← Book details Auren Kwangila Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 97 OF 111

Sashe 97

Auren Kwangila Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Bin umarninta tayi ganin ba wasa a fuskarta ta wuce sumi sumi tabar kitchen din

Dafe kanta ummy tayi bayan fitarta tana mammakin irin wannan rashin kunyar ta 'ya'yan zamani

Yanzu su rasa inda zasu baje kolin iskancinsu sai a dakinta?

Dama tun dawowarshi gidan tana lure da take takenshi

Ko tsiramata idanun dayake a dining duk lokacin cin abinci tana sane shiyasa wani sa'in idan abun yaso yin yawa saita tashi tabarmasu dining din

Su ke abinsu amma ita ke jimasu kunyar

Jiya jiyan nan tazo ta taddasu zaune afalo qasa kamar su shige jikin juna saidai tajuya tafasa yin abinda ya sauko daita, daga baya ma saidai ta aika baby takirata ganin har isha'i na niyyaryi bata dawoba.

Hakan be isaba sai gashi the same day da daddare ganin har kusan 10 bata shigoba kamar yadda tasaba yasata fitowa ta leqa dakin baby taga wayam sai babyn kadai daketa sharar barcinta

Fitowa tayi tana wondering ina take

Ganin kwayakwan falo a kunne yasata Saukowa taga ko tana anan saidai me kafin ta qarasa ta hangosu manne dajuna a dining hakan yasata juyawa bashiri takoma inda tafito

Yanzu kuma wulaqancin nasu harya kai yanzu su rasa inda zasu baje kolin rashin kunyarsu sai a dakinta?

Kai gaskiya tana ganin rayuwa, dolene ma ta tarkatasu ta korasu kafin sujamata abin kunyar dayafi wannan

Wasa wasa tun tana tsumayen fitowarshi har abin yafara bata tsoro jin shirun yayi over

Jan stool tayi ta zauna ta zabga tagumi tana jiran taji koda motsin daya daga cikin su ne

Ita sai yanzu ma take danasanin riqe saudart, dama ummar sadeeq taja mata kunne akan haka tace tsakanin miji da mata sai Allah qarshenta tazo taji kunya gashi hakan kau yafaru

Ita wai nan riqeta tayi don ta garashi yasan muhinmmancin ta Ashe ja'irar 6ulamata qasa a ido zatayi

Aiko tunda abin hakane gwara suzo Susan inda dare yayi masu, bata iyawa

Jin qauri ya turnuke kitchen din yasata saurin tashi ta kashe gas cooker din tana bude tukunyar dake akai

Ganin abin ciki yafara kamu yasata jan tsaki ta dauko wurin kwashewa ta kwashe tana ayyana dolene ma suzo su kama gabansu bazasu maidata uwar banza ba

Tana cikin jiqa tukunyar datayi kamun a sink taji motsi abakin kofa

Waigowa tayi suka hada ido da ashraf da saika rantse da Allah ba shi ta kamaba ya saka Yar mutane a corner don yawani maze kamar babu abinda yafaru

Dauke kai tayi tacigaba da abinda take

Qarasowa ciki yana cewa
"Ummy yau ke ke breakfast din? Ina maid din?"

Bata ko dagoba tace
"Na aiketa" a gajarce

"Ayyah nashiga dakine naga ban gankiba shine nace bari nazonan Ashe kina ciki ma"

"Hmm" kawai tace don ita bawai son firar takeba ita in so samune ma yatafi yabata wuri

"Ummy to nidai zan wuce office munada aiyuka masu yawa baxan iya tsayawa yin break ba, nayi a office"

Cikin zuciyarta tace
"Jikayi nace katsaya dama?"

Amma a zahiri tace
"To Allah ya tsare, take care" batareda ta juyoba

Da amin ya amsa yafice yana mammakin wannan tsare gidan na ummy, watsar da tunanin yayi tinawa dayayi aidama haks take yan kwanakin nan dukdan saudart amma yasan maganinta Ai idan tasan wata Ai batasan wataba

Koda yafita saida ta jima sosai a kitchen din kafin tafito tayi shahadar komawa saman

Kamar yadda tazata bata taddataba dakin hakan yasa ta maido dakinta ta rufe tana sauke Ajiyar zuciya

Bin dakin tayi da kallo taganshi tsab tsab. Kada kanta tayi ta wuce toilet tana ayyana dolene ma su tattara subarmata gida😆

A bangaren saudart tana samu ashraf yafita tayi sauri ta ida gyara dakin, batajin tana iya hada ido da ummy dukda batasan meya faruba amma gani take data kalleta zata gano abinda yafaru, hakan yasa tana gamawa ta lalla6a tabar dakin takoma na baby

Ummy kau maid dinsu takira akan taje tasamu saudart dakinsu tayimata maganar breakfast don ahalin yanzu batajin zata iya facing dinta

Saudart kau bata kawo komai aranta ba ta sauka tayi break dinta abubbuwan dasuka faru dazun naqara dawomata a qwanya, dolene tadan ja dabaya da ashraf idan ba hakaba watarana kunya za'aji, yanzu ace dazu ummy tashigo ta gansu ahakan ina zatasa kanta? Dolene ta takamashi birki tunda taga kamar kunya be isheshiba (ruwa kike yarinya😒)

Yinin ranar ummy bata fitoba bare su hade, gwara gwara ma da baby tadawo sun shigo tareda saudart dakinta akan lunch sai cemasu tayi suje suci kawai she's busy

Ba wanda yakawo komai aranshi suka fita don zuwa suci, baby na bata labarin yadda exam din yau yayi zafi.

***

Zaune take a dakinta tana dudduba wasu kaya da za'a kawomata sari daga China aka bubbugo kofa

Saida tadanyi jimm sannan tabada izinin shigowa

Ashraf ne yashigo cikin shigarshi ta jallabiya ash colour da alama daga massallaci yake don dama ba'a dade da idarda isha'i ba

Kallo daya tayimashi ta dauke kai tana amsa sallamarshi

Qarasowa yayi ciki ya zauna qasa kusada qaffafunta yadora kanshi à cinyarta

Saurin ture kanshi tayi afusace tana cewa
"Meye haka?"

Shagwa6a fuska yayi kamar zaiyi kuka yace
"Kai ummy"

Tsaki taja tacigaba da abinda take

Kumbura fuska yayi yana hura hanci wai nan yayi fushi besan dama ciki take dashi ba

Tsaki tasake ja ta dago daga abinda take tace
"Kana jina? Jibi ka dauke matarka kabarmin gidana na gaji da ganinku fatan kajini dakyau? Jibi jibin nan kaji na gayamaka, tom" tafada tanajan kunnenta daya alamun yajita dakyau sannan tayi kwafa tacigaba da abinda take

Wara idanu ashraf yayi cikin tsagwaron mammakin kalamanta

"Ummy jibi?"

Cikeda masifa ta zaburomashi tace
"Eh jibin! Dan wlh karma ka kuskura kuwuce..."

Kasa ida maganar tayi jin ya qanqameta yana ihun murna

"Kai ummy amma Allah ya tsundumaki a aljannar fiddausi, insha Allah ga kofar gidanki gana annabi (s.a.w), Allah ya baki duk abinda kikeso, Allah ya hadaki kema da Abba a aljanna"

Wani dundu takai mashi abaya tana tureshi ajikinta
"Dan gidanku zoka fitarmin a daki, marar kunyar banza kawai"

Dariya yake yana Sosa baya inda tazuba mashi qulli yace
"Babu komai ummy, dukda haka Allah ya saka da alhairi ya kuma farantamaki yadda kika faranta Mani"

Pillow din gefenta ta dauka ta jefeshi dashi tana cewa
"Bazaka fitaba nace?"

Saurin ficewa yayi yana Dariya harda dafe ciki

Kwafa ummy tayi tana kada kai, can kuma tayi murmushi tana girgiza kai tana fadin Allah ya shirya

Shikau qasa ya sauka yana cigaba da kaka6a dariyarshi don har kwarewa yake tsabar Dariya

Aqasa suka hade da saudart datayo hanyar sama itada da baby

Tsayawa sukayi kallon ikon Allah ganin yadda yake dariyar kamar sabon kamu

Ganin saudart yasa ya tattakura ya fashe dawata dariyar yana nunata yana tafi

Sororo sukayi suna kallonshi suka kalli juna sannan suka qara maida kallonsu kanshi

Dakyar ya iya hadiye dariyarshi yace
"Congrat *MRS ASHRAF AUWAL*" saikuma yaqara fashewa da Dariya yana tafi yawucesu yana cewa
"Well play momma, well play"

Daga saudart har baby binshi da kallo sukayi baki bude har saida yafice daga falon sai a sannan suka kalli juna

Fashewa da wata mahaukaciyar Dariya baby tayi harda rintse idanu

Sororo saudart take kallonta itama tanajin gabanta na dan faduwa, kodai sun haukace ne?

Qarfin halin cewa
"Kekuma lafiya?" Tayi tana danja baya kartaji saukar bugu

Qara kecewa da Dariya baby tayi kafin tace
"Wlh mijinki ya haukace, Allah ya zare, shikenan Yaya ya zare"

Takuma fashewa dawata dariyar tanayin sama dagudu

Binta da kallo saudart tayi adan tsorace zuciyarta na ayyana mata kodai dagaske basuda lafiyar ne?

Ita bataga abin Dariya ba anan, shi ya sauko yana Dariya marar dalili itakuma tana Dariya wai ya haukace, idanma haukacewar yayi aiba Dariya ya kamaceta ba, kuka ya kamaceta.

Ta jima atsaye tana jujjuya abin aranta sannan ta fara hawan saman jiki a sanyaye

Asama kau dakin ummy baby tafada tana cigaba da dariyarta mai kamada ta mahaukata

Kafin ummy ta dago harta fado Kanta tana cigaba da dariyarta

Tureta ummy tayi tana cewa
"Lafiyar ki lau kuwa?"

Cikin Dariya baby tace
"Wlh ummy yanzu muka hadu da yaya qasa yana gagga6a Dariya kamar sabon kamu, wlh harda tafi" takuma fashewa dawata dariyar

Wani dogon tsaki ummy taja bayan tagama binta da kallon takaici

Kofa ta nunamata tana cewa get out

Ba musu ta tashi tafita tana cigaba da dariyarta

Saudart na zaune a dosane gefen gado tana tunane tunane tajiyo dariyar baby na tunkaro dakin

Saurin dago Kai tayi tana kallon kofar.

Shigowa tayi tana cigaba da dariyarta saidai yanzu tadan rage saboda cikinta daya fara amsawa

Bata ko kalli saudart ba ta fada kan gado tana qara dafe cikinta daya fara mata ciwo Dom Dariya

Itadai saudart na zaune tana kallon ikon Allah tana ayyana duk yadda akai baby bata rasa ingilmu akanta

Saida ta huta sannan ta tashi ta wuce toilet saudart tabita da kallo

Bata dade ba tafito daure da towel da alamu wanka tayi

Kallon saudart datayi zugum tana kallonta tayi tace
"Aunty ke ba yanzu zakiyi wankan ba?"

Ajiyar zuciya ta sauke tace
"A'a yanzu zanyi"

Daga haka ta tashi ta wuce itama toilet din tana qara mammakin abinda yasamesu

Koda tafito har baby tayi barci

Chanza kaya zuwa na barci tayi tazo ta kwanta gefen baby tana kallonta

Saida ta tottofamata addu'o'i sannan itama tayi addu'ar barci ta rintse idanu

Ta dade tana jujjuya abinda yafaru dazun kafin wani barci mai dadi yazo yayi awon gaba da ita...✍️

Ummin fasihu🧚🏻‍♀️

🤵🏻👰🏻AUREN KWANGILA🤵🏻👰🏻
(Contract marriage)

Story written by Ashaanty love💖

100

A bangaren ashraf kau he is super happy, shi bema wani lura da baby ba daya sauko qasa kodayake ga yadda yakeji alokacin koda ya gantan hakan ba zai hanashi bayyana farincikinshi ba.

Yau ummy ta sashi farincikin da be ta6a yiba arayuwarshi, haryanzu ganin abin yake kamar wasa

Koda yashiga dakinshi, saiti yayi kamar a wasan tsere ya falfala da gudu yayi wani qundunbala akan gado yana Dariya, jiyake kamar yayi hauka don farinciki.

Harya dauko wayarshi zai kira amininshi saikuma yayi tsaki ya jefar da wayar can gefen gado yakoma ya kwanta rigingine yana qiyasta yadda zasu shimfida sabuwar rayuwarsu su biyu a matsayin ma'aurata

Ranar dakyar barci yasaceshi can tsakiyar dare wanda ke cikeda da mafarkan saudart
Chapter 97 · 0% Book details