daman ma su suna Abubakar suna da kirki da jin kai."
Cikin asibitin na koma na iske duk sun fito waje Adda Fati ne ke tare da Amma aciki sai na karisa kusa da Ramatu na zauna muka kara gaisawa.
Nura na tambaya tace min da Safen nan ya wuce na gyada kai ina masa Fatan isa lafiya.
Noor ta ke ba ma Nono sai da ta gama na karbeta ina yi mata wasa. kallona ta yi kafin tace"Ya jikin ki ke ma?
Kai tsaye nace"Ni ai na warware."
Da sauri tace"Sai kumburin Fusakarki bai sabe ba."
A hankali nace"Zai washe shima."
Ramatu tace"Ki ci abinci ga shi nan na Fito miki da shi."
Na amsa mata da toh.
Tazo da filet da cokali sai na Dibi abincin naci Faten wake ne da kifi kadan ma naci saboda cikina ba ya min dad'i.
Ramatu tace"Yakamata ki je gida ki yi wanka ki sauya kayan jikin ki."
Kai Tsaye nace"Shima haka ya ce."
Ramatu tace"Shi wa?
Cikin sigar mamaki. Mirmishi na yi kafin nace
"ABUBAKAR SADIQ.."
daga kasan raina na fad'i sunan saboda Muhimmanci da sunan ke da shi a Rayuwata.
Ramatu tace"Au Abubakar Sadiq sunansa? Ma sha Allah wai a ina kuka had'u?
Kallonta na yi kafin na fara bata labarin hadu'warmu na karishe da fad'in"Saboda Rudewa haka na zo asibitin nan ba takalmi. Bawan Allah nan takalminsa ya bani na saka sai da ya fita ya siyomin wannan sannan ya karb'i na shi. Ramatu gaskiya ya na da kirki tare da abokinshi suka kwana a asibitin nan da Amma fa."
Ramatu tace"Gaskiya ya na da kirki. Allah ya ba shi lada."
Na amsa da Ameen. Mun cigaba da Hiran kirkin Sadiq. Kafin Adda ta fito tace Amma ta farka gabdaya muka Dumguma cikin dakin.
Amma ta bude ido tas ta na kallon kowa ta na gane kowa duk wanda ya gaisheta sai ta amsa sannan ta ambaci sunansa.
Ina zuwa kusa da ita na riko hannunta ina Fad'in"Amma kin bani Tsoro na zata tafiya za ki yi ki barni."
Amma ta yi mirmishi cikin muryan ciwo tace"ke ce ki ka ba ni Tsoro, Ba na so ki yi nesa da ni Hasiya."
Kai na gyad'a mata ina fad'in"In sha Allahu ba in da zan je Amma. Ina nan tare da ke sai mutuwa."
Amma na dariyan jin dadi murya a sanyaye tace"Sai aure dai ko Hasiya.?
Sai naji kunya na dukar da kai Inna Talati ke fad'in"In sha Allahu sai aure zai Rabaku."
Gabadaya Murna ta cikani ganin Amma ta samu lafiya.
Cikin muryan ciwo Amma tace"Wa ya kawo ni asibiti?
Muka kalli juna ni da Ramatu kafin ma nayi magana Adda tace"Wani bawan Allah ne Amma. Yanzu ya fita ba da jimawa ba."
Amma ta jinjina kai kafin tace"Allah ya biyasa da Aljannah."
Muka amsa da Ameen Ameen.
Adda Fati na fad'ama zan je gida na Dawo tace ya kamata kan naje na gyara jikina.
Nan na bar Adda Fati da Ramatu tare muka fita da Inna Talatu da su Maman Salihi Inna talatu ta samu abun hawan zuwa sabon gari. Mu kuma muka samu na anguwan mu.
Suna ta min daidaiciyar mgana ko kallonsu ban yi su kan su susan ba su kyauta ba kowa ya yi nagari ai ya sani.
Sai kuma yaji tana fad'in bata san sunan asibitin ba.
Sai ya kalleta nima daidai na juya ina kallomsa sai ya lumshe min ido kafin ya Bude kai Tsaye yace"Ba ni wayar na fad'a mata."
Ba musu na mikamasa baayan na ce ma Adda ga shi za'ayi mata kwantance.
Karban wayan ya yi, bayan ya yi sallama sun gaisa da Adda sannan ya Fad'a mata sunan asibitin sannan suka yi sallama.
Tun bayan gama wayar sai Dakin ya Dauki shuru sai da aka kirasa a waya ya fita ya jima bai dawo ba. Sai ga shi an bude kofa ina juyowa naga Adda Fati kan gaba sai Ramatu sai Inna Talatu sai maman boy da maman Salihi da kaltume.
Ni ba ta su na ke ba mikewa na yi ina musu maraba. Ina jin Maman boy na fadin'Sannu Hasiya."
Takaici yasa ban amsa ba sun san da Sannu ne ina neman taimakon su ba su taimakamin ba.
Duka suna Tsaye gaban gadon Amma na ce ma Adda"Wa ya nuna muku dakin?
Adda Fati tace"da wayar da kika kirani, na kira sai ga shi wani Saurayi ya fito ya shigo damu har nan likita ne?
Sai na girgiza kai kafin nace"Shi ne wanda ya taimakamin aka kawo Amma asibiti. Adda tare muka kwana sai da safe ya tafi dazu nan ya dawo shi ya kashe komai da a ke bukata."
Inna Talatu tace"Allah Sarki Allah ya biyasa."
Su Adda suka amsa da Ameen su Maman boy suka fara daidaiciyar mgana wai ba su ji bugun kofata ba sai daga baya.
Ramatu ko kusa da ni ta dawo ta na fadin"Hasiya kin ci abinci!?
Na gyada kai kafin nace"Ya siyamin waina yanzu kuma ya kawo wad'anan kaya da mgangunan Amma."
Ramatu tace"Angode masa. na zo da abinci fulas ne bamu yi tunanin Daukowa ba."
Adda tace"Sai na koma na Dauko ba matsala."
Inna Talatu ta kalleni tace"ba ta farka ba ne.?
Kai tsaye nace"Ta farka ta sha ruwa ta koma sun ce jininta ne ya yi kasa."
Suka jinjina kai suna mata fatan samun lafiya.
Ba mu ji turo kofarsa ba sai jin sallamarsa muka yi.
Gabadaya mu ka juya muna kallonsa.
*Littafin TSAKA MAI WUYA paid book ne, iya Book 1 ne free Pay N500 For BOOK 2,3. Regular group or VIP GROUP N1000. Via 0552179550 Jamila Umar gt bank.*
*Shedar biya ta wad'anan lambobin 09069067488 or 08032773332.*
*SPECIAL GROUPS Follow@Jamilaumarjanafty On AREWABOOKS mutanen mu na Niger za su Tuntubi Kausar Aglan nissa +22796562223 Nagode*
*Janafty*
*TSAKA MAI WUYA.*
*Wattpad:Jamilaumar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*
https://chat.whatsapp.com/GoRzZ7ZgslV2alO5hYGAnj
*15*
Cikin takun natsuwarsa ya karisa shigowa cikin D'akin.
Yadda muka zuba masa ido ne yasa ya da'n dukar da kansa ya na fad'in"Sannun ku. Ya mai jikin?
Sai suka amsa gabadaya da sauki kafin su shiga gaishe shi ya amsa cikin sakewa Adda da Inna talatu ne suka fara masa godiya.
Kansa na kasa yace"Bakomai.."
Ni ya kallah nima daidai lokacin na Dago ina kallonsa da Sauri nace"Uhm wannan yayata ce Adda Fati. Sauran yan gidanmu ce wannan kuma kawata ce."
Na fad'a ina nuna Masa Ramatu kallonta ya yi lokaci d'aya ya na fadin"Sannun ku zuwa."
Suka amsa masa sai dakin ya dauki Shuru Adda Fati sai ta katse shurun da Fad'in"A nan garin ka ke?
Kai tsaye ya kalleta kafin yace"A'a."
Daga haka bai kara cewa komai ba.
Inna talatu tace"Angode sosai Allah ya saka maka da alheri."
Bai amsa ba kansa na kasa sai dai ya na ta faman mirmishi.
Karisawa ya yi ya duba Amma na d'an lokaci kafin yace min zai tafi.
Adda ta fara jero masa addu'o'i ita da Inna Talatu.
Baya amsawa sai dai yace bakomai kawai ammh da Inna Talatu tace"Allah ya jikan magabata. In iyayenka na raye Allah yasa su gama lafiya. In kuma ba sa raye Allah ya ba su Aljannah."
Ya na gabda zai fita ya juyo cikin mirmishi sannan ya amsa da"Ameen Ameen Nagode."
Daga haka ya fice Ramatu ta zungureni ta na fad'in"Ki raka shi mana"
Kallonta na yi sai ta gyad'a min kai daidai Lokacin da Adda ke kara fad'in"Hasiya bi shi mana. Ki kara masa godiya."
Maman boy da gulma tace"Wlh kuma daga gani asibitin akwai cacan kudi. Tunda ba ta gwamnati ba ne"
Jin haka yasa na bisa da Sauri har ya kai Haraban asibitin ya na tafiya. Sai na kasa kiran sunansa illah sauri sauri da na rika yi har na cimmasa.
Tsayawa ya yi ya na kallona kafin yace" Me yasa ki ka fito?
Kaina na kasa nace"Na zo ne na kara maka godiya."
Mirmishi ya yi kafin yace"Godiyar nan ta isa hakanan HASIYA.."
Kallonsa na yi cikin mamakin kiran sunana da ya yi sai ya ware min ido ya na fad'in"Ko ba sunan ki kenan ba?
Kai na gyad'a masa cikin kunya alamun hakane cikin yar mamaki ya kalleni ya na fad'in"Hasiya sunane? Sunan ba Asiya ba ne?
Kai na girgiza masa kafin nace"Hasiya ne sunan."
Shima cikin girgizamin kai yace"To ko dai sunan Fulani ne?
Kallonsa na yi kai tsaye kamar yadda ya ke kallona. Ya ga mahaifiyarmu da zanen Fulani a gefen bakinta, Da kuma gefe da gefen fuskarta.
Sannan yaga Adda Fati da nace yayata ce itama sai yaga yanayinta kamar na Fulani ko buzaye so ya ke ya tabbatar.
Na rasa me zan ce masa ne yasa nace"Amma ce bafullatana. Baba kuma bazazzagi ne, Sunan Hasiya kuma kanwar Baba ce da ta rasu, sai ya maida min sunanta."
Kai tsaye yace"Kenan ki na jin Fullanci.?
Kai Tsaye nace"ba na ji fa sai abunda ba'a rasa ba."
Mirmishi ya yi kafin yace"Na sha kina ji ne nace ki koyamin. ni ban iya kowani yare ba."
Baki na bude kafin nace"Wlh ni ma ban iya ba."
Yadda na yi saurin rantsewa yasa ya yi mirmishi kafin yace"Ban ce ki rantse ba. Yanzu ammh gida zaki koma ki yi wanka ki huta ko?
Ni ban yi wannan Tunanin ba sai da ya fad'a sai na kara bin kaina da kallo yarkace yarkace kamar yar gudun Hijira.
Sai naji kunya na dukar da kaina ina wasa da gefen zanin Amma da na yi Lullubi da shi.
Shi ko bai damu ba kai tsaye yace"Gaskiya ya kamata ki je gida ki Huta."
Da toh na amsa shi har mun yi sallama akan gobe zai dawo ya kara Duba Amma da jiki. Na juya zan koma cikin asibitin sai ya kawai naji muryansa cikin kaushi ya kira sunana.
"Hasiya.."
Da sauri na juyo ina fad'in"Na'am.."
Ya na daga in da ya ke yace"Ki kwantar da Hankali zata warke kin ji ko?
Sai na gyada masa kai. Mirmishi ya yi ya juya ya fara tafiya sai ga shi na Tsaya har sai da ya bace ma ganina.
Mirmishi na yi acikin raina nace"Daman ma su suna Abubakar suna da kirki da jin kai."
Cikin asibitin na koma na iske duk sun fito waje Adda Fati ne ke tare da Amma aciki sai na karisa kusa da Ramatu na zauna muka kara gaisawa.
Nura na tambaya tace min da Safen nan ya wuce na gyada kai ina masa Fatan isa lafiya.
Noor ta ke ba ma Nono sai da ta gama na karbeta ina yi mata wasa. kallona ta yi kafin tace"Ya jikin ki ke ma?
Kai tsaye nace"Ni ai na warware."
Da sauri tace"Sai kumburin Fusakarki bai sabe ba."
A hankali nace"Zai washe shima."
Ramatu tace"Ki ci abinci ga shi nan na Fito miki da shi."
Na amsa mata da toh.
Tazo da filet da cokali sai na Dibi abincin naci Faten wake ne da kifi kadan ma naci saboda cikina ba ya min dad'i.
Ramatu tace"Yakamata ki je gida ki yi wanka ki sauya kayan jikin ki."
Kai Tsaye nace"Shima haka ya ce."
Ramatu tace"Shi wa?
Cikin sigar mamaki. Mirmishi na yi kafin nace
"ABUBAKAR SADIQ.."
daga kasan raina na fad'i sunan saboda Muhimmanci da sunan ke da shi a Rayuwata.
Ramatu tace"Au Abubakar Sadiq sunansa? Ma sha Allah wai a ina kuka had'u?
Kallonta na yi kafin na fara bata labarin hadu'warmu na karishe da fad'in"Saboda Rudewa haka na zo asibitin nan ba takalmi. Bawan Allah nan takalminsa ya bani na saka sai da ya fita ya siyomin wannan sannan ya karb'i na shi. Ramatu gaskiya ya na da kirki tare da abokinshi suka kwana a asibitin nan da Amma fa."
Ramatu tace"Gaskiya ya na da kirki. Allah ya ba shi lada."
Na amsa da Ameen. Mun cigaba da Hiran kirkin Sadiq. Kafin Adda ta fito tace Amma ta farka gabdaya muka Dumguma cikin dakin.
Amma ta bude ido tas ta na kallon kowa ta na gane kowa duk wanda ya gaisheta sai ta amsa sannan ta ambaci sunansa.
Ina zuwa kusa da ita na riko hannunta ina Fad'in"Amma kin bani Tsoro na zata tafiya za ki yi ki barni."
Amma ta yi mirmishi cikin muryan ciwo tace"ke ce ki ka ba ni Tsoro, Ba na so ki yi nesa da ni Hasiya."
Kai na gyad'a mata ina fad'in"In sha Allahu ba in da zan je Amma. Ina nan tare da ke sai mutuwa."
Amma na dariyan jin dadi murya a sanyaye tace"Sai aure dai ko Hasiya.?
Sai naji kunya na dukar da kai Inna Talati ke fad'in"In sha Allahu sai aure zai Rabaku."
Gabadaya Murna ta cikani ganin Amma ta samu lafiya.
Cikin muryan ciwo Amma tace"Wa ya kawo ni asibiti?
Muka kalli juna ni da Ramatu kafin ma nayi magana Adda tace"Wani bawan Allah ne Amma. Yanzu ya fita ba da jimawa ba."
Amma ta jinjina kai kafin tace"Allah ya biyasa da Aljannah."
Muka amsa da Ameen Ameen.
Adda Fati na fad'ama zan je gida na Dawo tace ya kamata kan naje na gyara jikina.
Nan na bar Adda Fati da Ramatu tare muka fita da Inna Talatu da su Maman Salihi Inna talatu ta samu abun hawan zuwa sabon gari. Mu kuma muka samu na anguwan mu.
Suna ta min daidaiciyar mgana ko kallonsu ban yi su kan su susan ba su kyauta ba kowa ya yi nagari ai ya sani.