← Book details Shu'umin Namiji Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 108 OF 112

Sashe 108

Shu'umin Namiji Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hannayenta tasanya acikin gashin kansa, tashiga ya mutsawa, hadda kai masa cizo a wuyansa.   Sai da tayi masa buji buji da kayan jikinsa kafun ta ƙyalesa, gashin kansa ma gaba ɗaya ta hargitsa masa shi.  Koda ta kawo masa abinci tare sukaci, yana kwance ajikinta itakuma tana bashi abincin abaki,  ahaka har ya ƙoshi.

Kallonta yayi da idanunsa, dake tsumata kana yace "Namatsu abani ke Baby na, wallahi ina kewar ɗumin ki sosai, amma Hajiya gaba ɗaya ta kanenaye min ke, waidole saikinyi arba'in, Babyna kice tabarmu mu koma gidanmu kinji!" cikin yanayi na shagawaɓa ya faɗi haka.

Murmushi Zahrah tayi, haɗe da sanya hanu ta shafi kumatun sa, cike da ƙaunarsa tace "Kayi haƙuri Hubby, nima ina kewar sucking ɗinka,  kuma ai bawai bazan dawo bane zan dawo fa" tafaɗi hakane don kawai  ta kwantar masa da hankali.

Ya buɗe baki zaiyi magana kenan muryar Hajiya ta karaɗe kunnuwansu, inda take cewa. 
"To iyayen rashin kunya, saika tashi katafi dare na ƙarayi, ke kuma miji daɗi, ga yaronki nan, abincinsa yakeso ki basa."   kunyar Hajiya ne yakama Zahrah, haka ta amshi yaron kanta a ƙasa. 
Doctor kuwa turawa Hajiya baki yayi, haɗe da cewa "Hajiya zantafi, amma kiɗanyi haƙuri ba yanzu ba mana"

Baki Hajiya ta sake tana kallonsa. "Sannu marar ta ido, wallahi saika tafi yanzu kuwa" Hajiya tafaɗi haka tana me kama hanunsa, haka yanaji yana gani ta fitar dashi daga ɗakin, Zahrah kam dariya taketa yi masa.   Bayan ta shayar da yaron natane, tashiga toilet tayi wanka, doguwar rigan bacci tasanya, kana ta ɗauko diary'nta, rubutu tayi aciki, ta mayar dashi ma'ajinsa. Kwanciya tayi luf akan gado, cike da tunani kala kala bacci ya ɗauketa.... 

*** *** ***

Yau kwanansu 50 cif cif agidan Hajiya, sunƙara kwanaki 10 akan kwanakin gama wankansu,  idan kaga Zahrah bazakace ita bace, sosai taƙara cika da kyau, fatarta ta ƙara haske, komai nata yasake cika, gwanin sha'awa,  yau ne zata koma gidanta, tuni Dr.Sadeeq ya sanja mata kayan furnitures ɗinta, komai yasanya mata sabo,  Hajiya kuwa tun tuni taketa ɗirka mata magunguna, haka Aunty Raliya ma ta dage sai bata wasu magunguna masu ƙarfi take, ita kuwa sha take abunta, wanda taji yanada bauri ne kawai take ajiyewa bata sha.

Wanka ta tsantsara cikin wata jar atamfa Super Exclusive, wacce taji ɗinkin riga da sket, sosai kayan ya amshi jikinta,   zama tayi da kanta, ta tsantsarawa fuskarta kwalliya, sai gashi kuwa kyawunta ya ƙara bayyana,  dogon gashinta dayasha gyara ta tubke da ribbon haɗe da kafa ɗaurin ɗan kwalinta me kyau,  wani red ɗin takalmi tasanya aƙafanta me tsinin gaske, ɗan ƙaramin mayafi ja ta ɗauka ta rufe jikinta dashi, babu abun dake fita ajikinta, sai daddaɗan ƙamshi.

Yana tsaye ajikin motarsa dake fake a  compound ɗin gidan,  yaga fitowarta, kusan suman tsaye yayi.  "Tabbas Zahrah me kyauce, tahaɗu tako ina, kullum ƙara kyau da cika take, lallai kuwa da yayi saken barin Zahrah, tabbas da yazama soko, marar rabo, samun mace kamar Zahrah, babban sa'ane daya samu a rayuwarsa" yafaɗi haka acikin zuciyarsa, yana hangame da baki wajen kallonta, baisan ma taƙaraso garesa ba, saida yaji ni'imtaccen ƙamshinta na ratsa cikin hancinsa.

Murmushinta me kyau tayi masa haɗe da kashe masa idanunta ɗaya.    "Ya dai kwalliyar tayi maka ne" tafaɗi haka tana me juya masa bayanta. Alaman yaganta da kyau.

Yawu ya haɗiye, alokacin da idanunsa suka sauƙa akan hips ɗinta,   baigama dawowa hayyacinsa ba, yakuma jefa idanunsa akan ƙirjinta, jikinsa na rawa ya jawota ya rungumeta.

Wani irin ajiyar zuciya suka sauƙe atare. 
  "I really Miss you Babyy!!"  yafaɗi haka akasalance.

"Miss you too dear!"  itama ta mayar masa da amsa cikin muryar raɗa.

Hajiya dake kallonsu ta window tasaki murmushi haÉ—e da komawa cikin falonta ta zauna, aranta tanayi musu fatan shiriya.

Saida suka biya ta JABI lAKE sukayi sayayya tukun kafun daga nan suka wuce gida.

Wanka ta sakeyi ta shirya kanta cikin wata irin fitinanniyar sleeping gown, wacce ta bayyana komai na surarta bata ɓoye komai ba,  rigar doguwace har kusan ƙafa, amma kuma duk da haka itaɗin kamar babu take, kasancewarta shara shara.   dogon gashinta ta sake a bayanta, haɗe da shafe jikinta da shu'umar Humra,     wani sweet Lip Gloss tashafa akan leɓenta.

Yana zaune a falo yana danna laptop ɗinsa,  ƙamshinta ne yafara kawo masa ziyara, lokacin daya sauƙe idanunsa, akanta sai da yaji wani irin shock ajikinsa,  da sauri ya miƙe ya ƙarasa gareta.   buɗe hannayensa yayi daniyar rungumeta, da sauri ta matsa gefe, tanayi masa dariya, haɗe da yin wata irin tsayuwa,  wacce takusa zautar dashi.

Lumshe idanunsa yayi tare da sanya hanunsa ya jawota jikinsa. Ƙam ya rungumeta, sai gashi yana sauƙe ajiyar zuciya akai akai.   Kallon juna suka shiga yi idanun ko wannensu ɗauke da tsananin sha'awar ɗan uwansa. Jikinsa na rawa ya kama lip ɗinta na ƙasa, yana tsotsa ahankali, jiyake kamar yanashan honey.    da kanta ta zame rigar dake jikinta, ta faɗi ƙasa, take surarta ya bayyana,  hmmm ba yau yafara ganinta ba, amma kuma ya zautu ƙwarai daganin surar jikinta, jiyake kamar ma baitaɓa kusantarta ba, sosai yayi missing ɗinta.    Jikinsa na rawa ya ɗauketa suka wuce bedroom,  tuni dama Asad yayi bacci, dama shi haka yake sam baida ƙiriniya,  daya ƙoshi sai bacci, bakuma zai tashiba sai dai idan yanajin yunwa.  

A yau ɗin ne suka sake tabbatar da cewa sunyi kewar juna,  musamman ma  Doctor Sadeeq da kusan cinyeta ne kawai baiyi ba, gaba ɗaya ya zauce, ya susuce, wasu maganganu yake wanda ita kanta batasan me yake cewa ba, saboda sun lula wata duniya ta musamman, wacce  sukayi nisa  acikinta basaji basa gani, kansu kawai suka sani. Aranan nan wata zuma suka shayar da junansu, wanda bazasu taɓa mantawa ba. Wannan ranan takasance rana ta biyu masu muhimmanci a garesu.

*** *** ***

Bayan wata 6........

America

Zufa ne keta ketowa ta goshinsa, gaba ɗaya baya cikin nutsuwarsa, kai komo yaketayi agaban labour room ɗin sama da 1 hour kenan yana abu ɗaya, jiyake kamar yasanya hanu akansa yaita ƙwala ihu.  Ɗaya daga cikin  Nurse ɗin dake kanta na fitowa  ya nufi wajenta, da sauri idanunsa sunkaɗa sunyi jajur dasu.  Murmushi Nurse ɗin tayi masa haɗe  da cewa "Ina tayaka murna, matarka ta haihu, kasamu baby girl"   wani irin sanyin daɗi yaji acikin ƙirjinsa, baisan lokacin dayayi sujja don nuna godiyarsa ga Allah ba. 

Ana kaita ɗakin hutu, wata nurse tace yashigo ya karɓi babynsa,    lokacin daya sanya hannayensa ya amshi babyn, wani irin kukane ya ƙwace  masa, alokacin da idanunsa suka sauƙa akan kyakkyawar fuskarta kuwa,  bugun zuciyarsa ne ya ƙaru, saboda  kokaɗan  yarinyar bata kama da mahaifiyarta,  durƙushewa yayi aƙasa, riƙe da yarinyar tasa yana kuka, hakan kuwa sosai yabawa likitotin mamaki.

Bakomaine yasa sa yake kuka haka ba,  face tsananin danasani na rayuwar da yayi abaya da yake.   yakasance mazinaci, mashayin giya.  "Yanzu idan ƴarsa mafi soyuwa agaresa, tataso taji labarin abun da ya aikata a baya,  wani irin kunya zaiji? mezaice da'ita idan ta tambayesa, meyasa yazamo haka?" tambayar da yayiwa kansa kenan, amma kuma baida amsa, baida kuma me amsa masa.

Rungumeta ya sakeyi tsam,  acikin ƙirjinsa, ahankali yace.

"Kindawo gareni Zahrah, Allah yadawomin dake, Inasonki Inasonki, inamiki so na musamman Allah ya albarkaceki ƴata!!!" kiss ya manna mata akan goshinta, kana yazuba mata idanu,  bazaiyi mamakin kamannin daya gani akan fuskar ƴartasa ba, saboda yasan ba aja da ikon Allah, kuma hakan ma wata rahamace da Allah yayi masa,  Allah ya hanasa Zahrah alokacin dayaso, yanzu yakuma basa Zahrah alokacin dayaso,   hancinta bakinta duka kalan nasa ne, amma kuma idanunta tamkar idanun Zahrah aka ciro aka sanya mata, kallon farko da yarinyar tayi masa, saida yaji tsikar jikinsa ya tashi, saboda gani yayi tamkar Zahrah ce dakanta agabansa.  yana rungume da yarinyar ya ƙarasa gaban Afrah dake kwance akan gado tana kallonsu,  ranƙwafowa yayi ya manna mata kiss akan goshinta, hanu yasa yashafi kumatunta, haɗe da cewa "Nagode ƙwarai Afrah, Allah ya miki albarka, bazan manta da wannan ƙoƙarin da kikamin ba, Inasonki"

Karo na farko kenan arayuwarta da taji kalmar nan tafito daga bakinsa akanta,  "Inasonki" ta maimaita kalmar abakinta cike da mamakinsa.
Kansa yajinjina mata haɗe da sakin murmushi. 

"Ki kwanta ki huta, nasan kinsha wahala sosai" yafaÉ—i haka yana shafa kanta.
Lumshe idanunta kawai tayi saiga hawaye nabin kan fuskarta. Hanu ta miƙa masa ya bata yarinyar,   ba iya mamaki ba hadda tsoro saida ya bayyana akan fuskar Afrah, sakamakon ganin fuskar yarinyar ɗago kanta tayi ta kalleshi da sauri.

Kamar yasan me take tunani,  murmushi yayi mata haɗe da ɗaura hanunsa akan kafaɗanta.   "Kada kidamu, Allah ne yayi ikonsa, Allah ne yadubeni yayimini rahama,  sannan kuma ko da ace kowa zaiyi mamakin kamannin yarinyar ni bazanyi ba, saboda wacce take kama da ita, jinin jikinane, sannan kuma Allah yana da ikon yin komai"

Ajiyar zuciya kawai Afrah ta sauƙe haɗe da kafe yarinyar nata da ido, tabbas da badan taji ƙauna irinta uwa da ƴa akan yarinyarba, to tabbas da tace ba itace ta haifi yarinyar ba, Zahrah ce, shine aka sanja mata, aka ɗauki nata aka kaita wani gun, itakuma aka kawo mata wannar, a matsayin ƴarta. Rungume ƴar tata tayi, tanajin ƙaunarta aranta.
***

Suna komawa gida Zaid yayiwa Afrah kyautar zuƙeƙiyar mota, tare da kuɗi Naira Million 3 duk na murnan ta haifa masa baby ne,  washe gari kuwa suka tarkato suka dawo Nigeria, abisa takurawan Mom ɗinsa. amma da anyi suna yace  zasu koma.  Aranan da aka haifa masa Zahrah aranan ya mallaka mata babban kamfaninsa na ƙera takalma, dake Italy, aranan kuma akasanjawa kamfanin suna zuwa sunan yarinyar, saɓanin da dayake sunan Zaid.

Tunda aka haifi Zahrah Zaid baibari kowa ya ɗauketa ba, inbanda uwarta, nan ma nono kaɗai take bata,  idan yaɗauketa yashiga ɗakinsa da ita, kulle ƙofar yake da key gudun kada wani ya damesa, komai na duniya shiyake mata, wani irin so da ƙaunar yarinyar yake ji, wanda baitaɓa jin irin saba, akullum kallon Zahrah kawai yakeyiwa yarinyar. Irin soyayyar dayake yiwa yarinyar shike tsorita kowa.
Chapter 108 · 0% Book details