Sashe 73
Auren Kwangila Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Samun wuri mamy tayi a gefen gadon dakin ta zauna sannan ta nunama saudart dake tsaye gefenta alamun itama tazo ta zauna.
Babu musu ta tako ta zauna inda mamyn ta gwadamata ta zauna ta sauke kanta kasa.
Shiru ne yadan ratsa dakin kafin mamy ta kawar da shirun ta hanyar cewa
"Saudart..."
Dagowa saudart tayi ta kalleta batareda ta amsaba
"Gayamin gaskiya, meyasa kika amince da cigaba da zama da mijinki?" Ta tambayeta tana tsareta da idanu.
Dan murmushi saudart tasaki tana sauke idanunta sannan ta girgiza kai ahankali.
"Look, ba maganar kurame zakiyimin ba, ki bude baki kiyimin magana" inji mamy
"Babu komai mamy, kawai gani nayi hakan yafi, tunda allah yakawo fahimtar juna atsakani bekamata kuma mu butulcemashi ta wannan hanyar ba, afterall kowa nada laifi a wannan case din this will serve as a lesson to us" tafada vatareda ta yarda sun hada idanu da mamyn ba.
Shiru mamy tayi tana nazarinta don kwata kwata bata gamsu da dalilantaba
"Saudart kin amincene....saboda ni?" Ta tambayeta ahankali idanunta kafe a kanta.
Dagowa saudart tayi ta kalleta saidai kuma takasa cewa komai sai hawayen da ke qoqarin taruwa a idanunta.
Sadda kai tayi qasa tashiga girgiza kai ahankali alamun A'a
"Saudart look at me.. nace kin amincene ki cigaba da zama da wanda bakiso ne saboda ni?"
Bata kalletan ba sai amsa mata datayi asanyaye da
"Mamy nariga na fadamaki dalilina"
Kamo hannunta duka mamy tayi tana matsowa kusada ita sosai
"Then look into my eyes and say it" tafada tana kallonta
Kasa dagowan tayi sai hawayen dasuka silalo mata suka digomasu a hannu.
"Kenan saboda ni kika yarda?" Inji mamy asanyaye.
Kasa amsawa saudart tayi sai hawayen dasuke saukomata ahankali.
Tasan wannan ne karo dabiyu ta zata cuci kanta arayuwa, nafarko tayine saboda daddy, mahaifi kuma jajirttace akanta yanzu kuma saboda mahaifiyarta mai qaunar cigabanta.
Bazata iya jure ganin mamy cikin damuwa da 6acin rai ba bayan tasan tanada hanyar magancesu, bazata ta6a bari mamy taji kamar batada wani matsayi awajenta kamar yadda tafada kwanaki, tana iya sadaukar da farincikinta ga mutanen nan biyu muddin su zasu samu farincikin don tasan suma sun sadaukar da fiyeda hakan akanta.
Ta yarda zata cigaba da zama da ashraf ne don gujewa 6acin ran mamy, ta yarda ne don mamy ta daina tunanin batada matsayi a wajenta bane. She sacrifice her happiness for her and she's ready to do more sacrifices for her muddin hakan zai sata farinciki.
"Saudart why? Kinsan abinda kikayi kuwa? Kin yarda ki zauna da wanda bakiso na tsawon rayuwarki? Saboda me? Saboda nayi blunting ranan cikin fushi? You should have know i don't mean all i've said, 6acin rai ne kawai yasani fadin wadansu abubuwan amma shine zaki tafka kuskuren dakikayi a farko?"
Itadai shiru tayi sai hawayen da haryaunzu be bar gangarowa ba.
"To bazai yiwuba, indai saboda ni zakiyi zaman cutuwa to tun wuri a warware wannan abun, cos baxan iya jurar ganinki kina rayuwar qunci ba"
Sai a sannan ta dago kanta jin yadda mamy ke magana seriously.
"Mamy.." tafada ahankali saikuma tayi sniffing tasa hannu ta share fuskarta sannan tasake cewa
"Mamy duk ba wannan ba nake buqata ba yanzu, addu'arki nafi buqata, bamu saniba wataqila hakan shiyafi alhairi, na yarda da farko saboda daddy dukda banaso amma a sakamakon hakan daddy ya sake re-uniting da mutanenda zumuncinsu ya dade da watsewa, yanxu kuma na yarda saboda ke saboda farincikin ki nasan bazan ta6a danasaniba, insha allah alhairi zai biyo bayan wannan ma kamar koma fiyeda wancan. So mamy batin tada magana bata tasoba, addu'arki kawai zata zama gata agareni"
Kallonta kawai mamy keyi cikin tausayawa, tasan saudart diyace mai biyyaya tasan abinda ya faru ba laifinta bane maiyasa 6acin rai ya rufemata idanu ta gayamata irin magangganun data gayamata? Tasan bata qaunar 6acin ranta kuma kullum cikin taka tsantsan take don gudun 6acin ranta meyasa takasa tunawa da hakan alokacin?
Jawota tayi vatareda tace komaiba ta rungume.
Luff saudart tayi a kafadar mamy tanajin wani dumin dadi na ratsata wanda har hakan saida ya wanzar da murmushi a fuskarta.
"Allah yayimiki albarka saudatu, allah kema yabaki 'ya'ya masu biyayya masu gudun 6acin ranki wadanda zakiyi alfahari dasu duniya da lahira"
Qara lafewa saudart tayi jikinta cikin jindadin addu'ointa tana amsawa da amin
"Allah yasa hakan shizai fiyemaki alhairi allah yasa kici ribar haqurinki"
"Amin mamy na" inji saudart murmushi fall fuskarta.
Ahankali ahankali mamy kemata nasiha gameda haquri da zamantakewar aure tana nusar daita nauye nauyen dake kanta na haqqin abokin zamantakewar auren nata.
Itadai saudart batace komaiba sai lafewa datayi jikinta tana sauraronta magangganun kuma nasamun matsuggunni a can qasan zuciyarta.
Ta dauki lokaci mai tsayi tana mata nasiha da shawarwarru inganttatu wanda hakan yayi nasarar kashe jikin saudart murus.
Daga qarshe tace "yanzu meyasa kika dawo nan harda uwar trolley? Sokike baban naki yaga kamar ni na huremiki kunne?"
Murmushi saudart tayi tace
"To mamy dama waya huremin kunnen?"
Dunguremata kai mamy tayi tana tashi tsaye tace
"Oho dai nidai babu ruwana is better kizo ki koma"
"Mamy shifa yace inzo" tafada a shagwa6e
Ta6e baki mamy tayi ta bude kofa tana cewa
"Kanku dai akeji bari naje nasan yanzu wadancan lasfikokin zasu dawo daga islamiyya su kuma rikita gidan da hayaniyarsu" ta fice.
Ajiyar zuciya saudart ta sauke bayan fitar mamy takoma ta jingina da kan gado.
Sosai takejin wani irin dadi da nishadi a zuciyarta tasan muddin iyayen nata zasu cigaba dayimata addu'a to bazata ta6a ganin ba daidai ba a rayuwarta.
Komawa tayi ta kwanta tana hasaso yadda zamansu zai kaya da wanda bata ta6a jin ko digon sonshi a zuciyarta ba, saidai ta qudura a ranta koma menene bazata ta6a barin tsanarshi ya hanata neman aljannarta ba awajenshi, zatayimashi biyyaya bakin gwargwado don neman aljannarta amma bazata ta6a budemashi kofar zuciyarta ba bare sonshi yashiga.
Kusan tare Abba dasu Abdul suka dawo da marece, shima abba yayi mammakin ganinta kuma yaji dadi sosai dayaji tazo tayasu yan kwanaki ne.
Da daddare haka suka baje a falo sunata kwasan fira suna dariya wanda firar yau tafi ta kullum dadi saboda kasancewar saudart acikinsu, saudart nada baiwar da idan tana waje sai an gane kuma komin qanqantar lokacin dakukayi tareda ita idan ta tafi saita barku da kewarta, that's her vibe.
Sai da lokacin kwanciya yayi sannan kowa ya haqura akaje aka kwanta.
Tana komawa daki kuma suka dasa da daddy dake can cikin kewarta sai qorafi yakemata wai ta tafi ta barshi, saida barci yafara cin qarfinta sannan sukayi sallama ta kwanta.
💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖
Yau kwana uku kenan da dawowar saudart gidan mamy.
Zaune take kan kujera, kaffafunta a saman kujerar ta takure waje daya idanunta kafe da wani english novel dake hannunta mai taken *ice and fire*.
Ta shagala sosai a karatun novel din don sosai labarin ya qayatar daita don sai sakin murmushi take akai akai.
Ringing din wayarta ne ya katse mata karatun tasa hannu ta daukota batareda ta janye idanunta daga kan novel din ba.
Dagawa tayi ta kara a kunne batareda ta kalli screen din ba tayi sallama.
Lumshe idanu yayi a dayan 6angaren ya bude cikin wani irin yanayi sadda muryarta ta dakar mashi dodon kunne. Batareda yace komaiba.
Jin shiru yasata duba screen din taga baquwar number ce hakan yasata dan yamutse fuska ta maida wayar a kunnenta tace
"Hello?...hello?" Amma shiru ba amsa
"Mtcheew network problem" tafada tana katse kiran ta ajiye wayar tacigaba da karatunta.
Furzar da iska yayi daga bakinshi yana dan murmushi sannan yasake dailing din number.
Wani dogon tsaki taja wanda har saida su habeeb suka juyo daga kallon dasuke suna kallonta.
"Kema ki koma ciki mana ki daga wayar dama tayaya zakiji ana kallo?" Inji mamy da itama tana falon tana danna wayarta.
Miqewa tayi batace komaiba ta nufi sama tana daga kiran da harya kusan tsinkewa.
"Hello?..." tafada tana shigewa dakinta.
Shiru!
"Look nifa banjin komai, idan ansan baza'ayi magana ba adaina bugowa mana idan kuma network ne kindly send sms dukda banga alamun network dinne ba" tana kaiwa nan ta tsinke kiran ta maida wayar silent tanajan tsaki ta fada kan gado tana cigaba da karatunta.
Sauke wayar yayi daga kunnenshi yana murmushi jin ta tsinke wayar. Jin muryarta kadai ba qaramin nishadi yasashi ba.
Komawa yayi ya jingina da kujerar office dinshi yana kallon number tata wanda dakyar yasameta a wayar baby daya sace jiya da daddare.
Shiga yayi wurin saving din contact yayi saving din number da *other half* yana murmushi.
Bude kofar office din da'akayi yasashi dagowa ya kalli kofar still murmushi a fuskarshi.
Sadeeq ne yashigo looking so tired don kallo daya zakamashi kasan ya kwaso gajiya don tie dinshima a safsafce yake.
Dan hade rai A.A yayi yana kallonshi harya je wajen qaramin fridge din office din ya dauko ruwa mai shegen sanyi yadawo ya zauna ya 6alle murfin yashiga kwankwada.
Tsaki ashraf dake binshi da harara tundazu yayi yace
"Nifa na rasa gane kanka kwana biyun nan, saidai kazo office da safe bayan azahar you are nowhere to be found sai gab da za'a tashi sannan ka lalla6o kadawo, gidan uban wa kake zuwa on duty" yafada yana hararanshi.
Banza sadeeq yayi ya kyaleshi har saida yaga bayan ruwan sannan yayi cilli da goran yana komawa yana balancing akan kujerar dayake akai.
"Kutt.. wlh kaje ka dauke kasa a waste basket wannan wane irin wulaqanci ne?" Yafada yana ajiye wayar hannunshi.
"Mtcheew headache ne kai wlh" inji sadeeq yana tashi zaibar office din.
Saurin tashi ashraf shima yayi ya nufi inda yayimashi jifa da goran ya dauka yadawo ya cusamashi a hannu yace
"Tafi da abinka kuma kayi gaggawar rubutomin note akan inda kake zuwa yawon gantalinka na yan kwanakin nan ko kaga takardar sallama wlh"
Kya6e baki sadeeq yayi yanufi kofa hannunshi maqale da goran ruwan da ashraf ya cusamashi yana cewa "mad oo"
"Zakasan mad oo idan banga note dinba first thing tomorrow morning" inji ashraf yana kwafa.
Bude kofar yayi yafita yamaidota da karfi ya rufe.
Babu musu ta tako ta zauna inda mamyn ta gwadamata ta zauna ta sauke kanta kasa.
Shiru ne yadan ratsa dakin kafin mamy ta kawar da shirun ta hanyar cewa
"Saudart..."
Dagowa saudart tayi ta kalleta batareda ta amsaba
"Gayamin gaskiya, meyasa kika amince da cigaba da zama da mijinki?" Ta tambayeta tana tsareta da idanu.
Dan murmushi saudart tasaki tana sauke idanunta sannan ta girgiza kai ahankali.
"Look, ba maganar kurame zakiyimin ba, ki bude baki kiyimin magana" inji mamy
"Babu komai mamy, kawai gani nayi hakan yafi, tunda allah yakawo fahimtar juna atsakani bekamata kuma mu butulcemashi ta wannan hanyar ba, afterall kowa nada laifi a wannan case din this will serve as a lesson to us" tafada vatareda ta yarda sun hada idanu da mamyn ba.
Shiru mamy tayi tana nazarinta don kwata kwata bata gamsu da dalilantaba
"Saudart kin amincene....saboda ni?" Ta tambayeta ahankali idanunta kafe a kanta.
Dagowa saudart tayi ta kalleta saidai kuma takasa cewa komai sai hawayen da ke qoqarin taruwa a idanunta.
Sadda kai tayi qasa tashiga girgiza kai ahankali alamun A'a
"Saudart look at me.. nace kin amincene ki cigaba da zama da wanda bakiso ne saboda ni?"
Bata kalletan ba sai amsa mata datayi asanyaye da
"Mamy nariga na fadamaki dalilina"
Kamo hannunta duka mamy tayi tana matsowa kusada ita sosai
"Then look into my eyes and say it" tafada tana kallonta
Kasa dagowan tayi sai hawayen dasuka silalo mata suka digomasu a hannu.
"Kenan saboda ni kika yarda?" Inji mamy asanyaye.
Kasa amsawa saudart tayi sai hawayen dasuke saukomata ahankali.
Tasan wannan ne karo dabiyu ta zata cuci kanta arayuwa, nafarko tayine saboda daddy, mahaifi kuma jajirttace akanta yanzu kuma saboda mahaifiyarta mai qaunar cigabanta.
Bazata iya jure ganin mamy cikin damuwa da 6acin rai ba bayan tasan tanada hanyar magancesu, bazata ta6a bari mamy taji kamar batada wani matsayi awajenta kamar yadda tafada kwanaki, tana iya sadaukar da farincikinta ga mutanen nan biyu muddin su zasu samu farincikin don tasan suma sun sadaukar da fiyeda hakan akanta.
Ta yarda zata cigaba da zama da ashraf ne don gujewa 6acin ran mamy, ta yarda ne don mamy ta daina tunanin batada matsayi a wajenta bane. She sacrifice her happiness for her and she's ready to do more sacrifices for her muddin hakan zai sata farinciki.
"Saudart why? Kinsan abinda kikayi kuwa? Kin yarda ki zauna da wanda bakiso na tsawon rayuwarki? Saboda me? Saboda nayi blunting ranan cikin fushi? You should have know i don't mean all i've said, 6acin rai ne kawai yasani fadin wadansu abubuwan amma shine zaki tafka kuskuren dakikayi a farko?"
Itadai shiru tayi sai hawayen da haryaunzu be bar gangarowa ba.
"To bazai yiwuba, indai saboda ni zakiyi zaman cutuwa to tun wuri a warware wannan abun, cos baxan iya jurar ganinki kina rayuwar qunci ba"
Sai a sannan ta dago kanta jin yadda mamy ke magana seriously.
"Mamy.." tafada ahankali saikuma tayi sniffing tasa hannu ta share fuskarta sannan tasake cewa
"Mamy duk ba wannan ba nake buqata ba yanzu, addu'arki nafi buqata, bamu saniba wataqila hakan shiyafi alhairi, na yarda da farko saboda daddy dukda banaso amma a sakamakon hakan daddy ya sake re-uniting da mutanenda zumuncinsu ya dade da watsewa, yanxu kuma na yarda saboda ke saboda farincikin ki nasan bazan ta6a danasaniba, insha allah alhairi zai biyo bayan wannan ma kamar koma fiyeda wancan. So mamy batin tada magana bata tasoba, addu'arki kawai zata zama gata agareni"
Kallonta kawai mamy keyi cikin tausayawa, tasan saudart diyace mai biyyaya tasan abinda ya faru ba laifinta bane maiyasa 6acin rai ya rufemata idanu ta gayamata irin magangganun data gayamata? Tasan bata qaunar 6acin ranta kuma kullum cikin taka tsantsan take don gudun 6acin ranta meyasa takasa tunawa da hakan alokacin?
Jawota tayi vatareda tace komaiba ta rungume.
Luff saudart tayi a kafadar mamy tanajin wani dumin dadi na ratsata wanda har hakan saida ya wanzar da murmushi a fuskarta.
"Allah yayimiki albarka saudatu, allah kema yabaki 'ya'ya masu biyayya masu gudun 6acin ranki wadanda zakiyi alfahari dasu duniya da lahira"
Qara lafewa saudart tayi jikinta cikin jindadin addu'ointa tana amsawa da amin
"Allah yasa hakan shizai fiyemaki alhairi allah yasa kici ribar haqurinki"
"Amin mamy na" inji saudart murmushi fall fuskarta.
Ahankali ahankali mamy kemata nasiha gameda haquri da zamantakewar aure tana nusar daita nauye nauyen dake kanta na haqqin abokin zamantakewar auren nata.
Itadai saudart batace komaiba sai lafewa datayi jikinta tana sauraronta magangganun kuma nasamun matsuggunni a can qasan zuciyarta.
Ta dauki lokaci mai tsayi tana mata nasiha da shawarwarru inganttatu wanda hakan yayi nasarar kashe jikin saudart murus.
Daga qarshe tace "yanzu meyasa kika dawo nan harda uwar trolley? Sokike baban naki yaga kamar ni na huremiki kunne?"
Murmushi saudart tayi tace
"To mamy dama waya huremin kunnen?"
Dunguremata kai mamy tayi tana tashi tsaye tace
"Oho dai nidai babu ruwana is better kizo ki koma"
"Mamy shifa yace inzo" tafada a shagwa6e
Ta6e baki mamy tayi ta bude kofa tana cewa
"Kanku dai akeji bari naje nasan yanzu wadancan lasfikokin zasu dawo daga islamiyya su kuma rikita gidan da hayaniyarsu" ta fice.
Ajiyar zuciya saudart ta sauke bayan fitar mamy takoma ta jingina da kan gado.
Sosai takejin wani irin dadi da nishadi a zuciyarta tasan muddin iyayen nata zasu cigaba dayimata addu'a to bazata ta6a ganin ba daidai ba a rayuwarta.
Komawa tayi ta kwanta tana hasaso yadda zamansu zai kaya da wanda bata ta6a jin ko digon sonshi a zuciyarta ba, saidai ta qudura a ranta koma menene bazata ta6a barin tsanarshi ya hanata neman aljannarta ba awajenshi, zatayimashi biyyaya bakin gwargwado don neman aljannarta amma bazata ta6a budemashi kofar zuciyarta ba bare sonshi yashiga.
Kusan tare Abba dasu Abdul suka dawo da marece, shima abba yayi mammakin ganinta kuma yaji dadi sosai dayaji tazo tayasu yan kwanaki ne.
Da daddare haka suka baje a falo sunata kwasan fira suna dariya wanda firar yau tafi ta kullum dadi saboda kasancewar saudart acikinsu, saudart nada baiwar da idan tana waje sai an gane kuma komin qanqantar lokacin dakukayi tareda ita idan ta tafi saita barku da kewarta, that's her vibe.
Sai da lokacin kwanciya yayi sannan kowa ya haqura akaje aka kwanta.
Tana komawa daki kuma suka dasa da daddy dake can cikin kewarta sai qorafi yakemata wai ta tafi ta barshi, saida barci yafara cin qarfinta sannan sukayi sallama ta kwanta.
💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖
Yau kwana uku kenan da dawowar saudart gidan mamy.
Zaune take kan kujera, kaffafunta a saman kujerar ta takure waje daya idanunta kafe da wani english novel dake hannunta mai taken *ice and fire*.
Ta shagala sosai a karatun novel din don sosai labarin ya qayatar daita don sai sakin murmushi take akai akai.
Ringing din wayarta ne ya katse mata karatun tasa hannu ta daukota batareda ta janye idanunta daga kan novel din ba.
Dagawa tayi ta kara a kunne batareda ta kalli screen din ba tayi sallama.
Lumshe idanu yayi a dayan 6angaren ya bude cikin wani irin yanayi sadda muryarta ta dakar mashi dodon kunne. Batareda yace komaiba.
Jin shiru yasata duba screen din taga baquwar number ce hakan yasata dan yamutse fuska ta maida wayar a kunnenta tace
"Hello?...hello?" Amma shiru ba amsa
"Mtcheew network problem" tafada tana katse kiran ta ajiye wayar tacigaba da karatunta.
Furzar da iska yayi daga bakinshi yana dan murmushi sannan yasake dailing din number.
Wani dogon tsaki taja wanda har saida su habeeb suka juyo daga kallon dasuke suna kallonta.
"Kema ki koma ciki mana ki daga wayar dama tayaya zakiji ana kallo?" Inji mamy da itama tana falon tana danna wayarta.
Miqewa tayi batace komaiba ta nufi sama tana daga kiran da harya kusan tsinkewa.
"Hello?..." tafada tana shigewa dakinta.
Shiru!
"Look nifa banjin komai, idan ansan baza'ayi magana ba adaina bugowa mana idan kuma network ne kindly send sms dukda banga alamun network dinne ba" tana kaiwa nan ta tsinke kiran ta maida wayar silent tanajan tsaki ta fada kan gado tana cigaba da karatunta.
Sauke wayar yayi daga kunnenshi yana murmushi jin ta tsinke wayar. Jin muryarta kadai ba qaramin nishadi yasashi ba.
Komawa yayi ya jingina da kujerar office dinshi yana kallon number tata wanda dakyar yasameta a wayar baby daya sace jiya da daddare.
Shiga yayi wurin saving din contact yayi saving din number da *other half* yana murmushi.
Bude kofar office din da'akayi yasashi dagowa ya kalli kofar still murmushi a fuskarshi.
Sadeeq ne yashigo looking so tired don kallo daya zakamashi kasan ya kwaso gajiya don tie dinshima a safsafce yake.
Dan hade rai A.A yayi yana kallonshi harya je wajen qaramin fridge din office din ya dauko ruwa mai shegen sanyi yadawo ya zauna ya 6alle murfin yashiga kwankwada.
Tsaki ashraf dake binshi da harara tundazu yayi yace
"Nifa na rasa gane kanka kwana biyun nan, saidai kazo office da safe bayan azahar you are nowhere to be found sai gab da za'a tashi sannan ka lalla6o kadawo, gidan uban wa kake zuwa on duty" yafada yana hararanshi.
Banza sadeeq yayi ya kyaleshi har saida yaga bayan ruwan sannan yayi cilli da goran yana komawa yana balancing akan kujerar dayake akai.
"Kutt.. wlh kaje ka dauke kasa a waste basket wannan wane irin wulaqanci ne?" Yafada yana ajiye wayar hannunshi.
"Mtcheew headache ne kai wlh" inji sadeeq yana tashi zaibar office din.
Saurin tashi ashraf shima yayi ya nufi inda yayimashi jifa da goran ya dauka yadawo ya cusamashi a hannu yace
"Tafi da abinka kuma kayi gaggawar rubutomin note akan inda kake zuwa yawon gantalinka na yan kwanakin nan ko kaga takardar sallama wlh"
Kya6e baki sadeeq yayi yanufi kofa hannunshi maqale da goran ruwan da ashraf ya cusamashi yana cewa "mad oo"
"Zakasan mad oo idan banga note dinba first thing tomorrow morning" inji ashraf yana kwafa.
Bude kofar yayi yafita yamaidota da karfi ya rufe.