← Book details Auren Kwangila Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 47 OF 111

Sashe 47

Auren Kwangila Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Karka damu shi wannan din is my backbone, idan bashi bani, kome kafada Mani kamar shi ka fadamawa, so feel free to say anything... Besides banga abun long story ba anan, wannan magana ce na signing da divorce, banga abun tsayawa na wasting din lokaci ba, as you can see munada ayyuka dayawa gabanmu Wanda zamuyi attending, can we please proceed with the signing Mr A.A?" Tafada tana jin kamar tayi exploding dan haushi

Shiru office din yasake dauka, Shidai sadeeq na gefe yana kallon ikon Allah, bashida tacewa don haka nashi idanu.

Dora hannayenshi yayi akan table din yadanyi leaning forward sannan yace

"Yes miss, nima banaso na 6atamiki precious time dinki nima na 6ata nawa, all I ask is five minutes of your time and mine, minti biyar kacal then komai saiya wakana"

"Wai minti biyar din me? Wace magana ce dole saimun ke6e?..."

Katseta yayi dacewa

"Look miss, wannan office ne ba kasuwa ba ok? Don't dare shout on me, wata hudu dasuka wuce, ke daya kikazo signing din contract din, daga ni sai ke, that's the same procedure we gonna take, five minutes kawai na tambaya and after that sai ayi koma menene" yafada shima cikin fada dukda wata zuciyar na kwa6arshi akan ba tahaka yakamata yabiba amma girman kanshi yahanashi sauraronta.

Saudart iya quluwa ta qulu, bude baki tayi zatayi magana daddy ya damke hannunta Wanda hakan yasata yin shiru ta juyo tana kallonshi.

Daga mata Kai yayi ahankali alamun ta amince kawai sannan ya maida kallonshi ga Ashraf dake masu wani kallo mai wuyar fassaruwa yace

"Five minutes ko? Ok munbaka, muda muka jira kusan five months, five minutes bazai bada matsala ba"

Yana kaiwa nan yamiqe tsaye ahankali sannan ya kalli saudart da kallo daya zakamata ka fuskanci ranta beso wannan hukuncin ba, yadan yimata murmushi sannan yafita.

Binshi dawani disgusting kallo Ashraf yayi harya fita don ya tsaneshi fiyeda yadda kuke tsammani, a duniya bayajin akwai Wanda ya tsana sama da wannan mutumin.

Sadeeq ma bejira komai ba ya nufi kofar fita yana addu'ar daidaito atsakaninsu, qasan zuciyarshi kuma fall take da takaicin ashraf, ya rasa irin taurin kanshi, shi a tunaninshi kwantar dakai zaiyi yabasu haquri asamu a warware komai amma gani yayi ma wani sabon wulaqanci ya tsiro dashi da girman Kai

Can gefen Alhaji ya zauna yana Satan kallonshi cikin zuciyarshi yana cewa
"Albasa batayi halin ruwaba"

**********************************************

Shiru office din yasake dauka, babu Wanda keda niyyar magana acikin su.

Ba yau suka fara ke6ancewa su biyu awaje dayaba amma yau yanayin dasukeji yasha banban Dana da.

Duk sai suka zama speechless, babu mai ko motsi atsakaninsu.

Sun kusan cinye mintuna biyu ahakan sannan Ashraf ya sauke ajiyar zuciya mai sauti Wanda hakan yasa tadan dago ta kalleshi, sai gani tayi yasa hannu ya dauki bundle daya cikin kudaden yana dan jujjuyawa a hannunshi.

Dagowa yayi ya kalleta still yana jujjuya kudin a hannunshi itakau ta kauda idanunta tana jinta duk a takure

"Sun cika?" Yafada still idanunshi kanta

"Ka qilga" ta amsa ataqaice without looking at him

Murmushin gefen baki yayi Wanda shi kadai yasan yayi abunshi yana maida kudin cikin sauran sannan ya kama zip din jakkar ya zuge

"Why the sudden change? Meyasa baki gayaman ba" Ya tambayeta yana maido dubanshi akanta.

Kallon Rashin fahimta tayi mashi Wanda shima besan tanayi ba saboda glass dinta daya kare idanun.

"I said why? You should have tell me" yafada calmly

"Tell you? Meyasa saina gayamaka?" Tafada tana mashi wani kallo

Ajiyar zuciya yasaki sannan yace

"Ok..ok..firstly inason yimiki godiya akan abinda kikayi mana, that shows you're loyal"

Mere baki tayi tana yatsina fuska

"Me kenan? I don't get you"

Murmushin gefen bakin yasakeyi sannan yace

"Kin taimaki al'umma da dama, da wadanda sukayimawa a farko damu dama wadanda zasu sake yimawa nan gaba da asirinsu be tonuba, thank you"

Ta6e baki taqara yi don ita bata wannan takeba

"It ok, besides ni don Allah nayi badon ayi appreciating dina ba, now back to business" tafada cikin qosawa da maganganun shi

Tsayawa yayi yana kallonta yana tunanin dama har haka ta tsaneshi? A qagare take ma ya sawwaqe mata don alamu sun nuna a matse take, zaman nan ma da maganar dasukeyi kamar an matsamata ne, kallo daya zaka yimata ka hango qiyayyar datake mashi Wanda hakan yaqara sagemashi gwiwa.

Jiyake kamar ya zube agabanta yaita bata hqr har ta haqura su zauna tare cikin aminci da soyayya, amma bazai iyaba, kar Allah ya gwada mashi ranarda zai zube gaban mace yana bata hqr, bazai ma ita misalta kanshi a wannan yanayin ba.

"Ok.. Back to business" yafada yana komawa ya jingina da kujerarshi yana kallonta

"Now me kikeso?" Ya tambaya yana bin kyakyawar fuskarta da kallo kamar yasamu mirror

"Me nakeso? Kafini sanin abinda nakeso" tafada cikin 6acin rai ganin kamar Neman raina mata hankali yake

"A tunani na zaku bari harsai mun cika 6months sannan mu warware komai, don't forget yanzu dududu watannin mu uku da auren, me kike tunanin duniya zata fada akanmu" yafada shima yana mammakin kanshi na maganar dayayi

Kallon mammaki saudart ta tsaya tana mashi

"Me duniya zatace? Ina ruwana da abinda zatace? It's my life Mr"

"Yes, it's your life, babu Wanda zaiyi questioning dinki amma mamy fa? Me zaki cemata idan kin koma gida bayan watanni uku a matsayin bazawara?"

Sosai maganar ta daki saudart har saida hakan yanuna a yanayinta.

Ganin hakan yasashi dorawa da

"Yes in so samune murabu din kowa ya kama gabanshi kowama yahuta, amma me zaki gayama mamy? Don't forget batasan komaiba gameda wannan auren ba, ya zataji idan labari ya risketa na kinfito bayan watanni uku da auren ki? Wane dalili zaki fadamata ya rabamu?" Yafada yana kallon yadda yanayinta ke qara chanza wa.

"D..don't worry, nasan me zan gayamata, wannan ba damuwarka bace" tafada trying to be firm

"Me zaki fadamata? Cewa dama auren contract ne auren mu?"

"Wannan be shafeka ba, uwatace ba takaba, babu abinda yashafeka"

"Nikau ya shafa miss, mezan fadawa Ummy idan muka rabu? Mezance shine silar rabuwarmu?" Yafada trying to convince her

"Look mubar wannan maganar, contract ne ya hadamu, kuma shi zai rabamu, babu ruwan wani da abinda zai fada don gamsar da mahaifiyarshi, besides aure nawa akayi? Normal aure, amma basuyi three months dinba auren ya rabu? Mutuwar auren mu a yanzu ba wani Abu bane it's normal, kana iya gayamata duk abinda kaga dama, I don't care" tafada firmly

Sa halshe yayi ya kashi qasan le66enshi ya tsaya yana kallonta ganin tarkonshi besamu danuwa ba

"Amma kinsan mutuwar aure saida dalili? Wani dalili zan bayar na rabuwa dake?"

"Dalili? Dama saida wani dalilin, atunanina kafi kowa sanin dalilin haduwarmu shi zai zama silar rabamu"

"Amma wannan ba hujja bace dazamu rabuba haka kawai, dole sai an samu kwakwarar dalili"

Tsayawa tayi sororo tana kallonshi

"What are you driving at wai?" Ta tambaya tana kallonshi unbelieving

Jan kujerar shi yayi dabaya sannan yamiqe tsaye ya nufi window din office din da labulen ke bude ya tsaya yana kallon waje hannunshi a aljihu itakau sai binshi da idanu take

"Dukda auren mu ba normal aure bane, auren yarjejeniya ne, hakan be hana asashi a jerin aure saboda shima shafamashi fatiha akayi kuma igiyoyin nan uku akwai su tsakanin mu, dan haka shima aurene kuma yana cikin auren da Allah yafada cikin *suratul thalaq*

Inda Allah (swt) yayi hani da saki batareda da qwaqwaran hujjaba, bayyananniya.

Saki yana daya daga cikin abinda Allah beso, Wanda awata ruwayarma cewa ake idan aure yarabu, al'arshi girgiza take saboda girman abun koda kuwa akwai kwakwaran dalili bare wannan Wanda bekai hujjar dazamu fake daita ba mu sa6ama mahallicinmu, idan mukayi hakan me zamu cewa mahallicinmu? Dame zamu kare kanmu?"

Saudart datayi mutuwar zaune tunda yafara magana kasa cewa komai tayi.

Wai meke shirin faruwa ne? Meya kawo wannan maganar kuma? A tunaninta izuwa yanzu sunmance da sun wuce wurin amma sai bullowa yake da abubuwa daban daban

"Look A.A ko mema kake? Meya kawo duk wannan wa'azin? Ohh dama duk kasan da wannan ka fara qirqiro maganar auren tun farko? Inajin kai ka faro komai ba wanibs, ina ilimin, ina sanin a lokacin? Koko sai daga baya duk kasan wadannan?

You force me into this marriage kuma yanzu kafara gayamin story? No way! Bazan ta6a zama dakaiba a matsayin miji, are you not ashamed? Just listen to yourself, bazai ta6a yiwuwa ba kanaji? I can't even stand you, bana jure zama na tsayin lokaci wuri daya dakai, shine kakemin maganar zaman aure, are you kidding me? Look Gwara kabar wannan kwalo kwalon naka and face the reality, this is just business and zai qarene a business! So wa'azinka bazai qareni da komaiba, ka Adana abinka zaifi yimaka amfani mallam" tafada cikin huci

Juyowa yayi yana kallonta tunda tafara har takai aya,

Takowa yayi cikin takunshi harya iso gabanta inda take zaune yana kallonta

"And who told you nima sonike na cigaba da zama dake din, I have no option ne, abinda nasani shine bazan qara tafka sa6oba kamar yadda nayi a bayaba, bazan sakeki batareda wata qwaqwarar hujjaba, final!"

Miqewa tsaye saudart tayi ba shiri
"What!" Tafada tana zare tabarau dinta, jikinta har rawa rawa yake saboda tashin hankali

"Look are you ok? What did you mean by bazaka sakeni ba? Me kake nufi? Na zauna da Wanda duk duniya babu Wanda natsana kamarshi? No way!" Tafada cikin qaraji, tashin hankali qarara a fuskar

Kalmar tsanar data ambata ba qaramin dukanshi tayi ba hakan yasa ya dago idanunshi dasuka fara chanza launi shima ya zubamata

"Nikuma bazan sakekiba! No way!" Yafada cikin 6acin rai

Kallo tabishi dashi na yan daqiqu sannan tasaki wata bushashiyar dariya Wanda daga ji iyakarta fatar bakin

"Wlh kayi kadan Ashraf, baka isaba, dolene ka sakeni! Saika sakeni wlh!"

"Nikuma bazan sakekiba! Aure yanzu aka farashi, sai kisani sakinki din!" Shima yafada a tsawace

"I hate you! You brat! I hate you!!" Tafada cikin qaraji hawaye na 6alle mata.

sai kuma tafara daukar files files din table din tana jifanshi dasu kamar sabuwar kamu tana nannata I hate you din cikin kuka sosai.
Chapter 47 · 0% Book details