Sashe 44
Shu'umin Namiji Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wani irin bugawa taji zuciyarta tayi, sakamakon jin abun da Dr Sadeeq yace. Wani irin yanayi ta tsinci kanta ciki, wanda baza'a ƙirasa da farinciki ba, ba kuma za'a ƙirasa da yanayin baƙin ciki ba.
"Zahrah na!" yaƙira sunanta jin cewa tayi shiru batace dashi komai ba.
"Umm" ta'amsa masa a kasalance.
"Naji kinyi shiru, ko dai bakiyi farinciki da hakan bane?"
Yajefo mata tambayar da batayi zaton zai mata shi a yanzu ba..
"A'a nayi farinciki mana, kawai dai kainane ke É—an min ciwo" tafaÉ—i haka don ta kare kanta, gudun kada yafuskanci wani abu.
"Ayya kiyi haƙuri, anjima idan zanzo zan tahomiki da magani ko, yanzu ki kwanta ki huta, nasan ma stress ne, insha Allah zuwa anjima zaki ji ki normal" yafaɗi hakan cike da kulawa.
"To" kawai ta'iya cewa dashi, haÉ—i da zare wayar akan kunnen ta.
Nannauyar ajiyar zuciya ta sauƙe, haɗe da share ruwan hawayen da suka fito daga cikin idanunta.  "Yazama dole nakoyi soyayyarka Dr Sadeeq, domin bayan kai babu wani wanda zai bani kulawa kamar haka, ya Allah kamin maganin matsalolina!" tafaɗi hakan a bayyane, bayan ta ɗaga idanunta zuwa sama.
Da ƙƴar ma ta'iya cusa abincin da Inna ta bata, domin kuwa hakanan taji zuciyarta ta cunkushe.
Kwanciya tayi akan katifarta tana ƴan tunani, take bacci ɓarawo ya siɗaɗo ya ɗauketa, batare da tashiryawa hakan ba....
Zaune yake akan wata haɗaɗɗiyar kujera, wanda take ita kaɗaice kuma na mussaman acikin bedroom ɗinsa, dake cikin guest hause nashi. ɗan ƙaramin table ne aje a gabansa, wanda samansa ke ɗauke da zungureriyar kwalbar wine da kuma glass cup.
Wayar sace riƙe a hanunsa, gaba ɗaya hankalinsa akan wayartasa yake, murmushine ɗauke akan fuskarsa, yayinda yake playback ɗin vedi'on daya mata ɗazu fitowarta daga cikin shoprite, batare da ta sani ba.
Harzuwa yanzu bai tantance mai yakeji a jiki da zuciyarsa ba a game da Zahrah, abu ɗaya yasani shine, yasan cewa "yana matuƙar buƙatarta a kusa dashi, fiye da tunanin mai tunani, yakuma ɗauki haka, amatsayin fitinanniyar sha'awarta da yake" sake playback ɗin vedion yayi bayan yakai ƙarshe akaro na barkatai domin kuwa yayi playback ɗin vedi'on yafi sau goma daga zamansa a wajen zuwa yanzu.
Wani irin sanyi haÉ—e da kewarta ne suke ratsa zuciyarsa alokaci guda.
"A hankali zankuma cimma burina akanki Zahrah, akaro na biyu ma ina da tabbacin cewa zanyi nasara akan ki, domin niban kasance Loser ba, bakuma zantaɓa kasancewa Loser ba, har abada !" yafaɗi haka cike da son ƙarfafamawa kansa guiwa.. A taƙaice dai haka Zaid yayita playback na vedio ɗin da yayi mawa Zahrah yana kallo, zuciyarsa cike da nishaɗi, abu ɗayane zai hanasa zuwa gareta a yanzu, shine plan ɗin daya shirya mata, bakuma zai je gareta ba, harsai ya tabbatar da cewa ta gama rufzawa cikin tarkonsa, da ya ɗana mata a karo na biyu....
(😲)
Doctor Sadeeq ne tsugune a gaban Baffa Amadu, wato ƙanin mahaifinsa. Bayan ya gama kora masa bayanin duk abun dake faruwa, hatta fƴaɗe'n da akayimawa Zahrah bai ɓoye masa ba, domin kuwa a yanzu Baffa Amadu shine Uba a garesu, kasancewarsa ƙanin mahaifi'nsu.
Ajiyar zuciya Baffa Amadu yasauƙe, haɗe dayin gyaran murya irin tasu ta manya...
"Haƙiƙa kazo da babbar magana Sadeeq, amma kuma duk na fahimceka, bakuma zanyi ƙasa a guiwa ba wajen ganar da mahaifiyarka dakuma ƴar uwarka, amma kuma kasan dole sai an haɗa da haƙuri, kasan su mata koda yaushe tunaninsu baya zurfafa, bakuma ko da yaushe suke gane abun da ake so su fahimta ba, amma tunda kakawo matsalan nan wajena, ka kwantar da hankalinka, ni nan zanje har gida na samu mahaifiyartaka, zamu tattauna akan matsalan!"
Wani irin sanyin daɗi ne yashiga huda zuciyar Dr Sadeeq, sai yanzu yakejin nutsuwa na sauƙar masa, yanzu fatan sa ɗaya, shine Allah yasa mahaifiyarsa ta amince, amma tabbas Zahrah itace burin ran sa...
Daga haka sukayi sallama da Baffa Amadu, bayan ya tabbatar masa cewa lallai zaice yasamu mahaifiyartasa da batun...
Cike da farinciki Dr Sadeeq yabaro gidan Baffan nasa, kai tsaye gidansu ya nufa....
Zama yayi dirshan akan kujeran dake falonsa, haɗe da soma cire safar ƙafansa, fuskarsa cike take da annuri dagani kai kasan yanacikin farinciki...
Turo ƙofar falon nasa akayi da ƙarfin gaske, wanda hakan yatilasta masa ɗago kansa da sauri, don ganin ko waye.
Dammm haka yaji ƙirjinsa yabuga, sakamakon ganin fuskar Hajiyarsa da yayi babu ko ɗigon annuri akanta, saima wani irin mugun kallo da take jifansa dashi.
Cike da girmamawa yace "Hajiya Barkanki da....."
Saurin É—aga masa hanu tayi, alaman batason jin komai daga garesa..
Cikin ɓacin rai da tuƙuƙin zuciya Hajiya tasoma cewa....
"Lallai ka haifu Sadeeq, tunda har zaka iya kai ƙarana wajen ƙanin mahaifinka, yanzu akan wata watsatstsiyar yarinya, ka ke neman ka bijirewa auren ƴar uwa kuma aminiyata da aka baka? Ashe dama wacce kake ikirarin kana so ɗin, ba cikakkiyar mace bace, sauran layine? kaban mamaki ƙwarai Sadeeq, amma bakomai ni na sakema har haka ta faru, kuma tabbas zanɗauki ƙwaƙƙwaran mataki akan ka, daga kai har sakaryar yarinyar da ka bawa soyayyarta amanna, bansan cewa rashin hankalin naka har yakai haka ba, ashe har zuwa kamun ƙafa wajen mutane kakeyi, akan cewa azo a bani baki, nabarka ka auri wacce tagama raba budurcinta ga mazan layi, hmmm wallahi kasaurari hukuncin da zan yanke, kuma tun wuri ka gaggauta cire tunanin auren wannan yarinyar aranka, domin kuwa bamai yi wuwa bane!" fuuu haka Hajiya ta juya ta fice daga falon nasa ranta amatuƙar ɓace...
Kalmar "Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un!"
Shine abun da yafito daga bakin Dr Sadeeq, wanda yasanya hannayensa gaba ɗaya ya dafe kansa...   "Me yasa Aunty Raliya? meyasa zakimin haka?" yatambayi kansa cikin takaici dakuma ɓacin rai.  Tabbas yasan Aunty Raliya ce ta sanar da Hajiyansa komai, domin kuwa lokacin da yake gaban Baffa Amadu ta ƙirasa, bai ɓoyemata ba kuma yashaida mata cewa yana gidan Baffa Amadu'n, ashe ita harta gane mai yakawosa, shine kuma tasanar da Hajiyarsu komai...  Take idanunsa suka kaɗa sukai ja,, ba abun da yake masa ciwo kamar aibata Zahrah da akeyi, kowa idan yatashi sai yajefeta da sunan wacce ta watsar da mutumcinta a waje, alhalin kuma itama ba laifinta bane, ƙaddarace dakuma tsautsayi, domin kuwa shi kansa sheda ne akan abun da yafaru da'ita, tunda har kusan haukacewa tayi. Rasama me yake masa daɗi yayi, da wanne zaiji ne? da soyayyar Zahrah, ko kuma da fushin da Hajiyarsa keyi dashi. Gaba ɗaya ma ji yayi zazzaɓi nason kamasa don haka kawai sai ya koma ɗakinsa ya kwanta, ba abunda yake ambata sai sunan Allah, domin kuwa shi kaɗai ne zai iya kawo masa ɗoki,, dama kuma mu dashi muka dogara shine mai kowa kuma mai komai, sarkin da babu kamarsa, Allah kenan buwayi gagara misali, maiyin duk yanda yaso mai kuma ƙwacewa da kuma bayarwa alokacin da yaso, ga kuma duk wanda yaso.....
Zahrah kuwa tunda ta faɗa duniyar bacci ba'ita tafarka ba, sai gaf da'ana ƙiraye ƙirayen sallan magriba.. Kaitsaye banɗaki ta wuce taje tayi wanka haɗe da ɗauro alwala tazo ta kabbara sallan magriba.
Kayanta marar nauyi tasanya haɗe da ɗauƙan wayarta dakuma ledan da kayan siyayyanta ke ciki, tafito farfajiyar gidan nasu, zaune ta iske Inna tana faman ƙoƙarin kunna redio'nta, wanda koda yaushe take tare dashi kamar jaraba.
"Barka da dare Inna" Zahrah tafaÉ—a lokacin da tayi mawa kanta mazauni a kusa da Inna'n.
Inna bata amsata ba, saima kafe ledar dake hanun Zahrah'n da tayi da ido, Allah Allah take taga mene acikin ledar, domin dama bakinta ya bushe neman abun lasawa takeyi, kasancewar tuwo ta tuƙa abincin dare, bakuma tajin cinsa, tafison tasamu ƙwalam taɗan lasa, like o'o da o'o lol.
Tun Zahrah batakai ga buɗe ledar ba inna tayi gajen haƙuri haɗe da fusge ledar daga hanun Zahrah tashiga dubawa.
Ganin cewa tarkacen su Chocolate's da kuma su biscuit's ne acikin ledar yasanya Inna jan uban tsuka haÉ—e da bankamawa Zahrah harara.
"Aikin kenan gayyar tsiya, mutum yasan bakacin abu, amma saboda tsinannen baƙinciki dakuma mugunta, ko da yaushe shiyake saya bini bini, bazai sayo abun da duka gida za'a amfana ba mcheeww!" cikin ƙufula Inna taƙare maganar, domin kuwa ita duk wannan shirmen banzan basonsu take ba, tafiso taga daƙwalen kaza, kokuma gasheshshen nama mai zafi, yauwa tanan tafi kauri, amma kwata kwata kayan kantin nan ita ba zaɓinta bane.
Da ƙyar Zahrah ta iya danne dariyan Inna dake cikinta aciki.
BuÉ—e ledan tayi gaba É—aya haÉ—e sa sanya hanunta taciro wani É—an madaidaicin cake wanda daganinsa kasan yasha madara.
"Ungo wannan Inna shikan nasan zaki iyaci, saboda kema nasayoshi" Zahrah tafaɗi haka tana mai miƙamawa Inna cake ɗin.
"Yauwa kokefa, amma da kya bani wasu tarkacen banza"Â
Take Inna ta ɓare cake ɗin, tahau ci har lumshe idanu take, domin dai sosai cake ɗin yamata daɗi.
Murmushi kawai Zahrah tayi haÉ—e da gyara zamanta, tasoma latsa wayarta....
Wani yarone yashigo cikin gidan bakinsa É—auke da sallama, atare Inna da Zahrah suka amsa masa.
"Wai ana ƙiran Zahrah a waje" inji cewar yaron..
Wani irin faɗuwa Zahrah taji gabanta yayi harsaida tasanya hanu ta dafe ƙirjinta......
(🤔Miye Zaid yake sake shirya mawa Zahrah ne wai readersðŸ§.
Hajiya problem🤣 Team Dr saiku shirya kuyo gangami kuzo kuyi banbaki ga Hajiya kozata haƙura 😜)
(Ina jin bacci amma haka nayi tƴping ɗinnan, idan kunga tƴping eror kuyi haƙuri saboda typing ɗin dare nayi)
*Voted,Comment,and Share please..... Follow me on Wattpad @fatymasardauna
9:51 pm.....
(kuyi haƙuri banyi posting da wuri ba naje makaranta ne)
ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡
        *SHU'UMIN NAMIJI !!*
  Â
    *Written By*
 *phatymasardauna*
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
        *WATTPAD*
     @fatymasardauna
      〰ï¸ã€°ï¸ã€°ï¸ã€°ï¸ã€°ï¸ã€°ï¸ã€°ï¸
*Editing is not allowed📵*
  Â
  Â
    *CHAPTER 59 to 60*
Wani irin faÉ—uwa Zahrah taji gabanta yayi har saida ta sa hanu ta dafe kirjinta daya fara dukan uku uku.....
"Zahrah na!" yaƙira sunanta jin cewa tayi shiru batace dashi komai ba.
"Umm" ta'amsa masa a kasalance.
"Naji kinyi shiru, ko dai bakiyi farinciki da hakan bane?"
Yajefo mata tambayar da batayi zaton zai mata shi a yanzu ba..
"A'a nayi farinciki mana, kawai dai kainane ke É—an min ciwo" tafaÉ—i haka don ta kare kanta, gudun kada yafuskanci wani abu.
"Ayya kiyi haƙuri, anjima idan zanzo zan tahomiki da magani ko, yanzu ki kwanta ki huta, nasan ma stress ne, insha Allah zuwa anjima zaki ji ki normal" yafaɗi hakan cike da kulawa.
"To" kawai ta'iya cewa dashi, haÉ—i da zare wayar akan kunnen ta.
Nannauyar ajiyar zuciya ta sauƙe, haɗe da share ruwan hawayen da suka fito daga cikin idanunta.  "Yazama dole nakoyi soyayyarka Dr Sadeeq, domin bayan kai babu wani wanda zai bani kulawa kamar haka, ya Allah kamin maganin matsalolina!" tafaɗi hakan a bayyane, bayan ta ɗaga idanunta zuwa sama.
Da ƙƴar ma ta'iya cusa abincin da Inna ta bata, domin kuwa hakanan taji zuciyarta ta cunkushe.
Kwanciya tayi akan katifarta tana ƴan tunani, take bacci ɓarawo ya siɗaɗo ya ɗauketa, batare da tashiryawa hakan ba....
Zaune yake akan wata haɗaɗɗiyar kujera, wanda take ita kaɗaice kuma na mussaman acikin bedroom ɗinsa, dake cikin guest hause nashi. ɗan ƙaramin table ne aje a gabansa, wanda samansa ke ɗauke da zungureriyar kwalbar wine da kuma glass cup.
Wayar sace riƙe a hanunsa, gaba ɗaya hankalinsa akan wayartasa yake, murmushine ɗauke akan fuskarsa, yayinda yake playback ɗin vedi'on daya mata ɗazu fitowarta daga cikin shoprite, batare da ta sani ba.
Harzuwa yanzu bai tantance mai yakeji a jiki da zuciyarsa ba a game da Zahrah, abu ɗaya yasani shine, yasan cewa "yana matuƙar buƙatarta a kusa dashi, fiye da tunanin mai tunani, yakuma ɗauki haka, amatsayin fitinanniyar sha'awarta da yake" sake playback ɗin vedion yayi bayan yakai ƙarshe akaro na barkatai domin kuwa yayi playback ɗin vedi'on yafi sau goma daga zamansa a wajen zuwa yanzu.
Wani irin sanyi haÉ—e da kewarta ne suke ratsa zuciyarsa alokaci guda.
"A hankali zankuma cimma burina akanki Zahrah, akaro na biyu ma ina da tabbacin cewa zanyi nasara akan ki, domin niban kasance Loser ba, bakuma zantaɓa kasancewa Loser ba, har abada !" yafaɗi haka cike da son ƙarfafamawa kansa guiwa.. A taƙaice dai haka Zaid yayita playback na vedio ɗin da yayi mawa Zahrah yana kallo, zuciyarsa cike da nishaɗi, abu ɗayane zai hanasa zuwa gareta a yanzu, shine plan ɗin daya shirya mata, bakuma zai je gareta ba, harsai ya tabbatar da cewa ta gama rufzawa cikin tarkonsa, da ya ɗana mata a karo na biyu....
(😲)
Doctor Sadeeq ne tsugune a gaban Baffa Amadu, wato ƙanin mahaifinsa. Bayan ya gama kora masa bayanin duk abun dake faruwa, hatta fƴaɗe'n da akayimawa Zahrah bai ɓoye masa ba, domin kuwa a yanzu Baffa Amadu shine Uba a garesu, kasancewarsa ƙanin mahaifi'nsu.
Ajiyar zuciya Baffa Amadu yasauƙe, haɗe dayin gyaran murya irin tasu ta manya...
"Haƙiƙa kazo da babbar magana Sadeeq, amma kuma duk na fahimceka, bakuma zanyi ƙasa a guiwa ba wajen ganar da mahaifiyarka dakuma ƴar uwarka, amma kuma kasan dole sai an haɗa da haƙuri, kasan su mata koda yaushe tunaninsu baya zurfafa, bakuma ko da yaushe suke gane abun da ake so su fahimta ba, amma tunda kakawo matsalan nan wajena, ka kwantar da hankalinka, ni nan zanje har gida na samu mahaifiyartaka, zamu tattauna akan matsalan!"
Wani irin sanyin daɗi ne yashiga huda zuciyar Dr Sadeeq, sai yanzu yakejin nutsuwa na sauƙar masa, yanzu fatan sa ɗaya, shine Allah yasa mahaifiyarsa ta amince, amma tabbas Zahrah itace burin ran sa...
Daga haka sukayi sallama da Baffa Amadu, bayan ya tabbatar masa cewa lallai zaice yasamu mahaifiyartasa da batun...
Cike da farinciki Dr Sadeeq yabaro gidan Baffan nasa, kai tsaye gidansu ya nufa....
Zama yayi dirshan akan kujeran dake falonsa, haɗe da soma cire safar ƙafansa, fuskarsa cike take da annuri dagani kai kasan yanacikin farinciki...
Turo ƙofar falon nasa akayi da ƙarfin gaske, wanda hakan yatilasta masa ɗago kansa da sauri, don ganin ko waye.
Dammm haka yaji ƙirjinsa yabuga, sakamakon ganin fuskar Hajiyarsa da yayi babu ko ɗigon annuri akanta, saima wani irin mugun kallo da take jifansa dashi.
Cike da girmamawa yace "Hajiya Barkanki da....."
Saurin É—aga masa hanu tayi, alaman batason jin komai daga garesa..
Cikin ɓacin rai da tuƙuƙin zuciya Hajiya tasoma cewa....
"Lallai ka haifu Sadeeq, tunda har zaka iya kai ƙarana wajen ƙanin mahaifinka, yanzu akan wata watsatstsiyar yarinya, ka ke neman ka bijirewa auren ƴar uwa kuma aminiyata da aka baka? Ashe dama wacce kake ikirarin kana so ɗin, ba cikakkiyar mace bace, sauran layine? kaban mamaki ƙwarai Sadeeq, amma bakomai ni na sakema har haka ta faru, kuma tabbas zanɗauki ƙwaƙƙwaran mataki akan ka, daga kai har sakaryar yarinyar da ka bawa soyayyarta amanna, bansan cewa rashin hankalin naka har yakai haka ba, ashe har zuwa kamun ƙafa wajen mutane kakeyi, akan cewa azo a bani baki, nabarka ka auri wacce tagama raba budurcinta ga mazan layi, hmmm wallahi kasaurari hukuncin da zan yanke, kuma tun wuri ka gaggauta cire tunanin auren wannan yarinyar aranka, domin kuwa bamai yi wuwa bane!" fuuu haka Hajiya ta juya ta fice daga falon nasa ranta amatuƙar ɓace...
Kalmar "Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un!"
Shine abun da yafito daga bakin Dr Sadeeq, wanda yasanya hannayensa gaba ɗaya ya dafe kansa...   "Me yasa Aunty Raliya? meyasa zakimin haka?" yatambayi kansa cikin takaici dakuma ɓacin rai.  Tabbas yasan Aunty Raliya ce ta sanar da Hajiyansa komai, domin kuwa lokacin da yake gaban Baffa Amadu ta ƙirasa, bai ɓoyemata ba kuma yashaida mata cewa yana gidan Baffa Amadu'n, ashe ita harta gane mai yakawosa, shine kuma tasanar da Hajiyarsu komai...  Take idanunsa suka kaɗa sukai ja,, ba abun da yake masa ciwo kamar aibata Zahrah da akeyi, kowa idan yatashi sai yajefeta da sunan wacce ta watsar da mutumcinta a waje, alhalin kuma itama ba laifinta bane, ƙaddarace dakuma tsautsayi, domin kuwa shi kansa sheda ne akan abun da yafaru da'ita, tunda har kusan haukacewa tayi. Rasama me yake masa daɗi yayi, da wanne zaiji ne? da soyayyar Zahrah, ko kuma da fushin da Hajiyarsa keyi dashi. Gaba ɗaya ma ji yayi zazzaɓi nason kamasa don haka kawai sai ya koma ɗakinsa ya kwanta, ba abunda yake ambata sai sunan Allah, domin kuwa shi kaɗai ne zai iya kawo masa ɗoki,, dama kuma mu dashi muka dogara shine mai kowa kuma mai komai, sarkin da babu kamarsa, Allah kenan buwayi gagara misali, maiyin duk yanda yaso mai kuma ƙwacewa da kuma bayarwa alokacin da yaso, ga kuma duk wanda yaso.....
Zahrah kuwa tunda ta faɗa duniyar bacci ba'ita tafarka ba, sai gaf da'ana ƙiraye ƙirayen sallan magriba.. Kaitsaye banɗaki ta wuce taje tayi wanka haɗe da ɗauro alwala tazo ta kabbara sallan magriba.
Kayanta marar nauyi tasanya haɗe da ɗauƙan wayarta dakuma ledan da kayan siyayyanta ke ciki, tafito farfajiyar gidan nasu, zaune ta iske Inna tana faman ƙoƙarin kunna redio'nta, wanda koda yaushe take tare dashi kamar jaraba.
"Barka da dare Inna" Zahrah tafaÉ—a lokacin da tayi mawa kanta mazauni a kusa da Inna'n.
Inna bata amsata ba, saima kafe ledar dake hanun Zahrah'n da tayi da ido, Allah Allah take taga mene acikin ledar, domin dama bakinta ya bushe neman abun lasawa takeyi, kasancewar tuwo ta tuƙa abincin dare, bakuma tajin cinsa, tafison tasamu ƙwalam taɗan lasa, like o'o da o'o lol.
Tun Zahrah batakai ga buɗe ledar ba inna tayi gajen haƙuri haɗe da fusge ledar daga hanun Zahrah tashiga dubawa.
Ganin cewa tarkacen su Chocolate's da kuma su biscuit's ne acikin ledar yasanya Inna jan uban tsuka haÉ—e da bankamawa Zahrah harara.
"Aikin kenan gayyar tsiya, mutum yasan bakacin abu, amma saboda tsinannen baƙinciki dakuma mugunta, ko da yaushe shiyake saya bini bini, bazai sayo abun da duka gida za'a amfana ba mcheeww!" cikin ƙufula Inna taƙare maganar, domin kuwa ita duk wannan shirmen banzan basonsu take ba, tafiso taga daƙwalen kaza, kokuma gasheshshen nama mai zafi, yauwa tanan tafi kauri, amma kwata kwata kayan kantin nan ita ba zaɓinta bane.
Da ƙyar Zahrah ta iya danne dariyan Inna dake cikinta aciki.
BuÉ—e ledan tayi gaba É—aya haÉ—e sa sanya hanunta taciro wani É—an madaidaicin cake wanda daganinsa kasan yasha madara.
"Ungo wannan Inna shikan nasan zaki iyaci, saboda kema nasayoshi" Zahrah tafaɗi haka tana mai miƙamawa Inna cake ɗin.
"Yauwa kokefa, amma da kya bani wasu tarkacen banza"Â
Take Inna ta ɓare cake ɗin, tahau ci har lumshe idanu take, domin dai sosai cake ɗin yamata daɗi.
Murmushi kawai Zahrah tayi haÉ—e da gyara zamanta, tasoma latsa wayarta....
Wani yarone yashigo cikin gidan bakinsa É—auke da sallama, atare Inna da Zahrah suka amsa masa.
"Wai ana ƙiran Zahrah a waje" inji cewar yaron..
Wani irin faɗuwa Zahrah taji gabanta yayi harsaida tasanya hanu ta dafe ƙirjinta......
(🤔Miye Zaid yake sake shirya mawa Zahrah ne wai readersðŸ§.
Hajiya problem🤣 Team Dr saiku shirya kuyo gangami kuzo kuyi banbaki ga Hajiya kozata haƙura 😜)
(Ina jin bacci amma haka nayi tƴping ɗinnan, idan kunga tƴping eror kuyi haƙuri saboda typing ɗin dare nayi)
*Voted,Comment,and Share please..... Follow me on Wattpad @fatymasardauna
9:51 pm.....
(kuyi haƙuri banyi posting da wuri ba naje makaranta ne)
ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡
        *SHU'UMIN NAMIJI !!*
  Â
    *Written By*
 *phatymasardauna*
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
        *WATTPAD*
     @fatymasardauna
      〰ï¸ã€°ï¸ã€°ï¸ã€°ï¸ã€°ï¸ã€°ï¸ã€°ï¸
*Editing is not allowed📵*
  Â
  Â
    *CHAPTER 59 to 60*
Wani irin faÉ—uwa Zahrah taji gabanta yayi har saida ta sa hanu ta dafe kirjinta daya fara dukan uku uku.....