← Book details Shu'umin Namiji Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 101 OF 112

Sashe 101

Shu'umin Namiji Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tsaye yake acikin kitchine gaba ɗaya ya haɗa gumi, banda ƙonewan da yayi a hanunsa yafi  sau biyar, yanzuma ƙonewa yayi a babbar yatsarsa, na hanun dama, ya tsaya yana hura wajen,    kwanon soya ƙwaine ɗaure akan gas, yayinda hanunsa ke riƙe da cokali,  gaba ɗaya gaban gas ɗin ya ɓaci da manja, gashi har gaban rigar sa manjan ya taɓa, waishinan wainar fulawa yakeyi (Hana baba tashi, mudai muke cemai anan, amma sauran garuruwa bansan me suke ƙiranshi ba, kunsan hana baba tashi akwai daɗi, musamman idan yaji yaji😋😂)

Ƙoƙarin juya wainar fulawan yake, amma yaƙi juyuwa, gaba ɗaya ya ƙona hannayensa, har wainarma tasoma ƙonewa, da ƙyar ya samu ya kwashe, kuma dama wanda ke cikin kaskon shine na ƙarshe, kashe gas ɗin yayi haɗe da ɗaukan tissue ya goge gumin dake tsastsafowa a goshinsa,    plate ɗin wainar da kuma roban yaji yaɗauka ya nufi falo.

Tana zaune akan sofa, tayi piecess da ƙafafunta, sanye take da wata ƴar riga marar nauyi,  itanan zaman jiransa take, yakawo mata wainar fulawanta taci. Yana shigowa cikin falon tasaki dariya, domin kuwa har kumatunsa manja ne.
Ganin haka yasanya sa  ɓata fuska, haɗe da tsayawa yana jifanta da hararan wasa.

"Kaganka kuwa, chab aikuwa  kayi dumu dumu da manja!" tafaɗi haka tana ƙoƙarin gimtse dariyarta.

Shagwaɓe fuska yayi kamar wani ƙaramin yaro,  plate ɗin wainar yakawomata gabanta ya aje mata, haɗe da aje mata roban yaji,  muƙut  haka ta haɗiyi wani yawu tsabar kwaɗayi, tuni ya wunta ya tsinke, jawo plate ɗin gabanta tayi, haɗe da gutsuran wainar fulawan takai bakinta.  Da sauri ta tofar da wainar fulawan sai kuma tashiga kelaya amai, babu ƙaƙƙautawa, amatuƙar ruɗe yayo kanta,  shiya riƙeta harta gama yin aman,  dakansa ya gyara wajen,   zama yayi haɗe da jawota jikinsa cike da tausayinta, yashiga yi mata sannu.   
Kwanciya tayi luf acikin ƙirjinsa tana me sauƙe ajiyar zuciya,  sosai tagalabaita, amai ba wasa ba.

Bayanta yake shafawa a hankali, yana É—an jijjigata, kamar wata jaririya.

"Abincinne ba daɗi, yasa kikayi amai?"  yatambayeta.

Ya mutsa fuska tayi haɗe da ɗaga masa kai ashagwaɓe tace "Ƙauri haɗe da warin hayaƙi wainar fulawan keyi"

Narke fuska yayi haɗe da karya wuyansa gefe,  "yanzu duk ƙoƙarin nan da yayi, yatashi a banza?" yatambayi kansa.

Ajiyar zuciya yayi haɗe da cewa "Kiyi haƙuri, bansan ya akayi yayi warin hayaƙi ba, yanzu to mezakici?" cike dakulawa ya kuma tambayanta.

Zahrah ƴar rigima da shagwaɓa, sake narke masa tayi, ɗan ƙaramin bakinta taturo gaba, haɗe da cewa "Ni yanzu,  Banana PineApple Smoothie kawai zan sha"

"Banana pineapple smoothie ba abincine wanda zai riƙeki ba, kifaɗamin yanzu me kike so bayan  smoothie ɗin?"

"Gasashshen nama, wanda aka sa masa, sweet pepper dakuma onion" ta faÉ—i haka tana tanÉ—e baki.

Hanu yasanya yashafi gefen kumatunta, inda dogon suman kanta ya kwanta,  "Wannan ba abun damuwa bane, kinaso muje mu sayone kokuma naje ni kaɗai?"

Tsulum tatashi zaune haÉ—e da cewa "muje tare"

Ɗaki suka koma shida kansa ya shiryata cikin, wani doguwar riga na lace, yanaɗe mata jikinta da wani vail marar nauyi,  shima kayan jikinsa ya sauya, suka fita hanunsu sarƙe acikin na juna. 

Wani haɗaɗɗen hotel suka nufa,  hotel ɗin namusammanne, domin kuwa sai waƴanda suka amsa sunansu ne suke zuwa cin abinci wajen.

Yana riƙe da hanunta suka kutsa cikin hotel ɗin,   awani ɓangare wanda babu yawan jama'a sosai suka zauna,   suna zama wata waiter da jikinta ke sanye da uniform taƙaraso wajensu, cike da girmamawa ta basu menu, dan zaɓan abun da suke so,   Zahrah ce takarɓi menu'n tazaɓi abun da takeso akawo mata, Dr.Sadeeq kam bai buƙaci komaiba, saboda a ƙoshe yake.
Mintuna kaɗan aka kawowa Zahrah abun da takeso,  gyara zamanta tayi, haɗe da ɗaukan gasashshen namanta tasoma ci, harwani lumshe idanunta takeyi tsabar daɗi, ji take kamar bata taɓa cin wani nama me daɗin wannan ba,  sosai taci naman, kana ta ɗaura banana pineapple smothie akai,   shidai kallonta kawai yake, kome tayi burgesa take,  kallonshi tayi da fararen idanunta, haɗe da ɗaukan tsokan nama guda ɗaya, takai bakinsa, babu musu yabuɗe bakinsa tasamai,   ɗage masa giranta guda ɗaya tayi  sama,  haɗe da cewa "Yakaji naman, daɗi ko? hmm ai daga yau kullum anan zanna cin nama!" taƙare maganar tana jijjiga kanta,  shidai murmushi kawai yaketa aika mata.

Harta gota, zata wuce, sai kuma tayi saurin dawowa da baya, sake ware idanunta tayi akan yarinyar, tabbas itace  bazata manta fuskarta ba,   kallon yarinyar tashigayi sosai,  itakuma yarinyar sai dariya take tana kaɗa kanta, da'alama tana cikin farinciki.    "Zahrah!" taƙira sunan yarinyar ahankali, yanda ita kaɗai da tayi maganar ne zataji me tace,   "Itace wacce hotunanta suka cika jikin bangon ɗakin Zaid, kenan itace Zahrah'n Zaid? itace mafarki dakuma burinsa?" abun da Afrah ke faɗa kenan acikin zuciyarta, tsintar kanta tayi da tsayawa tana kallon ta, bawata babba bace bazata wuce 20 to 21 year ba,  aƙalla tasan zata fita da 3 year,  ita kanta yarinyar tayi mata kyau, domin kuwa tana da burgewa, kyawunta abayyane yake,  "Hmmm idan dai har Zaid zaina mafarkin samun irin wannan tauraruwar, me zaiyi da irina?" Afrah ta tambayi kanta a bayyane.

"Mekikeyi a tsaye anan kuma?"

Muryar Zaid yakaraÉ—e cikin kunnuwanta, da sauri tajuyo tana kallonsa, sam ita tama manta da cewa tare suke.

Kallonta yayi naɗan sakanni, kafun ya raɓa ta gefenta ya wuce.

Ƙirjin Dr.Sadeeq ne ya buga, alokacin dayaga gilmawan Zaid ta bayan Zahrah,  amma kuma da dukkan alamu shi Zaid ɗin bai lura dasu ba.

"Ya kamata mutafi ko princess, idan yaso saimu yi take away  ɗin naman mutafi dashi gida, sai ki ƙarasa ci acan" Dr.Sadeeq yafaɗa a ƙagauce.

"Um um nidai Hubby kabarni please,  nakusa nacinye fa" Zahrah tafaɗa a shagwaɓe.

Babu yanda ya iya, dole haka ya barta, taƙarasa cin namanta.

Tana kammalawa kuwa, yakama hanunta suka bar cikin hotel ɗin,   ba gida suka nufa direct ba, saida suka biya wajen saida ice cream yasaimata, kana suka ɗauƙo hanyar gida.

Gaba ɗaya jin zuciyarsa yake a jagule, "Meyakawo Zaid wannan hotel ɗin? Kodai bibiyan matarsa yake?" tambayar da Dr.Sadeeq ke tayiwa kansa acikin zuciyarsa kenan, amma bayida wanda zai basa amsoshin tambayoyinsa. (😂 Doctor fa yana tsoron Baba Zaid yasin)

Suna isowa bakin gate É—in gidannasu, me gadi ya wangale gate É—in Doctor yatura hancin motarsa ciki.

Tana ganin shigarsu cikin gidan, tasaki wani irin murmushi, tun fitowarsu a hotel É—in take biye dasu, acikin motarta, batare da tabari sun gane hakan ba.

"Zanyi muku zuwa na musamman"   tafaɗi haka a bayyane.  Haɗe dayin reverse ta juya akalar motarta  zuwa gida...

(Zanfara yi muku 1 read more, saboda banason  editing, wallahi wuya yake ban😥)

      *20/february/2020*

  *✔️OTE me on Wattpad*
        @fatymasardauna

#Love
#Romance.......
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

      *SHU'UMIN NAMIJI !!*

    *Written By*
Phatymasardauna

*Dedicated To My Brother KHABIER*

*🌈Kainuwa Writers Association*

_{United we stand and succeed; Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers }_

*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*

            *WATTPAD*
     @fatymasardauna

*Chapter 112*

Yana zaune acikin falon, taturo ƙofa tashigo bakinta ɗauke da sallama, cike da mamaki yake kallonta. "Bakije gidan Ƙawartaki bane?" ya tambayeta yana me tsareta da kyawawan idanunsa.

Murmushi tayi haɗe da ƙarasowa cikin falon, zama tayi gaf dashi, haɗe da ɗaukan hanunsa ta ɗaura akan cinyarta.   "Naje nasamu batanan, kuma dama banaso nabarka kai kaɗai agida, shiyasa na dawo" tafaɗi haka tana me ƙara faɗaɗa murmushinta.

Kansa yajinjina haɗe da ɗaukan goran ruwan dake  aje a gabansa, yakai bakinsa,  kallonsa take tanaso tafaɗa masa abun dake cikin ranta, amma kuma tsoro takeji saboda batasan taya zai ɗauki maganar ba.

Matsewa kawai tayi haɗe da sanya hanunta ta saƙalo hanunsa,  fuskarsa takafe da ido kana tace "Yau nahaɗu da Zahrah"
Da sauri ya É—ago kansa ya kalleta, cike da tsananin mamaki yace "Wace Zahrah?"

"Zahrah wacce kasani, wacce kuma tunaninta ke maƙale acikin zuciyarka, babu dare babu rana" ta bashi amsa.

"A ina kikasanta, har kikasan cewa itace Zahrah'n danake tunani akowani lokaci?" yajefomata tambaya yana me kafeta da idanunsa.

"Duk wanda yasanka dole zaisan Zahrah, mussamman ma ace wanda yake kusanci dakai, ko kamanta cewa har yanzu akwai hotonta acikin É—akinka?"

Miƙewa yayi daga zaunen dayake haɗe da cusa hannayensa cikin aljihun wandonsa.

"Zahrah É—aya na sani a rayuwata, kuma tajima da mutuwa, saboda haka ni bansan wata Zahrah ba" yanakaiwa nan azancensa yasakai yawuce cikin bedroom É—insa, ko waiwayenta baiyi ba.

Mamakine ya bayyana ƙarara akan fuskar Afrah, sakamakon jin kalaman Zaid da tayi,  "Dare safe rana, bashida wani aiki sai tunaninta, tasha jinsa yana kuka a toilet, dukkuma akan Zahrah ɗinne, amma wai kuma yau da bakinsa yake cewa Zahrah ta mutu, anya kuwa Zaid yana lafiya?" Afrah ke magana da zuciyarta.
Murmushi tayi asakamakon tunawa da wani abu da tayi, tashi tayi tanufi É—akin da Zaid yashiga.

Yana zaune agefen gadonsa hanunsa, riƙe da wani littafi da kuma biro,  da'alama nazartan littafin yake, amma kuma idanunsa cike suke da ƙwalla, yanajin motsin shigowar Afrah, yayi sauri ya rufe littafin, ransa a ɓace, ya juyo gareta.

"Mekikazo ɗauka? Bana faɗa miki cewa bakoda yaushe ne, nake da buƙatarki ba, please get out!" yaƙare maganar yana meyi mata nuni da ƙofar fita daga cikin ɗakin.

Ajiyar zuciya ta sauƙe haɗe da takowa zuwa garesa, tana zuwa gabansa ta durƙusa haɗe da zube guiwowinta a ƙasa.

"Kagafarceni idan abun dana faɗa maka akan Zahrah ya ɓata maka rai, banyi haka donna ɓata maka ba, saidai kuma zanfaɗa maka koda zaka tsaneni ne,  wallahi bazaka taɓa yin rayuwar farinciki ba, harsai kasamu Zahrah ka ƙara neman yafiyarta,  nasan cewa kana da buƙatar Zahrah akusa dakai, fiye da yanda kake da buƙatar ko wace mace a duniya,  amma kuma ƙaddara babu yanda bata juyawa bawa, dan Allah kayarda dani, akwai abunda zanyi wanda zaisa kusamu jituwa a tsakaninka da Zahrah, harma da mijinta"
Chapter 101 · 0% Book details