← Book details Shu'umin Namiji Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 63 OF 112

Sashe 63

Shu'umin Namiji Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Nayi kewarka Man, ashe de kaima kayi kewata? katafi ka barni da tunanin daɗin da kajiyar dani, wanda har rana me kamar ta yau babu wani ɗa namiji da yajiyar dani kwatan kwacin wannan" Meenal taƙare maganar cikin yanayi na shagwaɓa haɗe da sake matsowa tashige cikin jikinsa,, ɗan guntun murmushi yasakar mata haɗe da soma ƙarewa fuskarta kallo, Meenal kyakkyawar yarinyace wanda kyawun nata kuma yazama na ɗan maciji, domin kuwa Meenal tantiriyar ƴar iska ce kuma cikakkiyar mazinaciya wanda idan ta kafamawa namiji ƙahon zuƙa duk nuƙu nuƙunsa sai ta jefasa cikin raminta, sai dai idan kuma shiɗin ya kasance gwaska na gasken gasken, tofa nan ne zasu dai dai ta, kamar dai Zaid da ta buga ta rawa yaƙi faɗowa raminta, domin kuwa shi ɗin ma ɗan iskane me lasisi san nan kuma gwaska ne me zaman kansa, wannan yasa Meenal takasa turasa a cikin raminta..

Hanu Meenal tasanya akan faffaɗan ƙirjinsa tashiga shafawa haɗe da cusa kanta acikin wuyansa cike da ƙwarewa take manna masa kiss,, tamkar wata mayya haka take sake shigewa cikin jikinsa..

Lumshe idanunsa yayi haɗe da cusa hanunsa cikin sumar kanta,, take yasoma sauƙe ajiyar zuciya akai akai domin kuwa gani yake tamkar Zahrah ce kwance haka a jikinsa,, idanu Meenal ta kafesa dashi cike da mamakin irin sauyawan da yayi, nafarko ta hango tarin damuwa acikin idanunsa yayinda na biyu kuma ta hango wani abu mai ɗaure kai acikin idanunsa,,, "Man!" taƙira sunansa cikin wata irin murya, idanunsa kawai ya jefa acikin nata idanun batare da yace da'ita komai ba,, dama haka takeso burinta shine yaɗaga kyawawan idanunsa ya kalleta,, take ta sauya salon nata kallon ta marairaice idanunta,, fuskarta ta matso daf da tashi fuskar lokaci ɗaya tasoma ƙoƙarin haɗe bakinsu waje ɗaya, kamar koda yaushe ƙin aminta da hakan yayi da sauri ya kawar da kansa gefe, saboda hakan baya daga cikin tsarinsa haɗa miyau da matan bariki, domin babu abu mafi saurin sanya shaƙuwa kamar haɗakar yawun baki, sosai kiss yake sanya shaƙuwa a tsakanin masu yinsa, domin haɗuwar yawun bakuna biyu wani sinadari ne na musamman,,,, bata damu ba domin dama tasansa bayawa mace kiss batakuma san dalilinsa na hakan ba, wan nan kuma ita duk ba damuwarta bane matuƙar zai kusanceta to zatafi kowa farinciki,,,,, hanunta ta sanya akan mararsa tashiga shafawa a hankali haɗe da ɗaura bakinta akan nipples ɗinsa, jawota yasakeyi jikinsa bayan ya cire mata ƴar ƙaramar rigar jikinta, kansa ya cusa acikin ƙirjinta yana me shaƙar ƙamshin turarenta, haɗe da sanya hannayensa a bayanta yasoma shafawa a hankali,, take Meenal tasoma sauƙe numfashi akai akai dama ƙiris take jira saboda akunne take ƙwarai... Lokaci ɗaya Meenal tarikice wasu irin salo take gwadawa Zaid masu sanya mutum ya fita a hayyacinsa, yayinda shima yagama ruɗata da nasa salon har saida yakusa sanyata shiɗewa,, amma kuma wani abun mamakin shine yanayin hakan ne cikin wani irin yanayi wanda baisan dame zai ƙira sunan yanayin ba, kwata kwata baijin wani abu mai suna sha'awa a jikinsa duk dakuwa irin romancing ɗinsa da Meenal keyi, lumshe idanunsa yayi haɗe da jawota yadawo da ita ƙasansa aniyarsa shine ya kusanceta amma kuma sai yaji zuciyarsa tashiga bugawa da sauri sauri yayinda Zahrah tashigo cikin ransa ta tsaya cak, take idanunsa suka haskomasa irin kallon tsanan da tayi masa ɗazu, nan danan yaji komai yafice masa arai, da sauri ya ture Meenal gefe haɗe da sanya hanu ya dafe kansa da yayi masa nauyi, da wani irin kallo Meenal da takai ƙololuwa wajen sha'awa ta bisa, meye haka yakeyi? badai halin nasa na wulaƙanci zai gwada mata ba? idan kuwa hakane Zaid yacuceta, saida yagama jefata acikin masifaffiyar sha'awarsa san nan yajuya mata baya, hanu tasanya ta rungumosa ta baya haɗe da soma goga masa breast ɗinta akan bayansa "Meke damunka Man? kada kabari damuwa ya hanaka jin daɗin rayuwa please" tafaɗi haka cikin narkakkiyar murya, hanunsa yasanya ya zameta daga jikinsa wani irin haushinta ma yake ji, miƙewa yayi direct ya wuce toilet ɗinsa ko waiwayota baiyi ba, baki sake haka Meenal tabisa da kallo harya shige cikin toilet ɗin,, kuka ta fashe dashi haɗe da matse cinyoyinta, tsakani da Allah take kuka domin kuwa iyaka cuta a wajenta shine abun da Zaid yayi mata...

Zaid kuwa yanashiga bathroom ya zame wandon dake jikinsa haɗe da nufar inda babban bathtub ɗin wankansa yake, ruwa ne me kyau da tsabta acikin bathtub ɗin, amma duk da haka saida ya zubar yakuma taran wani ruwan, turaren wankansa me daɗin ƙamshi ya sanya a cikin ruwan haɗe da shiga cikin ruwan ya kwanta a hankali,, lumshe idanunsa yayi haɗi da jingina kansa, zafi yakeji adai dai saitin zuciyarsa, tabbas yanaji ajikinsa cewa akwai abun da zai faru dashi bayan wanda yake faruwa dashi yanzu, "wace irin soyayya ce haka yake yiwa Zahrah me zafi?" tambayar da kullum sai yayimawa kansa kenan, lallai yau yasake tabbatar mawa kansa cewa yazama mutum me rauni, A she dama akwai wata rana da zai iya kasancewa haka? yaƙira Meenal ne don taɗebemasa kewa yakuma samu ya rage tarin sha'awar dake damunsa, domin kuwa har wani ciwo yakeji mararsa nayi masa, amma kuma sai gashi ya kasayin komai da Meenal, ashe ba Meenal ɗin bace muradinsa Zahrah ce, haƙiƙa yasake yardarwa kansa cewa abunda kake so shi yake wahalceka sannan kuma yasake tabbatar mawa kansa cewa ƘAUNA guda ɗayane tal aduniya, SO ne kawai yake da yawa, amma ƙauna ƙaunace,, kafun yaƙira Meenal yayi tunanin cewa idan tazo zata gusar masa da damuwarsa, sai kuma bayan tazo yaga ashe bazata iya ba, ashe yin sex da shan giya basune maganin damuwarsa ba, Zahrah har lau itace maganin damuwar sa,, anya kuwa zai warke daga damuwar nan tasa?

Yajima acikin bathroom kafun yayi wanka yafito jikinsa sanye da farar rigar wanka,, kallonsa ya maida kan gado inda yabar Meenal don ganin wani hali ta ke ciki domin kuwa sarai yaji kukanta lokacin dayake cikin bathroom,, dariyane taso ƙwacemai sakamakon ganin Meenal da yayi takure a can ƙarshen gado tana bacci, yayinda ta cusa hanunta na hagu a ƙasanta, sarai yasan Meenal jarabebbiya ce yanzu haka fingering tayi don samawa kanta relief, abun da yafi tsana kenan wato mutum yayi amfani da kansa don biyan buƙatarsa, amma kuma wannan halin Meenal ne,, kai kawai ya girgiza haɗe da nufan gaban dressing mirror ɗinsa, vaseline yashafa ajikinsa kasancewar garin ana ɗan yanayi na sanyi, saida ya feshe jikinsa da body spray kafun yasanya kayansa riga da wando na jeans masu kauri, sosai kayan sukai masa kyau, kuɗaɗe yaciro a cikin drower ɗinsa ya ajiye a kusa da Meenal daketa sharan bacci, kana yayi ficewarsa daga ɗakin, direct bai zarce ko inaba sai compound ɗin gidan, yanzu kam shida kansa yakeson yayi tuƙi, don hakane ma yazaɓi BMW blue colour amatsayin wacce zai fita da ita....

Dr.Sadeeq

Duk yanda Dr.Sadeeq yaso samawa kansa nutsuwa hakan yagagara domin kuwa sam zuciyarsa bata amince da zuwa wajen Zahrah da Zaid keyi ba, duk da yau yafara ganinsa aƙofar gidan su Zahrah'n amma jikinsa ya basa cewa ba yaune zuwansa na farko ba, amma bakomai zaiyi maganin abunne zai nisanta Zahrah da Zaid nisantawa me tsanani kuwa, da wannan tunanin bacci ya ɗaukesa...

Washe Gari.

Dasassafe Zahrah ta shirya tayi tafiyarta makaranta sai dai a ranta tana mamakin rashin ƙiranta da Dr.Sadeeq yayi, rabonta dashi tunjiya da yamma sunkuma rabu dashi akan cewa zai ƙirata sai gashi kuma har zuwa yanzu bai ƙirata ba, uzuri tayi masa akan cewa ko aikine yayi masa yawa domin tasan hakanan Dr.Sadeeq bazaiƙi ƙiranta ba...

Tana tafiya ba jimawa motar Dr.Sadeeq ta tsaya a ƙofar gidan nasu, fitowa yayi daga cikin motar yasha adonsa cikin blue ɗin shadda sosai kuma yayi kyau,, yaro ya aika cikin gidan yace yace ana sallama,, bajimawa yaron daya aika yadawo ya shaida masa ance me gidan yana fitowa.... Washe da baki Baffa yaƙaraso wajen Dr.Sadeeq dake tsaye " Maraba da Likita, dama kaine ai da kashigo ciki amma ka tsaya a waje sai kace wani baƙo"

Murmushi Dr.Sadeeq yayi cike da girmamawa ya sunne kansa ƙasa haɗe da durƙusawa ya gaishe da Baffa,, fuska cike da fari'a Baffa ya amsa gaisuwan,,,

"Aikuwa kayi rashin sa'a domin kuwa mutumiyar taka bata jima da fita a gidan ba, tatafi makaranta ko karyawa bata tsaya tayi ba, amma ina ga zaifi kyau mushiga daga ciki ko"

"A'a Baffa nan É—in ma yayi, dama wajenka nazo ae"

"To to masha Allah, saimu zauna ae ko abisa dakalin nan" Baffa yaƙare maganar yana meyi mawa Dr.Sadeeq nuni da dakalin ƙofar gidan.

Duk yanda Baffa yaso Dr.Sadeeq ya hau kan dakalin su zauna ƙiyawa yayi, domin kuwa Baffa surikinsa ne baidace ace sun zauna gaf da juna ba kodan saboda kara da matuntawa,,

"Shikenan to tunda dae kaƙi zama, inajinka Allah yasa dai lafiya?"

Kansa yaɗan sosa haɗe da sakin murmushi "Lafiya ƙalau Baffa dama akan maganan aure nane da Zahrah..." sai kuma yayi shiru ya kasa ƙarasa maganar dake cikin bakinsa, gani yake tamkar idan yafaɗi maganar kai tsaye Baffa zaice masa yayi gaggawa ko kuma yace yayi rashin kunya...

"Ka kwantar da hankalinka Likita kafaÉ—i duk wani abu dake ranka" Baffa yafaÉ—i haka ga doctor É—in..

"Am dama...dama inaso ne kabani izini nasake turo magabatana dan sukawo sadaki san nan kuma a tsaida ranar aure"

"Alhmdlh to ai wannan abun farinciki ne Likita, wannan ae bawani abun damuwa bane, nabaka dama ka turosu aduk sanda kakeso, sai de kuma zakaɗanyi haƙuri, saboda zansa lokacin da ɗan tsayi saboda kasan ba a yin aure kai tsaye haka dole sai anɗanyi mawa yarinya sayayya, ina fata hakan bazai sosa ranka ba?"

Murmushin jin daɗi Dr.Sadeeq yayi haɗe da cewa "Naji daɗi sosai Baffa, amma kuma maganar sayayya basai kun wahalar da kanku ba, domin zuwa yanzu gidan da zamu zauna baya buƙatan komai, saboda haka don Allah kada kusa kanku a wahala"
Chapter 63 · 0% Book details