← Book details Auren Kwangila Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 55 OF 111

Sashe 55

Auren Kwangila Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Ai fadi ma 6ata baki, she really need to learn the lesson of her life, tashi mutafi"

Jiki asanyaye ashraf yatashi, besan yadda zekuma qara facing din ummy bayan yagama sanin kallon datake mashi.

*************************************

Zaune suke gabanta qasan rug kamar dai jiya kowanne kanshi sunkuye.

"Ina kiranka baka dagaba" inji ummy tana kallon Ashraf daya kasa hada idanu da ita

"Am..sorry, na..barota a mota ne" yafada kanshi still a qasa

"Wacece wannan?" Tafada tana turomashi wani pics gabanshi.

Dagowa yadanyi yana kallon pics din.

Hotonshi ne da suzy tadan shige mashi ajiki tana dariya shikuma yadanyi murmushi

Bazai manta ranar dasukayi hoton ba, ranar suna school ba'a dade da gama sheqa ruwan sama ba, garin yayi shar mutane sun fito waje sai daukar pics suke.

Saukowa shima yayi hannunshi riqeda wani qaton littafi shima yatsaya yana kallon students din

"My.." yaji an kwala mashi kira abaya.

ko be juyoba yasan itace

Qarasowa tayi gabanshi tana haki, binta yayi da kallo yadda kayan jikinta suka dan jiqe gashi tawani tsuqe cikin jumpsuit (biri da wando) babu ko mayafi sai yar hular datasa akai.

"Please muma muyi hoton..please" tafada zata riqe hannunshi.

Dan zamewa yayi yana harararta

"Look at you, wai bakijin sanyi ne kam?" Ya tambaya yana binta da kallo cikin kishi

Itama kallon kanta tayi sannan ta kwa6e fuska

"Am sorry zan chanza yanzu, please mu dauka ko dayane"

"No" yafada firmly yana juyawa zai tafi.

Bunshi tayi tafara mishi magiyar ya bari ko dayane suyi, ganin bazata barshiba yasashi hqr ta tsaya ta fiddo wayarta ta matso jikinshi kadan, bece mata komaiba don aqagare yake tayi din yatafi.

"Please kayi murmushi mana wannan hade ran dukna menene?" Tafada a shagwa6e

Tsaki yaja sannan yadanyi yaqe ta daukesu sannan yadan tureta daga jikinshi yana cewa
"Ai shikenan ko? Am going to the library, see yah" yajuya yatafi.

"Nace wacece wannan?" Muryar ummy tasake maidoshi daga duniyar tunanin daya lula.

Ajiyar zuciya yasaki sannan ya bude bakinshi dakyar

"Tsohuwar budurwa ta ce"

Shiru dakin ya sake dauka.

Rintse idanunshi yayi snnan yacigaba dacewa

"A school muka hadu kuma muka fara soyyaya... saidai tafiyarmu batayi wani nisaba muka rabu don kwata kwata batada kamun kai, ga shigar datakeyi anyhow dukda ina nuna mata rashin dacewar haka amma bata dauka..."

Shiru yasakeyi idanunshi still rintse yana sauraron bugun zuciyarshi.

"Mun..mun rabune ranar dana..."

Shiru yasakeyi hoton yadda ya taddata suna musayar hot kiss dawani qaton arne a wani class na dawomashi a qwanya.

"Sadda na.. naganta dawani suna.." sai yayi shiru yakasa idawa.

Ummy kallonshi take tunda yafara magana kuma haryanzu bata daina kallonshi ba

"Ummy na rantse ban ta6a zina ba, ko zanyi bazanyi da qazamiyar yarinyarnan ba, bansaniba.. bansan abinda aka fadamaki kenan ba, yes aurenmu da Saudart AUREN KWANGILA ne amma babu wata yarjejeniya makamanciyar wadda ta fadamaki a tsakaninmu da saudart, she's innocent.. hasalima..bada son ranta akayi auren ba, believe me ummy.. kinfi kowa sanin halin danki..."
Ya qarashe maganar muryarshi nadan rawa rawa.

"Ummy suzy shaidaniyace, sharri ta qullamasu saboda daga baya tadawoma ashraf yaqi sauraronta shiyasa ta buyomashi ta wannan hanyar, ummy ni aminin ashraf ne tare muke akoda yaushe, ko alokacin dasuke soyyayar ban ta6a ganin ya riqe koda dan qaramin yatsanta ba, hasalima bawani sonta yakeba duk ita taita cusa kanta gareshi" inji sadeeq

"Hakane ummy, nima nasan suzy farin sani, qawayenta kawai zaki kalla kisan ko ita wacece, tasha cusa kanta gareni don tasamu shiga awajen yaya akaro na biyu, tasha tazo taita rarrashina akan nabata number yaya amma naqiya, ga sa bikin su yayama saida suka fito qarara suka nuna baqincikinsu, magangannu kala2 babu wanda basu fadaba, ummy ko rantsuwa nayi bazanyi kaffaraba suzy qarya tashiryama yaya do n tasamu a liqamashi ita" inji baby itama fuskarta bayyane da 6acin rai.

Shiru dakin yasake dauka, kan ashraf haryanzu aqasa zuciyarshi na bugawa yanason jin wane hukunci ummy zata yanke.

Ajiyar zuciya ummy tasauke mai sauti sannan tace
"Kalleni Ashraf"

Shiru yayi yakasa dagowa, bejin zai iya dagowa su hada ido daita, wani irin nauyinta yakeji

"Nace ka kalleni"

Ahankali yadago ya kalleta saikuma yayi saurin kauda kai ganin ta kafeshi da ido.

"Nasani, nasan qarya take kuma sharri takemuku tun alokacin datake maganar, nasan cikinku babu wanda zai iya aikata abinda tace kun aikata, nidama ban zargeka ba ban kuma zargi daughter ba cos I trust you both"

Ajiyar zuciya ashraf yasauke mai sauti yanajin kamar ana lifting din wani qaton dutse a qirjinshi.

"Wacece saudart? Meya hadaku? Meye silar wannan auren naku na contract?"

Tambayar ummy tasauka a dodon kunnensu.

Kowannensu shiru yayi zuciyarsu na bugawa.

"Magana nike" tafada tana binsu da kallo.

"Ummy.."

"Shhhh.. barshi yayi magana, dashi nake ba kai ba, ka gayamin komai ashraf karka saki ka 6oyemin komai" tafada tana kallonshi.

Shiru falon yasake dauka, sai motsi yake da baki amma yakasa magana, yarasa ta inama zai fara.

"Saudart diyace ga SHAMSU KANKIYA...Tsohon aminin Abbu" yafada yana lumshe idanu.

Ware idanu Ummy tayi tana kallon Ashraf unbelievably

Bakinta na rawa tace "Shamsu qolo?"

Kada kai yayi zuciyarshi na suya.

"Nafara ganin appointment letter dinshi ne wattanin baya dasuka wuce, akan yanason rance don farfado da company dinshi dake neman collapsing... ina ganin sunan naga tabbas kamar nasanshi wani wuri, hakan yasa babi diddigin qundinshi ta internet anan naga shidinne bawani ba... nan take tsohon raunin dayaimana a zuciya ya motsa naji na tsaneshi fiyeda yadda na tsaneshi da, dafarko sai naso qin taimaka mashi amma sai wata idea ta fadomin, mezai hana inyi ramuwar gayya nima in dandana mashi abunda ya dandana mana?

Saina amsa buqatarshi nabashi ranar dazamu hadu sannan nakoma naita bin diddiginshi daga kan iyalanshi zuwa abokan aikinshi dakuma abinda ya tara da abinda ake binshi bashi.

Saura kwana daya mu hadu na gayawa sadeeq plan dina, dafarko yaso hanani yacemin inbarshi da allah kawai mai yiwuwa sakkayar allah ce yake gani tun yanzu amma sainaqi saurararshi don alokacin *WUTAR FANSA🔥*(littafina ba gaba insha allah) ke ruruwa azuciyata, na nunamashi bansan zancenba acewata don indauki fansa yasa allah yaturoshi wajena..dakyar nayi convincing din sadeeq ya amince min shima.

Ranar farkon dayazo...."

Nan yashiga bata labarin zuwan Alhaji shamsu nafarko company dinshi da yadda suka kaya sai kuma zuwanshi da biyu da yadda ya gabatarmashi da sharaddinshi dakuma amsar daya bayar na zaije ya shawarta.

Yakuma gayamata zuwan da saudart tayi da abinda yafaru tsakaninsu wanda hakan yaqara 6atamashi rai dakuma qara jin lallai saiya aureta donya koyamusu hankali gabadaya.

Yabata labarin yadda alhaji yaita fadi tashi har yasamu saudart ta yarda dakuma yadda aurensu yakasance har izuwa zaman aurensu ya gangaro zuwa fara aikinta a companynshi da abubuwan dayaita mata na muzgunawa ya gangaro zuwa tafiyarsu spain da zamansu acan dakuma yadda ta taimaka mashi wajen kama mayaudaran mutanen dasukaso karyashi har zuwa lokacin dasuka dawomashi da kudinshi da niyyar kawo qarshen contract din da abinda yafaru aranar dukda ya 6oyemata kissing dinta dayayi sannan ya gangaro har zuwan da sadeeq yace yayi gidansu jiya da barazanar makashi kotu datayi.

Shiru yayi yana sauke numfashi ahankali saboda doguwar maganar dayayi.

Dakin yayi tsit babu mai ko motsi yadda kasan babu kowa ciki.

"Na aureta ne badon komaiba saidon in rama abinda yayimana ko fiyeda hakan, nabashi rancen ne bisa tsarin zanyi shige da fice yadda komai nashi zai lallace yakasance babu uwar kudi ba riba ga kuma uban bashi.

Nikuma lokacin sai in nuna bansan zancenba saiya biyani inhar yanason diyarshi, sonake ya talauce shima yakoma bayada komai shima ya dandana abinda ya dandana inyaso shima zuciyarshi ta buga ya fadi mattac..."

Tasss! Sautin dayaji a qunnenshi ya hanashi qarasawa.

Kafin ya tantance meyake faruwa tasake daukeshi dawani zazzafan marin a dayan kumatun

Dafe duka kumatun yayi ta dogo da sauri yana kallon ummy daka tsaye sai huci take idanunta sun chanza launi.

Toshe baki baby tayi da hannu biyu tana ware idanu, tashin hankali qarara a fuskarta.

"Da hankalinka?" Ummy ta fada tana nunashi da yatsa manuniya.

"Nace da hankalinka da iliminka ka aikata wannan abin da ko jahili bazai aikataba?"

Kasa koda motsi yayi daga tsugunnen dayake hannayenshi dafe da kunci yana kallonta

Yakasa yara yau ummy ta dora hannu akanshi da sunan duka abinda bazai iya tuna when last tayimashi va tsawon rayuwarshi

"Fansa haukane?! Aure? Aure ka maida abin wasa? Abun daukar fansa? Ka rusa rayuwar yarinya da future dinta duk akan fansa?" Ta tambaya cikin zaremashi idanu.

"Ummy don alla.." katseshi tayi ta hanyar qamtsamashi nashi qason marin

"Yimin shiru! Harda kai? Atunanina kafishi hankali ashe taron zamuce ta tadda muje?!"

Dafe kuncinshi shima yayi yana sadda kai qasa

"Kaiga sarkin zuciya? Mai zuciyar qarfe dabakasan kabar mutum da allah ba? Akan banzar daukar fansarka ka janyo wanda bata jiba bata ganiba kana neman lallatamata rayuwa?! Kana..."

Kasa idawa tayi ta juya kawai ta dafe kanta kasancewar ta mai zuciya idan ranta yayi mugun 6aci maganama gagararta yake.

Ganin hakan yasashi saurin rarrafowa yana riqemata qafa.

"Ummy am sorry, am soo sorry"

Fizge kafarta tayi da karfi taja baya.

"You're not but you will be, kutashi kufita! Kutashi nace!!"
Tafada tsakankanin abinda ya toshemata maqoshi.

Saurin tashi sadeeq yayi amma ashraf ko gezau

"Kutafi nace kuma kai.."

Ta nuna ashraf

"Gobe kamar yanzu inason ganinka anan gidan da takardar saudart, banaso ko igiya daya ta rage atsakaninku"

Agigice ya dago yana kallonta yayinda zuciyarshi tayi wani mugun bugawa.

"Kaji nagayamaka! Ke tashi kitafi dakinki!"

Ta dakama baby tsawa.

Dagudu ta tashi tayi sama aguje.

Itama bin bayanta tayi tahaye sama batareda tasake kallonsu ba.

Dafe kanshi ashraf yayi cikin tashin hankali wanda tunda yake beta6a shigaba yayinda zuciyarshi ke bada wani hucin zafi kamar a oven....✍️

*WAYE ASHRAF?*

Ummin fasihu ce🧚🏻‍♀️

👰🏻🤵🏻AUREN KWANGILA🤵🏻👰🏻
(Contract marriage)

Allah ka yayemana wannan annobar (covid19)🤲

Allah ka ji6anci lamurranmu, karka barmu da kanmu🤲

Story written by Ashaanty love💖
(Ummin fasihu)

065

*WANENE ASHRAF?*

*AUWAL MUHAMMAD* Haifaffen garin wudil ne dake jahar kano.

Su shidda ne awajen iyayensu *MUHAMMAD JARIRI* wanda akafi sani da *MAMMAN* da matarshi *AMEENATU*

Yayansu shidda, maza hudu mata biyu.

Auwal shine d'a nafarko, sai ibrahim dake bimishi sai Nuradeen, sai Jamila, sai Zaharadini sai auta Halimatu wanda watanta uku a duniya ta rasu.
Chapter 55 · 0% Book details