← Book details Auren Kwangila Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 58 OF 111

Sashe 58

Auren Kwangila Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kamar yadda yasaba saida yasha qamshi yana hura hanci sannan ya amince dukda can qasan ranshi murna yake don shima sadeeq na burgeshi don sadeeq badai raha da barkwanci ba, kwata kwata beda saurin fushi saidai idan aka quleshi beda kyau sa6anin ashraf da kamar akan wuya yake abu kadan ke hasalashi.

Ahaka suka qulla abota mai qarfi duk inda kaga daya sai kaga dayan har takai babu wanda besan da abotarsuba a fadin makarantar.

Alokacin allah yasama sana'ar kawu zaharadini albarka sosai don harya canza shago ya kama babba yana cigaba da sana'arshi ta kayan kitchen ashraf na dan kama mashi da tsaron shago duk sadda beda wani aikin yi.

Ahakan suka qarashe secondary school din lokacin baby ana primary.

Baby ta taso yarinya mai rigima da iyayi ga baki zai kamar parrot, rawar kanta yasa basa shiri kwata kwata da ashraf don kwa6darta yake idan tayimashi ba daidaiba babu abinda ya dameshi saidai yana sonta sosai.

Bayan result dinsu yafito ne suka samu daddadan albishir na scholarship da aka bada a school dinsu na mutane biyar qasar waje wanda ciki harda ashraf da sadeeq.

Farincikin ranar har rawa saida suka taka.

Cikin dan qanqanin lokaci aka gama shirin komai suka lula UK karatu.

Acanma bata sauya zaneba suna zuwa ba'a wani jimaba sukayi fice a school din saboda qoqarinsu ga hadin kai don kodayaushe tare suke dukda kamar kaji suke kodayaushe cikin fada suke donma sadeeq nada haquri.

Nanfa akaimasu caa don lokacin sun zama samari masu jida kyau da gayu dukda sadeeq ba fari bane amma baqinshi mai kyau ne ga uwa uba fara'a dake qarawa mutum kyau dayakeda ita.

Kan kace me yanmatan school din sukai musu caa dukda vasu cika tunkarar Ashraf ba don ba qaramin kwarjini yake musuba gashi fuskarshi ba wasa kullim a dinke take.

Sa6anin sadeeq da ba ruwanshi idan mace ta tinqareshi saiyace yanada aure harda 'ya'ya biyu qauye idan kuma tanason yayi nabiyu daita ya kaita qauye to.

Haka yake samu su rabu lfy dasu batareda ran kowa ta 6aci ba.

Ana haka kwatsam yaga ashraf na soyayya da suzy wata yar nigeria wanda itama karatu yakawota qasar saidai batada kamun kai ko kadan ga shiga ta fidda tsiraici.

Da farko yaso nisarda ashraf aibunta anma saiyaga kamar yana sonta sosai saiya qyaleshi saigashi basu wani yi nisaba suka rabu inda sukayi wani gaggarumin fada a filin makaranta sadda yaganta suna kissing da wani bayahude mai suna chris james

Daya nuna 6acin ransa akan haka saita fara bala'i wai bawani matsiyacin da zai hanata sakewa a school donma sun samu an biyamusu scholarship da a ina zasu ganta bare har raini yashiga tsakani?

Sosai abun ya6atawa ashraf rai don dakyar sadeeq ta janyeshi daga filin wanda yacika danqam da yan ganin qwam.

Tun daga lokacin kowa yakama gabanshi babu mai kula dan uwanshi har suka kammala abinda yakaisu suka dawo nigeria.

To anan ne zaharadini ya maidomasu dukiyarsu duka ganin ashraf ya mallaki hankalin kanshi.

Nan ummy taqi yarda suka amshi kudin kawai suka barmashi ribar dayaita juyawa hakan kuma ba qaramin dadi yayimasuba kuma hakan yaqaramata qima a idanun dangin mijinta.

Ahankali ahankali shima ashraf ya shiga harkar kasuwanci kasancewar shi dama ya karanta.

Nan sukayi hadin gwiwa da abokinshi kuma dan uwanshi sadeeq suka fara da kadan kadan har allah yasaka masu albarka suka bude tanqamemen company dinsu wanda suka samashi suna A.A ENTERPRISES LTD
wanda ahankali ahankali sukayi rassa a qasashe daban daban, talauci ya qaura a wannan ahalin suka koma kamar koma ince fiyeda yadda suke da.

Ashraf shima babanshi yabiyo a kyauta shiyasa kaf family dinshi babu mai kukan babu don babu babu din.

*CIGABAN LABARI*

sainaga ruwan comments tukun, naga alamun kwana biyu kun danyi sanyi🙁

Ummin fasihu ce🧚🏻‍♀️

👰🏻🤵🏻AUREN KWANGILA🤵🏻👰🏻
(Contract marriage)

Allah ka bamu zaman lfy a qasarmu nigeria🤲

Allah ka ji6anci lamuranmu, karka barmu da kanmu🤲

Story written by Ashaanty love💖
(Ummin fasihu)

067

*CIGABAN LABARIN*

Wani matsanancin ciwon kai ya saukoma Ashraf nan take yayinda jikinshi har tsuma yake saboda tashin hankali.

Ummy is requesting na ya datse igiyoyin dake tsakaninshi da Saudart duka kuma she mean it don ya hango dagaske take acikin qwayar idanunta.

Jiyayi an dafa kafadarshi ta dama.

Ko be dagoba yasan sadeeq ne hakan yasashi lumshe idanunshi dasuka chanza kala yana sauraron bugun ziciyarshi.

Har lokacin sadeeq na dafe da kafadarshi saidai yarasa kalmar dazaiyi amfani dashi wajen kwantar mashi da hankali don shima hankalin nashi atashe yake don shima bega alamun wasa ko sassauci atareda ummy ba.

Sun dade ahakan sannan sadeeq yayi qarfin halin jawo hannunshi sama alamun yataso sutafi.

Babu musu yatashi dakyar suka juya suka bar falon sadeeq na janye da hannunshi shikuma yana biye dashi kamar raqumi da akala.

Zama ummy tayi bakin gado tana dafe kanta da hannu daya.

This is unbelievable, takasa yarda da abinda Ashraf ya gayamata.

Saudart? Diyar shamsu? This is super shocking.

Ya akayi takasa hango kammaninta dana mahaifiyarta? Dama kullum idan ta kalleta saitaga kamar ta ta6a sanin face din awani waje.

Ya akayi takasa ganewa duk tsawon wannan lokacin? Kenan da khadija suke waya lokaci bayan lokaci?
Ya akayi takasa gane muryarta? Ya akayi su kawu ibrahim suka kasa gane shamsu lokacinda sukaje nemama Ashraf aure?

Qarar budewar kofa dataji yasata dagowa daga dafe kan datayi tana kallon mai shigowa.

Baby ce tashigo idanunta jawur alamun taci kuka.

Kallonta tacigaba dayi harta qaraso kusada ita ta zauna qasa.

Shiru dakin ya dauka kafin baby ta dago a raunane.

"Ummy?.." sai kuma tayi shiru tana hawaye.

Itama ummin shiru tayi saidai batabar kallonta ba

"Ummy don allah karki raba yaya da aunty..please karki 6ata komai ummy, ki gyarashi instead" tafada cikin muryar kuka.

Nan ma shiru, ummy batace uffan ba.

"Ummy.."

"Get out" inji ummy ahankali

"Ummy please..."

"Out!!!" Ta daka mata tsawa wanda babu shiri ta miqe tanufi hanyar fita tana toshe baki.

Komawa ummy tayi ta jingina da kan gadon, tunanika kala kala na kai kawo azuciyarta.

********************************************

Zaune saudart take a garden din gidansu ta kafe waje guda da idanu .

Tunda tasamu labarin ummy tasan komai hankalinta yaqi kwanciya.
Koda yaushe cikin fargaba take na kar mamy taji lbr don tasan idan taji to ta kade har ganyenta.

Wayarta ce tasake daukar ringing a karo na ba adadi.

Duba takai ga wayar tana kallon sunan mai kiran yayinda takejin wani iri cikin ranta.

Baby ce, tun shekaran jiya take matsamata da kira da massages kala2 tana magiyar tayi picking din call dinta.

Sosai takejin ba dadi har cikin zuciyarta don harga Allah tana qaunar baby fiyeda tunanin mai karatu don ta dauketa ne kamar qaramar qanwar da batadashi.

Haka taita kallon kiran harya tsinke sannan tasaki ajiyar zuciya ta dauki wayar ta kasheta gabadaya don Allah yasani ko zata shekara tana kira bazata iya dagawa ba, to ta daga tace me?

Komawa tayi ta jingina da resting chair din tana lumshe idanu tana tunanin hanyar daya kamata tabi don kawo qarshen wannan qaddararren auren.

Kafin su iso wani zazzafan zazza6i ya lullu6eshi, jikinshi yayi rauu.

Ganin haka yasa sadeeq juya akalar motar zuwa gidansu don bazai iya barinshi ta kwana shi kadaiba acikin wannan halin.

Dakyar ya taimakamashi yakaishi dakinshi ta kwantar dashi sannan yafito yana amsa tambayar ummy daketa tambayarshi lfy?

Amsamata yayi da zazza6i yakeyi sannan yayi saurin fita saboda gudun ta jegomashi wata tambayar.

Tunani umma tafarayi to idan zazza6i yake ina matarshi dazai kawoshi nan?

Hakan yasata daukar wayarta tashige daki don kiran unmy taji ko lfy?

Be dadeba sai gashi yadawo hannunshi dauke da ledar magunguna yashige dakinshi.

Cikin bargo ya tadda Ashraf yashige ya qudundune sai rawar sanyi yake.

Remote din a.c ya dauka ya kashe a.c din dakin sannan ya haura kan gadon yana dan yaye bargon.

"Ya sallam" tafada jin hucin zafin daya dakeshi, ahankali yakai hannunshi a saman goshinshi yajishi rauu.

"Sorry friend" yafada cikin tausayawa

"Bari na amsomaka abinci kaci kasha magani kaji ko?"

Shidai be bude idaninshi ba bare ya amsa.

Tashi sadeeq yayi ya bude kofar yafita don samarmasu abinci.

A falo ya tadda umma zaune da alamu ma tayi zurfi a tunani, jin takunshi yasa ta dago tana kallonshi harya qaraso.

Sosa qeya sadeeq yayi yanadan sinne kai alamun rashin gaskiya sannan yace

"Umma akwai abinci?"

Nuna mashi dining tayi batareda tayi magana ba tana tunanin to meke faruwa haka wanda Hajiya Fatima tace maganar bata waya bace saidai tazo?

Fatanta dai allah yasa lfy.

Wucewa yayi dining din ya dibarmusu abincin sannan yayi sama yana sauke ajiyan zuciyar sa'ar dayaci ummy bata tambayeshi komaiba.

Dakyar yasamu ashraf yaci abinci don har saida umma tasa baki sannan yadanci yasha magani yakoma ya kwanta yana rufe jikinshi gabadaya da bargo.

A ranar dai barci rabi da rabi yayi marar dadi saidai alhamdullilah zuwa safe jikin yadanyi sauki zafin jikin ya rage sosai saidai har lokacin kanshi nadan sarawa.

Yanzu ma bawani breakfast din kirki yayiba yatashi tashiga wanka yafito yabude closet din sadeeq ya ciro wasu qanannun wanda da alamu sabbi mane ya fara shiryawa.

Fitowa sadeeq yayi daga wanka shima ya tsaya yana kallon Ashraf dake taje sumarshi gaban mirror.

Qarasowa yayi shima wajen mirron yana daujan wani lotion ya matsa a hannu yafara murzama jikinshi.

"Ina zuwa haka?" Ya tambayi ashraf dake taje kanshi

"Ummy" yabashi amsa a taqaice

"Ok bari nima na shirya na rakaka"

"No katafi company kawai"

"Why? You need me, don't you?"

"Yes, amma company yafini buqatarka, katafi kawai nima zanzo bekamata ace daga ni harkai ba wanda yajeba" yafada yana daukan turaren dudduba turarrukan sadeeq yanason ganin wanda yakamata yafesa don babu kalar nashi anan.

"Ok but take care, uhm?"

"Sure" yafada yana ciro daya daga cikin turrarukan ya feffesa sama sama don duk basuyi mashi ba kawai manage yayi.

"Bani key" inji ashraf yana saka wayarshi a aljihu.

"Kafini sanin inda suke" inji sadeeq dake cikin closet tana za6an kayan dazaisa.

Guntun tsaki ashraf yaja yanufi bedside locker yaja ya dauki daya daga cikin keys din ya maida ya rufe.

"Natafi" yafada yana nufar qofa.

"Take care" inji sadeeq.

Koda yafito babu kowa falo sai wata mai aiki dake goge centre glass table.
Chapter 58 · 0% Book details