Sashe 57
Tsaka Mai Wuya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ban san ya zo kusa da ni ba sai da naji ya na fad'in"Wutar ta ki kamawa ne?
Da sauri na juyo ina kallonsa.
Ya na tsaye a gefena sanye da riga da wando masu ruwan toka rigar ta na da Layi layi sannan tare da dogon hannu na Fahimci ya na son saka riguna masu Dogon hannu.
Sannan Dabi'arsa ne ya na tsaye ya tura Hannayensa cikin Aljihun wandonsa.
Yau ma haka d'in ya yi sai naga ya yi min kyau. Haka daman masu suna Abubakar su ke da gayu da kyau tare da Tsari?
Shagalar da na yi ina kallonsa yasa har ya Durkusa a gabana ban sani ba sai ji kawai na yi ya na fad'in"Kawo na tayaki fifita wutar."
Da sauri na dawo Hayyacina da Sauri na tashi ina kallon bayana ganin matan gidanmu a tsakar gida an zuba mana ta mujiya musamman ma Kaltume.
Da sauri nace"Don Allah ka bar shi. Kayan ka za su yi hayaki?
Ya na kallona yace"kin tabbata zaki iya hura wutar?
Da sauri na gyad'a masa. Shiyasa ya mike ya na fadin"Bari na tafi"
Ban san bakina ya kubce ba sai da na jini ina fad'in"Tun yanzu?
Agogon Fatan da ke hannunsa ya kai ma Duba kafin yace"Mangariba ta kusa ne"
Jinjina kai na yi kafin na yi mgana ya rigani da fad"in"Zo mana Hasiya."
Ba musu na amsa masa.
Daki na koma na dauki Hijabina ina ce ma Amma Abubakar na kirana a waje ta amsamin ta hanyar d'aga kanta sama.
Ina fitowata matan gidanmu suka sakarmin na mujiya
Har na fice suna kallona na kuma san ina fita za'a dasa yi dani.
A kofar gidan na ganshi ya jingina da garu ya na kallon hanya.
Ina fitowa ya tashi daga jingina da ya yi da garu ya na kallona.
Kallo ba Dabi'an sa ba ne ammh sai ya samu kansa da karemin kallo, Fuskata ta kara masa Fayau saboda jan Hijabi ne ajikina in ba sanin fatata ka yi ba sai kayi Tunanin ba ni da jini ne saboda yadda Fata ta dashe fari sol ba alamun ja ja a jikina.
Ni kuma sai na Tsargu da yanayin kallon na shi. Barin ma da mutane ke ta wucewa suna kallon mu har da ma su waiwayowa suna cin Tuntube saboda Gulma.
Shi kuma kallona ya ke yi ammh kuma Tunaninsa ya tafi ga Tunanin sunan da Tahir ke kirana wato Zabiya kuma sai yaga gaskiyan shi kad'an ne ya ragemin ban zama Zabiyar ba.
Ko Amma fara ce Ammh ba kalan fari na ba ne Habiba ma haka kalan haskenta mai ja ne ba irin na wa ba ya na da tabbacin duk da bai ga sauran yan'uwana duka ba kalan Fatata ta fita Dabam da na su.
Gyara murya na yi dalilin da ya sa ya sauke kallonsa a kaina lokaci d'aya ya na fad'in"Hasiya mai d'anwake "
Ya fad'a cikin Zolaya. ni ma kai tsaye Nace"Habu mai siyan Danwake ba."
Dariya ya yi ya na girgiza kai kafin yace"Sunan ki Asiya ne ba Hasiya ba.'
Kai tsaye nace"Na fad'a maka ni sunana Hasiya ba Asiya ba ce."
Kai ya jinjina kafin yace"Daman an ce bafullatani da kafiyar tsiya."
Baki na tabe kafin nace"Da Amma ka ke ni bazazzagiya ce tunda Babanmu mu haifaffan garin zariya ne."
Shima kai tsayen yace"Ammh kin yarda ke Ruwa biyu ce Hausa Fulani. Wani ma in ba kin fad'a masa ba kin fi kama da buzayen yamai."
Cikin mamaki nace"Ina ne kuma Yamai.?
Ya na Bude ido yace"Baki san yamai ba?
Na gyad'a masa kai. Kai tsaye yace"Ke bakauya ce a she ban sani ba."
Ina yar Dariya nace"Kuma bak'auya ta had'u da bak'auye ba."
Baki ya rike ya na fad'in"Hasiya ashe haka ki ka ji Hausa ban sani ba.?
Ban ce masa komai ba sai dai na Murmusa.
Shuru ya yi na wani lokaci kafin yace"Bari na zo na tafi. An fara kiran sallah."
Ina dagowa nace"Kwana biyu ba ka zo ba? Ba tare da ya ba ma mganar Muhimmamci ba yace"Eh na yi tafiya ne."
Iduwana na kallonsa nace"Garin ku ka je?
Wannan karon da kai ya amsamin kafin ya yi mgana da sauri na tare shi da cewa"Gobe za ka zo?
Cikin mamaki ya kalleni sai na ji kunya da nauyi da sauri na gyara maganata da fad'in"Amma ce ke damuwa in baka zo ba."
Mirmishimsa mai Tsada ya saki kafin yace"Ko ban zo ba. zan aiko a siyamin Danwake."
Cikin marairaicewa nace"Don Allah kada ka aiko da kud'i"
Kai tsaye yace"Nima don Allah ba na son gaddama."
Ganin yadda ya yi mganar yasa ban kara cewa komai ba.
Sallama mu ka yi ya wuce ni koma na koma cikin gida ina shiga Maman Boy ta washe baki ta na fad'in"Ai na jiki shuru nace Hira ta yi dad'i. naga rushun ya ruru sai na aza miki Ruwan."
Ban sakar mata Fuska ba nace Nagode. na shige dakin Amma ina kallonsu suna had'a ido da Maman Salihi za'ayi gulma.
Acikin raina nace"Tunanin abunda bazai taba faruwa ba ku ke yi."
Ko da Allah ya ce zai Farun Hasiya?
******
Bai koma Daki ba sai da ya tsaya masallaci ya yi sallar mangariba ana wa'azi da Fadakarwa kan mutuwa yasa ya zauna har aka kira Isha'i.
Sai da sallar isha'in sannan Tahir ya zo bayan an idar da salla suka koma Daki tare.
Bai masa mganar ba sai da suka yi shirin kwanciya. Tahir wayarsa na Hannunsa shi kuma Sadiq Laptop dinsa ya jawo bai ma kai ga kunna ta ba yaji Tahir na fad'in"Wai dazu ina ka je.?
Ba tare da ya kallesa ba yace"Gidan su Hasiya na je."
Tahir takaici ya sa ka shi ijiye wayarsa duk ko abunda zai sa Tahir sauke waya lalle muhimmancin al'amarin ya girmama.
Sadiq bai ma san ya na yi ba kokarin Sarrafa Na'urar hannunsa kawai ya ke yi Lokacin da yaji Tahir na Fad'in"Sadiq ko dai ka fara son Zabiyar yarinyar nan da gaske ne?
Ba tare da ya bama tambayan Tahir Muhimmanci ba yace"So kuma? Ka cika maimaita mgana D'aya ina ce mun rufe wannan mganar da kai ko Tahir?
Tahir ya katseshi da Fad'in"To in baka so nayi zargin haka ka rabu da su mana. Yan'uwan ka ne da dole sai ka rika zuwa in da su ke? Ina ce daga Taimako ba shikenan ba?
Sadiq ya yi shuru kamar bazai yi mgana ba sai kuma chan yace" Tahir na fad'a maka Tausayin su na ke ji. Kuma ni wajen mahaifiyar su na ke zuwa matar na so na wlh."
Tahir ya yi wata Dariyar renin wayau kafin yace"Ta na sonka? Eh dole ta soka Tunda ta na son kaima ta jefa rayuwarka cikin gagari ta sanadin yarta kamar yadda ta jefa Sauran."
Sadiq bai Fahimci in da Tahir ya dosa ba shiyasa ya ce"Naji ka bar ni. Rayuwata ce ba taka ba Tahir."
Tahir yace"Kasan me naji a kan wannan yarinyar da Ahalinta?
Sadiq kai tsaye yace"Sai ka fad'a."
Ya fad'a hankalinsa na kan Allon Na'urar da ya ke kallo.
Tahir yace"ka na fita wani Mutum ya zo can u just imaging yarinyar da ka ke ma kallon yarinya karama auranta fa Biyu bazawara ce."
Sadiq ya yi shuru kafin ya Dago ya na kallon Tahir cikin mamaki yace"Me ka ce? Bazawara ?
Tahir yace"Yes ofCourse Bizet ba. Abunda zai kara baka mamaki ma shine Bayan mganar auran nata yarinyar ta na da wani abu a tare da ita na Dabam kuma"
Sadiq ya yi saurin cewa"Kamar na me?
Nan Tahir ya shiga zayyanemasa har da kari ya karishe da fad'in"An ce duk arzikin mutum in ya rabeta sai ya talauce in ma bai rasa rai ba. Mijinta na farko da shi da iyayensa sai da suka rasa komai nasu, na Biyun kuma ya na chan ya na jinya.
To wai yarinyar da ace itace silar karyan arzikin Ubanta ta yi kuma sanadiyar mutuwarsa da ciwon uwarta da duka Halin da suke ciki itace Sila kasan wasu haka Allah ke yin su da Farar kafa ba bu albarka ko wani nasibi a tare da su."
Tahir ya tsagaita ya na kallon Sadiq ya na so ya Fahimci yadda ya karb'i mganar sai yaga hankalinsa na kan abunda ya ke kamar ma bai ji abunda ya ke fad'i ba.
Kai tsaye Tahir yace"Baka ce komai ba?
Sadiq kai tsaye yace"Me zan ce maka Tahir?
Cikin mamaki ya ce"Baka ji mganata ba ne?
Sadiq yace"Na ji mana. Me ka ke so ayi yanzu?
Tahir ya gyara zama ya na fad'in"Ka yi nesa da su don Allah Sadiq. Ka na da wad'anda in wani abu ya sameka za su shiga wani Hali."
Sadiq ya yi kamar bai ji Tahir ba sai da shi ya gaji da jiran jin ta bakinsa ya kwace laptop d'in ya na fadin"Sadiq mgana fa mai muhimman na ke yi maka ka yi min banza"
Sadiq ya sauke ajiyar zuciya kafin ya ce"Tahir me ka ke so nace.?
Tahir yace"Au me ma zaka ce ka ke tambaya ta Sadiq?
Lafiyar ka Dukiyarka ka tseratar da su mana."
Sadiq ya goya hannayensa a saman kirjinsa lokaci d'aya ya na fad'in"To naga ai ni ba mai dukiya ba ne ballatana ace zan talauce."
Ya fad'a lokaci daya ya na kyalkyacewa da Dariya.
Da sauri na juyo ina kallonsa.
Ya na tsaye a gefena sanye da riga da wando masu ruwan toka rigar ta na da Layi layi sannan tare da dogon hannu na Fahimci ya na son saka riguna masu Dogon hannu.
Sannan Dabi'arsa ne ya na tsaye ya tura Hannayensa cikin Aljihun wandonsa.
Yau ma haka d'in ya yi sai naga ya yi min kyau. Haka daman masu suna Abubakar su ke da gayu da kyau tare da Tsari?
Shagalar da na yi ina kallonsa yasa har ya Durkusa a gabana ban sani ba sai ji kawai na yi ya na fad'in"Kawo na tayaki fifita wutar."
Da sauri na dawo Hayyacina da Sauri na tashi ina kallon bayana ganin matan gidanmu a tsakar gida an zuba mana ta mujiya musamman ma Kaltume.
Da sauri nace"Don Allah ka bar shi. Kayan ka za su yi hayaki?
Ya na kallona yace"kin tabbata zaki iya hura wutar?
Da sauri na gyad'a masa. Shiyasa ya mike ya na fadin"Bari na tafi"
Ban san bakina ya kubce ba sai da na jini ina fad'in"Tun yanzu?
Agogon Fatan da ke hannunsa ya kai ma Duba kafin yace"Mangariba ta kusa ne"
Jinjina kai na yi kafin na yi mgana ya rigani da fad"in"Zo mana Hasiya."
Ba musu na amsa masa.
Daki na koma na dauki Hijabina ina ce ma Amma Abubakar na kirana a waje ta amsamin ta hanyar d'aga kanta sama.
Ina fitowata matan gidanmu suka sakarmin na mujiya
Har na fice suna kallona na kuma san ina fita za'a dasa yi dani.
A kofar gidan na ganshi ya jingina da garu ya na kallon hanya.
Ina fitowa ya tashi daga jingina da ya yi da garu ya na kallona.
Kallo ba Dabi'an sa ba ne ammh sai ya samu kansa da karemin kallo, Fuskata ta kara masa Fayau saboda jan Hijabi ne ajikina in ba sanin fatata ka yi ba sai kayi Tunanin ba ni da jini ne saboda yadda Fata ta dashe fari sol ba alamun ja ja a jikina.
Ni kuma sai na Tsargu da yanayin kallon na shi. Barin ma da mutane ke ta wucewa suna kallon mu har da ma su waiwayowa suna cin Tuntube saboda Gulma.
Shi kuma kallona ya ke yi ammh kuma Tunaninsa ya tafi ga Tunanin sunan da Tahir ke kirana wato Zabiya kuma sai yaga gaskiyan shi kad'an ne ya ragemin ban zama Zabiyar ba.
Ko Amma fara ce Ammh ba kalan fari na ba ne Habiba ma haka kalan haskenta mai ja ne ba irin na wa ba ya na da tabbacin duk da bai ga sauran yan'uwana duka ba kalan Fatata ta fita Dabam da na su.
Gyara murya na yi dalilin da ya sa ya sauke kallonsa a kaina lokaci d'aya ya na fad'in"Hasiya mai d'anwake "
Ya fad'a cikin Zolaya. ni ma kai tsaye Nace"Habu mai siyan Danwake ba."
Dariya ya yi ya na girgiza kai kafin yace"Sunan ki Asiya ne ba Hasiya ba.'
Kai tsaye nace"Na fad'a maka ni sunana Hasiya ba Asiya ba ce."
Kai ya jinjina kafin yace"Daman an ce bafullatani da kafiyar tsiya."
Baki na tabe kafin nace"Da Amma ka ke ni bazazzagiya ce tunda Babanmu mu haifaffan garin zariya ne."
Shima kai tsayen yace"Ammh kin yarda ke Ruwa biyu ce Hausa Fulani. Wani ma in ba kin fad'a masa ba kin fi kama da buzayen yamai."
Cikin mamaki nace"Ina ne kuma Yamai.?
Ya na Bude ido yace"Baki san yamai ba?
Na gyad'a masa kai. Kai tsaye yace"Ke bakauya ce a she ban sani ba."
Ina yar Dariya nace"Kuma bak'auya ta had'u da bak'auye ba."
Baki ya rike ya na fad'in"Hasiya ashe haka ki ka ji Hausa ban sani ba.?
Ban ce masa komai ba sai dai na Murmusa.
Shuru ya yi na wani lokaci kafin yace"Bari na zo na tafi. An fara kiran sallah."
Ina dagowa nace"Kwana biyu ba ka zo ba? Ba tare da ya ba ma mganar Muhimmamci ba yace"Eh na yi tafiya ne."
Iduwana na kallonsa nace"Garin ku ka je?
Wannan karon da kai ya amsamin kafin ya yi mgana da sauri na tare shi da cewa"Gobe za ka zo?
Cikin mamaki ya kalleni sai na ji kunya da nauyi da sauri na gyara maganata da fad'in"Amma ce ke damuwa in baka zo ba."
Mirmishimsa mai Tsada ya saki kafin yace"Ko ban zo ba. zan aiko a siyamin Danwake."
Cikin marairaicewa nace"Don Allah kada ka aiko da kud'i"
Kai tsaye yace"Nima don Allah ba na son gaddama."
Ganin yadda ya yi mganar yasa ban kara cewa komai ba.
Sallama mu ka yi ya wuce ni koma na koma cikin gida ina shiga Maman Boy ta washe baki ta na fad'in"Ai na jiki shuru nace Hira ta yi dad'i. naga rushun ya ruru sai na aza miki Ruwan."
Ban sakar mata Fuska ba nace Nagode. na shige dakin Amma ina kallonsu suna had'a ido da Maman Salihi za'ayi gulma.
Acikin raina nace"Tunanin abunda bazai taba faruwa ba ku ke yi."
Ko da Allah ya ce zai Farun Hasiya?
******
Bai koma Daki ba sai da ya tsaya masallaci ya yi sallar mangariba ana wa'azi da Fadakarwa kan mutuwa yasa ya zauna har aka kira Isha'i.
Sai da sallar isha'in sannan Tahir ya zo bayan an idar da salla suka koma Daki tare.
Bai masa mganar ba sai da suka yi shirin kwanciya. Tahir wayarsa na Hannunsa shi kuma Sadiq Laptop dinsa ya jawo bai ma kai ga kunna ta ba yaji Tahir na fad'in"Wai dazu ina ka je.?
Ba tare da ya kallesa ba yace"Gidan su Hasiya na je."
Tahir takaici ya sa ka shi ijiye wayarsa duk ko abunda zai sa Tahir sauke waya lalle muhimmancin al'amarin ya girmama.
Sadiq bai ma san ya na yi ba kokarin Sarrafa Na'urar hannunsa kawai ya ke yi Lokacin da yaji Tahir na Fad'in"Sadiq ko dai ka fara son Zabiyar yarinyar nan da gaske ne?
Ba tare da ya bama tambayan Tahir Muhimmanci ba yace"So kuma? Ka cika maimaita mgana D'aya ina ce mun rufe wannan mganar da kai ko Tahir?
Tahir ya katseshi da Fad'in"To in baka so nayi zargin haka ka rabu da su mana. Yan'uwan ka ne da dole sai ka rika zuwa in da su ke? Ina ce daga Taimako ba shikenan ba?
Sadiq ya yi shuru kamar bazai yi mgana ba sai kuma chan yace" Tahir na fad'a maka Tausayin su na ke ji. Kuma ni wajen mahaifiyar su na ke zuwa matar na so na wlh."
Tahir ya yi wata Dariyar renin wayau kafin yace"Ta na sonka? Eh dole ta soka Tunda ta na son kaima ta jefa rayuwarka cikin gagari ta sanadin yarta kamar yadda ta jefa Sauran."
Sadiq bai Fahimci in da Tahir ya dosa ba shiyasa ya ce"Naji ka bar ni. Rayuwata ce ba taka ba Tahir."
Tahir yace"Kasan me naji a kan wannan yarinyar da Ahalinta?
Sadiq kai tsaye yace"Sai ka fad'a."
Ya fad'a hankalinsa na kan Allon Na'urar da ya ke kallo.
Tahir yace"ka na fita wani Mutum ya zo can u just imaging yarinyar da ka ke ma kallon yarinya karama auranta fa Biyu bazawara ce."
Sadiq ya yi shuru kafin ya Dago ya na kallon Tahir cikin mamaki yace"Me ka ce? Bazawara ?
Tahir yace"Yes ofCourse Bizet ba. Abunda zai kara baka mamaki ma shine Bayan mganar auran nata yarinyar ta na da wani abu a tare da ita na Dabam kuma"
Sadiq ya yi saurin cewa"Kamar na me?
Nan Tahir ya shiga zayyanemasa har da kari ya karishe da fad'in"An ce duk arzikin mutum in ya rabeta sai ya talauce in ma bai rasa rai ba. Mijinta na farko da shi da iyayensa sai da suka rasa komai nasu, na Biyun kuma ya na chan ya na jinya.
To wai yarinyar da ace itace silar karyan arzikin Ubanta ta yi kuma sanadiyar mutuwarsa da ciwon uwarta da duka Halin da suke ciki itace Sila kasan wasu haka Allah ke yin su da Farar kafa ba bu albarka ko wani nasibi a tare da su."
Tahir ya tsagaita ya na kallon Sadiq ya na so ya Fahimci yadda ya karb'i mganar sai yaga hankalinsa na kan abunda ya ke kamar ma bai ji abunda ya ke fad'i ba.
Kai tsaye Tahir yace"Baka ce komai ba?
Sadiq kai tsaye yace"Me zan ce maka Tahir?
Cikin mamaki ya ce"Baka ji mganata ba ne?
Sadiq yace"Na ji mana. Me ka ke so ayi yanzu?
Tahir ya gyara zama ya na fad'in"Ka yi nesa da su don Allah Sadiq. Ka na da wad'anda in wani abu ya sameka za su shiga wani Hali."
Sadiq ya yi kamar bai ji Tahir ba sai da shi ya gaji da jiran jin ta bakinsa ya kwace laptop d'in ya na fadin"Sadiq mgana fa mai muhimman na ke yi maka ka yi min banza"
Sadiq ya sauke ajiyar zuciya kafin ya ce"Tahir me ka ke so nace.?
Tahir yace"Au me ma zaka ce ka ke tambaya ta Sadiq?
Lafiyar ka Dukiyarka ka tseratar da su mana."
Sadiq ya goya hannayensa a saman kirjinsa lokaci d'aya ya na fad'in"To naga ai ni ba mai dukiya ba ne ballatana ace zan talauce."
Ya fad'a lokaci daya ya na kyalkyacewa da Dariya.