← Book details Shu'umin Namiji Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 26 OF 112

Sashe 26

Shu'umin Namiji Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

((Sau dayawa akan cutar damu ƴaƴan talakawa,   amma bamu isa mu kai ƙara ba,  mune da gaskia, amma mu'ake bawa rashin gaskia, maiyasa ? saboda mu bamu da kuɗi, wanda bashi da kuɗi kuma ba mutum bane a wajenku ko?  anacin zarafin ƙananan yara dakuma ƴan mata,  amma ba a iya ɗauka musu mataki, saboda kawai wanda suka aikata abun masu hanu da shuni ne, mukuma an maidamu ko'oho, Allah sarki Allah ka'iyar mana, kabimana haƙƙinmu gaduk wani wanda yazaluncemu Ameen.))

    
        *20/November/2019*

    
       *Voted, comment, and share please... Wattpad @Fatymasardauna*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

       
           *SHU'UMIN NAMIJI !!*

      *Written By*
Phatymerhsardauna

*Dedicated To My Lovely Brother Khabier*

*🌈Kainuwa Writers Association*

{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}

*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*

            *WATTPAD*
      @fatymasardauna

*( Masha Allah! ina matuƙar tayaki murnan kammala daddaɗan book ɗinki my sweetheart (Ladingo Ummu Fareesa) Allah ya baki ladan dake ciki, yakuma yafe miki kurakuran dakikayi aciki, haƙiƙa kinyi ƙoƙari sosai Sweetheart, kuma littafin HATSABIBIYA RAMLAT ya nishaɗantar, yakuma faɗakar, fatan mu Allah yaƙara miki basira da hazaƙa Ameen, ina miki fatan alkhairi My Sweetheart.)

*Chapter 36 to 37*

  A hankali yake tafiya da motarsa har yakawo ƙofar gidan,  dai dai tsayawur motar tasa, Baffa ya fito daga cikin gida.    

cikin hanzari ya ƙaraso inda motar Dr Sadeeq ɗin ke fake, "A'a likita kaine da yammacin nan haka ?" Baffa yafaɗa fuska cike da annuri,

"Eh wlh nine Baffa, tun safe naso zuwa, to aikine yayimin yawa "  Dr Sadeeq yafaɗa yana mai ƙoƙarin fitowa daga cikin motar tasa.

"To muje nayi maka iso zuwa cikin gidan ko, aikuwa mutumiyar taka tanacan ta kulle kanta a É—aki, tana karatu "

"Karatu kuma Baffa? badai ta dawo normal ba ?" Dr Sadeeq ya tambayi Baffa cikin sakin fuska, domin har yaÉ—anji sanyi a cikin zuciyarsa daga jin maganan Baffan,

"Ƙwarai kuwa likita, ai yanzu duk wannan hargowan kukan ta dainashi!" Baffa yafaɗa dai dai sanda suka kawo cikin gidan,

Da fari'a Inna ta tarbi Dr Sadeeq,  haɗe da baje masa tabarma a ɗan madaidaicin tsakar gidan nasu,   shima cike da mutum tawa ya gaida ta.

Bayan sun gama gaisawanne yake tambayar ko Zahrah tana shan magungunanta ?

Take Inna tace yabiyota tayi masa iso zuwa É—akin Zahrah'n,
Ba musu yabi bayan Inna duk da cewa yasan hakan baidace ba, amma bayida wani zaɓi sai hakan, domin kuwa shima yanason ganinta.

Zaune take akan katifa, yayinda hanunta ke ɗauke da wani ɗan ƙaramin Al'Qur'ani, tana karantawa ƙasa ƙasa,  a hankali taɗago kanta jin muryar Inna abakin ƙofar shigowa ɗakin nata,  

"Shigo mana likita " Inna tafaÉ—a tana mai wangale É—an yalolon labulen É—akin,

Yanashiga cikin ɗakin,  Zahrah tamiƙe zumbur daga zaunen da take, take jikinta yasoma rawa,

Ganin yanda yanayinta ya sauya alokaci ɗaya, yasa Dr Sadeeq tsayawa cak a inda yake, yana mai ƙare ma ta kallo,  kallo ɗaya yayimawa idanunta, yafahimci cewa tayi kuka, take yaji ba daɗi a zuciyarsa.

"Zahrah!" yaƙira sunanta cikin muryar nutsuwa,

Kasa amsa masa tayi saima kau da kanta gefe da tayi tana mai rumtse idanuwanta, domin kuwa sosai Likitan yake mata yanayi da Zaid.

Cikin muryar nutsuwa ya kuma  cewa "Kifito waje inason magana dake"

Yanakai ƙarshen zance'nnasa,  yajuya yafice daga cikin ɗakin.

Tunyanasa ran fitowar Zahrah hardai yacire rai domin kuwa babu alaman zata fito É—in.

Daga ƙarshe dai kayan marmari da kuma sauran magungunanta da ya taho mata dashi, sai Baffa ya bawa yace a bata, don yafahimci batason damuwa, kuma yafuskanci cewa tana matuƙar tsoronsa, baikuma san dalilin hakanba.

Tanajin ƙaran tafiyar motarsa ta sauƙe nannauyar ajiyar zuciya, hakanan duk sanda ta kallesa takejin faɗuwar gaba, shigowar Inna cikin ɗakin shiyayi sanadiyar katsuwar tunaninta,,

Ƙatuwar ledan da Dr Sadeeq  yakawo, wanda yake cike da kayan marmari Inna ta aje mata haɗe da watsamata harara gami dayin tsuka tafice daga cikin ɗakin, domin yanzu gaba ɗaya tsananin haushin Zahrah'n takeji.

Ko kallon ledan Zahrah batayiba ballantana ta duba miye a ciki, domin itakam yanzu anshata kuma haryanzu bata warke ba, don haka babu wani ɗa Namiji daya isa yasake yaudaranta, babu kuma wani Namiji da zata sake amincewa dashi a iya tsawon rayuwarta, tasan cewa ingancin rayuwarta yariga dayagama ƙarewa, domin kuwa tasan cewa babu wani namiji dazai aureta, bayan yasan cewa Zaid yariga da ya gama keta mata rigan mutumcinta.

New York City

Gudu sosai motar tasa keyi akan  titi tamkar zai tashi sama, yayinda jami'an tsaron dake tsaron titi suke tayi masa magana amma bayako sauraransu,   kai tsaye katafaren gidansa dake cikin New York ɗin ya nufa, tundaga fitowarsa acikin motar zaka gane cewa a matuƙar buge yake  domin kuwa sai haɗa hanya yake gakuma zungureriyar kwalbar giya dake  riƙe a hanunsa,  yana shiga cikin katafaren falonnasa, yafaɗa kan kujera, haɗe da lumshe  idanunsa,
"MY ZAHRAH!!"   yaƙira sunanta cikin wani sweetness voice ɗinsa, sannan kuma cikin yanayi mai nuni da cewa mutum yana cikin shauƙi,, da ƙyar ya iya miƙewa yakai kansa zuwa ɗaki, yanashiga cikin bedroom, kaitsaye ya wuce bathroom saida ya amayar da gaba ɗaya giyan da yasha, kafun yasamu nutsuwa, amma duk da haka mayen giyan bai sake sa ba.

Buɗe drowern sa yayi, haɗe da fiddo wani irin ƙaton hoto wanda gaba ɗayansa aka rufesa da glass ma'ana akayi masa gidan glass, ba hoton kowa bane face hoton kyakkyawar fuskar Zahrah tana murmushinta mai burgewa.

Murmushi yayi haɗe da mannawa hoton kiss, cikin unique voice ɗinsa yace "Inakewarki My Zumata, haƙiƙa keɗin ta da bance, verysoon inanan dawowa gareki, har yanzu sha'awarki bata sakeni ba, banƙoshi dake ba babyna, kikulamin da kanki kinji Sweet Zahrah na!!" yaƙare maganar cike da tsananin shauƙi, domin kuwa wani irin feelings yakeji a ga me da Zahrah'n, yarasa maiyake damunsa akan Zahrah, aƙa'idansa idan yayi sex da mace sau ɗaya, to baya sake waiwayanta harsai idan ita tawaiwayesa, nan ma saiyaga dama ya amsa tayinta, amma yau gashi yana mugun kewar Zahrah saboda yasha zumanta mai daɗin ɗanɗano, haryanzu baisan menene so ba, sha'awa kawai yasani akan haka kuma ya dogara.

Haka Bacci yaɗauki Zaid yanata sambatu irin na mashaya yayinda yake rungume da hoton Zahrah akan ƙirjinsa, yana ji  tamkar Zahrah'nce dakanta ya runguma a ƙirjinsa.

Washe gari bashine yatashiba sai ƙarfe 9 na safe, salati yasoma yi cike da ƙuncin rai,  sam baisan maiyasa yake makara  sallan asuba a kwana biyunnan ba,  ( Nace Saboda Zina bata haɗuwa da ibada )  daƙyar ya'iya tashi yashiga bathroom domin gaba ɗaya jiyake jikinsa na masa ciwo,gashi kuma baida time ɗin da zaiyi gym,   wanka yayi cikin mintuna ƙalilan, fitowa yayi sanye da rigan wanka ajikinsa, agurguje yamurza lotion ajikinsa haɗe da sanya hand dryer ya busar da gashin kansa,   wata baƙar jallabiya yasanya haɗe da nufar inda darduma ke shumfuɗe, yatada kabbaran sallah, ko kunya bayaji.

(Tir da hali irinnaka Zaid, sallah da rana faÉ—e faÉ—e Allah yashirya)

Yana idar da sallah, ya buɗe ma'adanan clothes ɗinsa haɗe da zaro wasu riga da wando masu matuƙar kyaun gaske,   koda yasanya kayan sosai suka amshi jikinsa kasancewarsu masu kalar  fari, daga takalmi, belt harzuwa agogon dake ɗaure a hanunsa kalar maroon garesu, haɗaɗɗiyar rigar suit maroon colour yaɗaura akan kayannasa, take yafito a asalin Zaid ɗinsa, wato  Abundance, Increase, Increment, Superabundance, Addition, Excess, Surplus, haƙiƙa Zaid kyakkyawane kuma cikakken namiji da ya isa ɗaukar hankali ko wacce irin mace ce afaɗin duniyar nan, haƙiƙa Zaid yana da kyakkyawar sura irinta cikakkun maza, haka kuma yanada matuƙar burgewa abubuwan da Zaid kedasu  naburgewa suna da tarin yawa, tamkar yanda ma'anar sunansa ke da tarin yawa,  shikansa yasan yayi kyau sosai, babu kuma abunda ke tashi a jikinsa sai tashin ƙamshi mai sanya nutsuwa da kuma sanya shauƙi,

Al'adarsa ce kullum kafun yafita saiya bawa hotonta kyakkyawan sumba (kiss), to yauma hakance takasance domin wannan hoton nata yaÉ—auko, ya manna mawa kiss, haÉ—e da maidashi ya aje, kaitsaye yafice daga cikin É—akin, ko sauraran kayan breakfast É—in da aka aje masa akan derny table baiyi ba yasakai yafice daga cikin Aljannar duniyar falon nasa,, yana fita yashiga cikin motarsa, kai tsaye yawuce babban hotel É—in dazasu gudanar da meeting, domin yau sunada gagarumin meeting, zuwa yanzu gaba É—aya duk an hallara a wajen shikaÉ—ai kawai ake jira, domin shida ma'aikatansa ne zasuyi meeting É—in.

Nigeria

Yau kimanin sati guda kenan tunda Dr Sadeeq yazo baisake zuwaba, ɓangaren Zahrah kuwa sosai takesamun sauƙi acikin zuciyarta, sakamakon karatun Al'Qur'ani da tariƙe babu dare ba rana, zuwa yanzu ta dangana komai nata ga Allah, tasan ko ba daɗe ko ba jima zai bi mata haƙƙinta.

Zaune take a tsakar gidannasu tazuba uban tagumi, amma a zuciyarta karatu takeyi,  Inna ce kishingiɗe a gefenta, tana koran sauron dasuka addabeta kasancewar dare yasoma rufawa domin kuwa har an idar da sallan magriba,,

Baffane yashigo cikin gidan fuskarsa É—auke da fari'a, Inna ce kawai ta amsa masa sallaman da yayi, kallon Zahrah yayi haÉ—e da cewa "tashi ki É—auko hijabinki likita na jiranki a waje"

Wani irin mummunan faɗuwa gabanta yayi, domin dudduniya a yanzu babu abun da zai ɗaga mata hankali kamar ace wai wani naƙiranta a waje,  sam itakam tagama cire ƙauna da sake zuwa ƙiran wani,  bata ƙaunarma koda sake fita waje ne,

"Wai ba magana nakeyimiki bane Zahrah kin shareni kuma bayan kinajina!" Baffa yafaÉ—a cikin faÉ—a faÉ—a,

Kuka Zahrah tafashe dashi haÉ—e da É—ago idanunta, ta kalli Baffa cikin muryan kuka tace "Baffa kataimakeni dan Allah, wallahi banso wani abu yasake faruwa da rayuwata !! "

"Ikon Allah, Malam kajita ko zata sake ɓarar mana da daman da muka samu na biyu, saikace akanta aka fara yin fyaɗe!" Inna tafaɗa cikin ɗaga  murya,,
Chapter 26 · 0% Book details