← Book details Shu'umin Namiji Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 67 OF 112

Sashe 67

Shu'umin Namiji Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Zahrah kuwa yau  da wani irin irin matsanancin ciwon kai ta tashi,  gaba ɗaya  idanunta sunyi luhu luhu dasu,  da gani kai kasan cewa kuka tasha ta ƙoshi. 
Yau ya kasance  aurenta da Dr.Sadeeq saura kwanaki shida kenan tana ƙirgawa kuma acikin kwanakin nan ne zasu fara gudanar da shirye shiryen da suka tsara,, gaba ɗaya ji takeyi bata marmarin auren, sannan kuma ji takeyi komai yafice mata arai, bawai kuma don batason Dr.Sadeeq ɗin ba, tun shekaran jiya Dr.Sadeeq yakawo mata ɗinkunanta da kuma kayan da zata sanya a kamu da wajen diner, amma kuma ko duba kayan batayi ba balle taga ma ko sunyi mata ko basuyi mata ba, batasan meyake damunta ba, amma tabbas tasan akwai wani baƙon al'amari dayake ta kusanto rayuwarta aduk kwanan duniya.     Yau hakanan tatashi taji ko gyaran jikin ma batason zuwa, amma kuma dazaran tace bazata jeba  tasan Inna zata sanyata agaba da yawan tambayoyi, don haka ma gwamma kawai ta je ɗin zaifiye mata...    Sauri sauri haka ta shirya tafito, saboda  tasan cewa yanzu haka Samad na ƙofar gida yana jiranta... ai kuwa tana fitowa taga motar Dr.Sadeeq fake a ƙofar gidan nasu, murmushi kawai tayi haɗe da ƙarasawa wajen motar...  "Allah sarki Samad yana da haƙurin jira, da Dr.Sadeeq ne da yanzun ya ƙirata a waya" tafaɗi haka a zuciyarta dai dai sanda taƙaraso gaf da motar, buɗe murfin motar tayi tashiga bakinta ɗauke da sallama,  "Kayi haƙuri Samad nabarka kana ta jira"  tafaɗi haka tana me ƙoƙarin rufe murfin motar, batare da takalli Inda Samad ɗin ke zaune ba.
Tana rufe murfin motar   tadawo da kallonta wajen zaman driver  fuskarta ɗauke da murmushi,,   a maimakon taga Samad saitaga Dr.Sadeeq, mamakine ya bayyana akan fuskarta alokaci guda, sake ware idanu tayi tana kallonsa, da'alama dai ganinsa yabata mamaki sosai...

 Murmushinsa me kyau yayi mata haɗe da kafeta da idanunsa wanda suke sauƙar mata da wani irin yanayi na kasala ajikinta..      Itama murmushin tayi masa haɗe da shagwaɓe fuska....
"Ni dai nayi fushi!"  tafaɗi haka a shagwaɓe...     

"Tuba nake"

Dr.Sadeeq yafaɗi haka yana me kama kunnuwansa da duka hannayensa..   alaman ban haƙuri.

  "Ni dai naƙi wayon"  tafaɗi haka  tana me kaɗa idanunta..     Murmushi yayimata haɗe da kamo duka hannayenta yasanya acikin nasa hanun,  lumshe idanunsa yayi alokaci guda haɗe da buɗewa

"Nayi kewarki sosai Zahrah na!" yafaɗi haka cikin wata murya me sanyi. 
Ɗan guntun murmushi tayi haɗe da soma ƙoƙarin janye hanunta  daga cikin nasa  hanun, amma kuma  bata samu daman hakan ba.    "Meyasa jiya kika ƙi ɗaga wayana?"  yatambayeta cike da kulawa bayan yagama karantar yanayin da take ciki.     Sai alokacin ne ma Zahrah ta tuno da cewa jiya taga  missed calls ɗinsa, sanann kuma bata bi bayaba,, ƙaƙalo murmushi tayi haɗe da cewa " Kayi haƙuri nayi bacci ne alokacin" 

Kansa ya jinjina badon wai ya gamsu da abun da ta faɗa ba,, ta da motar yayi suka hau kan titi.    Saida sukayi nisa a tafiyar kafun yadawo da kallonsa gareta, sosai tayimasa kyau komai nata ya canja, sai dai kuma kallo ɗaya yayimawa fuskarta yafuskanci cewa tayi kuka,  dafari yaso tambayarta meke damunta, amma kuma sai kawai ya share,,, sama sama yake janta da hira harsuka iso gidan Hajiya Shuwa... Yana ganin shigewarta cikin gidan ya sauƙe ajiyar zuciya ƴaɗe da kifa kansa akan steering motar,    "meke damun Zahrah ne?"   ya yiwa kansa tambayar a bayyane, amma sai dai kuma bayida amsar da zai bawa kansa....    A jiyar zuciya yakuma sauƙewa akaro na barkatai, zuciyarsa cike da tunani kala kala yaja motarsa yabar ƙofar gidan....... Ɓangaren Zahrah kuwa kwana biyun nan wasu irin magunguna masu ƙarfin gaske Hajiya Shuwa take bata tanasha, hakan kuwa shike taimakawa wajen hautsina mata tunaninta, wani irin abu takeji acikin jikinta  wanda kai tsaye za'a iya ƙiransa da suna sha'awa,  ko da yaushe yanzu Zahrah cikin jin feelings take, hattakai ta kawo yanzu alwala  ma baya daɗewa ajikinta yake karyewa  saboda sosai sperm ke fita ajikinta, duk kuma ɗaya daga cikin aikin magungunan ƙarin ni'iman da Hajiya Shuwa ke bata ne, lallai ita kanta tasan cewa Hajiya Shuwa tayi mata babban haɗi me matuƙar kyau...... (su Doctor za'asha nice😜🙈)

Tunda bacci ya ɗaukeshi da asuba bashi yafarka ba sai ƙarfe 9:30 am, da wani irin zazzafan zazzaɓi yatashi, wanda ya zamana ko ɗaga kansa ba ya'iyawa  hatta numfashima da ƙyar yake iya fitarwa. Yana a wannan halin  ne yaji anturo ƙofar ɗakin nasa, bai iya ɗago kansa ya dubi ko waye ba amma kuma duk da haka ya gane waye ne yashigo cikin ɗakin...   Dasauri Alhj Ma'aruf   yaƙaraso garesa...

"Lafiya Zaid meke damunka?" Alhaji Ma'aruf yafaɗi haka yana me kai hanunsa jikin Zaid, da sauri yajanye hanunsa daga jikin Zaid ɗin domin kuwa jiyayi jikin Zaid ɗin yaɗau zafi rau kamar wuta.   "Subahanallah, bana ƙira Doctor yanzu" Dad yafaɗi haka yana me ƙoƙarin ciro wayarsa daga cikin aljihu,,   bugu biyu Dr.Bilal yaɗauki wayar, cike da damuwa Dad yace yanason ganinsa jikin Zaid ne yatashi. take Dr.Bilal yace gashinan zuwa.. 
Zama Dad yayi jigum agefen gadon Zaid ɗin,  gaba ɗaya yarasa mekeyi masa daɗi, sosai matuƙa cutar Zaid ke damunsa, yana matuƙar ƙaunar Zaid sam bayaso wani abu ya samesa, musamman ma yanzu da Dr.Bilal yashaida masa cewa Zaid ɗin yana ɗauke da ciwon zuciya me tsanani... Mintuna kaɗan Dr.Bilal yaƙaraso gidan, babu wani ɓata lokaci kuwa yashiga yiwa Zaid wasu ƴan gwaje gwaje,  drip  yaɗaura masa bayan yayi masa wasu allurai guda biyu wanda zasu taimaka wajen kawar da zazzaɓi da kuma ciwon da kansa keyi masa uwa uba kuma su sanyasa bacci,  saboda idan yana a cikin hayyacinsa bazai taɓa barin zuciyarsa ta huta ba, yin hakan kuma shike ƙara sawa ciwon yayi tsanani...    Bayan sun fito compound ɗin gidan ne Dr.Bilal yagyara tsayuwarsa haɗe da  duban Alhaji ma'aruf,, bayani  yashiga yimawa Alhaji Ma'aruf ɗin sosai agame da ciwon Zaid ɗin.   Bayan sun kammala maganan ne Alhj Ma'aruf yakoma wajen Zaid da tuni wani baccin wahala yasake ɗaukansa......

*****

Rana bata ƙarya, ranar yau takasance laraba kuma yautake kamun Amarya, tun da safe gidan su Zahrah yake acike ƴan uwan Inna sun tattaro ƙwansu da ƙwarƙwatansu sun garzayo, don haka tuni gida yaɗauki hargowa da hayaniyan mutane yayinda amarya kuwa tunsafe take ƙunshe a ɗaki acewarta cikinta ne keyi mata ciwo,, Husnah da Suhaima ne suka taimaka wajen ɗebe mata kewa ta hanyar zama da'ita.....

Ƙarfe uku na yammaci kenan amma tuni gidansu Zahrah ya ɗinke da mutane, ciki kuwa hadda ƴan matan school ɗinsu  wanda Husnah ce ta gayyacesu, domin ita dai Zahrah bata da wasu ƙawaye Husnah ce kaɗai ƙawarta...  Kowacce ka kalla acikin ƴan matan nan  tasha kyau cikin kayan anko ɗinta.    Husnah ce tsaye akan Zahrah tana ta faman ɓaɓatu akan cewa Zahrah'n ta tashi su tafi shagon meckup domin tuni Dr.Sadeeq yaturo freinds ɗinsa waƴanda zasu kaisu shagon yin meckup ɗin suna ma jiransu aƙofar gida,,  ita dai Zahrah yau jitayi gaba ɗaya bakinta ya mutu sambatajin wani kuzari ajikinta.  Kayan da zata sanya da duk wani abun da zatayi amfani dashi, Husnah ta ɗaukar mata haɗe da kama hanunta suka fice daga cikin gidan.  Wasu haɗaɗɗun motoci suka shiga  kai tsaye aka wuce dasu wani shahararren shagon meckup....    

Kwalliya sosai shahararriyar meyin meckup ɗinnan ta tsantsarawa Zahrah akan fuskarta lokaci ɗaya saiga Zahrah ta sauya kamanni asalin kyawunta yasake bayyana tamkar wata balarabiya ita kanta Zahrah saida tayi mamakin ganin kanta, tabbas dabadan tasan ita ɗin ceba, to da sai tace sanja mata fuska akayi,    kowa yaga kwalliyanta saiyayi santi saboda tasha kyau iya kyau..    Wani doguwar rigan leshi me kyau da tsada ta sanya ajikinta, take  kyakkyawar surar jikinta ya bayyana kansa acikin kayan,  sosai ɗinkin yayi kyau yakuma amshi jikinta,  zama tayi aka tsantsara mata  haɗaɗɗen ɗaurin ɗankwali akanta, yayinda  aka nannaɗe mata dogon gashinta atsakiyar kanta, ita dai tsayawa tayi kamar wata statue tana mamakin irin baiwar kyawun da Allah yayi mata,   daga riganta har zuwa kan takalminta dakuma ɗan karamin fos ɗin dake rike ahanunta kalarsu yakasance light peach ne, yayinda stones ɗin kayanta suka kasance farare,   lokacin da su Husnah sukayi tozali da Zahrah ihu dakuma shewa suka sanya haɗe da tsantsar mamakin irin kyawun da Zahrah tayi, kowa dai yasan Zahrah kyakkyawace amma kuma basuyi tunanin kyawunnata har ya kai hakaba, lallai duk namijin daya samu Zahrah amatsayin mata yayi babban gamdakatar. Take su Husnah suka shiga ɗaukarta hotuna da kuma vedios suna watsawa a instagram dakuma whatsapp, suna cikin buga selfie abokan ango suka ƙaraso don ɗaukar ƙawayen amarya,, duka ƴan matan kowacce da motar da tashiga, yayinda aka bar Zahrah da Husnah sukaɗai saboda Ango yace shi dakansa  zaizo yaɗauki amaryarsa...   Ƙawaye basu jima da tafiya ba wayar Husnah tasoma ƙara,, murmushi tayi haɗe da kallon Zahrah adai dai lokacin da taɗaga wayar takara akan kunenta,    "To ranka shi daɗe gamunan fitowa" abun da Husnah tafaɗa kenan haɗe da miƙewa tsaye hannuwan Zahrah takamo haɗe da miƙar da'ita tsaye..
"Angonki yaƙaraso yace nafito masa dake"  murmushi kawai Zahrah tasakar mawa Husnah kana ta sunkuyar da kanta ƙasa.. A hankali Zahrah ke takawa yayinda rigar jikinta kejan ƙasa, babu abun dake tashi ajikinta sai daddaɗan ƙamshin turare,,  gaskiya Zahrah tayi kyau sosai ayau ɗin..
Chapter 67 · 0% Book details