← Book details Auren Kwangila Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 110 OF 111

Sashe 110

Auren Kwangila Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sosai kanshi yadau chaji don sosai yanuna shi dan halak ne don komai tare sukeyi da sadeeq yayinda ya dauke mashi abubbuwa da dama yayimashi da aljihunshi

Ranar Daren biki wanda yayi daidai da kauyawa day

A wani gidan gona na ashraf aka yishi

Cä6 duk wanda beje party dinnan ba yayi missing

Watakan ya qayatu kamar me, dukan jama'ar wajen sanye suke cikin kayan ainahin kauyawa wadanda suka amsa sunansu kauyawa don bazaka ta6a tunanin akwai daya daga cikin su daya ta6a taka gate din makaranta ba don kowannensu da irin shigar ban dariyar dayayi

Shidai ango sanye yake da wata kodaddiyar malun malun mai jirwaye jirwaye don asalinta blue shadda ce aka jiqata a hypo dukta 6aci, babbar rigar har tadeshi take saboda girma da tsawo yasa wani dan iskan three quarter aciki wanda ba'ama hangoshi don malun malun din ta rufeshi sai rawanin daya Nada akai da wani blue din soson wanka abin gwanin dariya

Itakau baby sanye ake cikin riga daban, zane daban kallabi daban tawani tamke kai fuskarta kau tasha makeup din qauyawa da dige dige

Ashraf sanye yake cikin wata kodaddiyar Yar shara sai baqin three quarter shima wanda shine shigar manyan abokan ango sunsha irin wannan cover shoes din na Fulani
Saudart itama sanye take da kaya duk daban2 ga dan tumbinta daya qara qawata abun itama fuskarta tasha makeup din kauyawa kamar wata aljana hakama sauran qawayen wasuma abin nasu harda hauka

Ranar masu rake sunyi ciniki don kowanne da Yar sandar rakenshi a hannu

Waqa aka samasu ta qauyawa akafara shiga kamar a dandali ana rawa

Can aka saka waqar Naira Marley da cblvck mai taken *baby kingsway*

Duka manyan abokan ango idan ka cire ashraf da aka nemeshi ko sama ki qasa suka shiga Tareda mai girma ango daketa fama da malun malun dinshi ta fama

Suka shiga yin rawar waqar iri daya wanda da alama sunsha training kafin su iyata

Nan take wajen ya dauki tafi da sowa, abinda zaifi baka dariya shine rawar sadeeq don kafin sugama ya jigata sakammokon shan qasan dayake idan babbar rigarshi ta tadoshi kuma haka Yake tashi ya cigaba da rawanshi ko ajikinshi

Ansha dariya har saida cikin wasu ya kulle don wani abin da gangan sukeyi duk dan suba mutane dry

Saida suka gama sannan akaba Amarya da ango fili don su danse, aka saka masu waqar macukule suka shiga maming yadda kasan su suka yita dama

Kai fadin abubbuwan da akayi awajen 6ata bakine don sosai wajen yazama dandalin barkwanci don wasu saboda dariya cikinsu harya qulle

Can na hango yan group din *AUREN KWANGILA 1&2* da yan group din *OFFICIAL MARCY NOVEL* da yan group din *HOME OF NOVELS*

Can na hango *Maman naseer* na kallon *ayiya baby* dake qoqarin kwaikwayon rawar tingarangajam da wasu maxa keyi a filin wasan yayinda *beebat* da *Fatima haruna* ke tsamo2 cikin qawayen baby da alamun dai ansamu shiga

Awani bangaren kuwa *Maman Zainab* inkiya *nifa na nutsu😆* tana gefen ta nutsu tana kallon yadda wata kwaila daya daga cikin qawayen baby ke rawa kamar zata lauye

Akusada ita naga *Umma aliyu* da *malaash* suna tunsura dariya ganin kwalliyar wata wanda sak ya maidata wata ifrituwa

Agefensu kuma *Rahila Abba* ce tana rawar tambola har wani zaro harshe ake alamun rawa tayi dadi

Acan tsakiyar taro na hango *Maman Hassan* da ita da tawagarta su *ummukulthum*, *Dr halima* da *ummu sabira* tsaye kowa da Yar sandar rakenta ana wazga ana rausaya kai alamun abin na antayasu cikin shauqi sosai

*Ummu Muhseen* kau ana maqale bayan wasu yanmata yangayu masu selfie sai tantado take ita da tsiya sai an dauka daita (lol😆)

A bangaren ashraf kau dama fili na hargitsewa a rawar farko ya faki idon abokan shi ya lalla6a ya janye matarshi suka gudu

Dama jinsu bash yake lokacin dasuke cewa babu abinda zai hanashi dansewa ranar partyn ko training din rawan dasuka yi kallonsu kawai yake don bega lalacewar da zata sashi yin rawa a bikin koda kuwa ya iya bare shi zero over kunnuwa ne a fannin rawa, bega dalilin da zaisa yayi embarrassing din kanshi da kanshi ba

Saudart kau ta cika tayi famm don taji haushin gudowar dayayi da ita batareda taga komai ba a partyn hakan yasa ko kallonshi batayi saima kauda kai datayi tana kallon window din motar

Acan kau sai wajajen 10 na dare suka tashi kowa ya watse bakinshi dauke da labarin partyn

Washegari saudart taqara jin zafin tafiya daita da ashraf yayi sakammokon lbrin da yan biki ke badawa na partyn dama vidiyoyin da akayi, ta ciji yatsa sosai na missing datayi bama ita kadai ba harda wadanda suma basu samu hallata ba

Aranar gida ya ida kacamewa da jama'a kasancewar ranar daurin auren ne

Amarya ana can daki ita da zugar qawayenta masu halinta Wato duk yan iyayi ne, babu abinda ke tashi a dakin sai shewa da hirraraku, Amarya an qame akan gado taci adonta cikin wani danqareren pink lace mai touches din fari, fuskarnan tasha makeup ga kannan dashima yasha dauri

Babu ruwanta tana tsakiyar qawayenta suna shewa suna maida yadda akayi kamar ba ita za'a daurawa aure anjima ba

A bangaren saudart kau tana cikin jama'a komai da ita akeyi sosai dangin su ummy da Abba suka yaba qoqarinta don taxage komai daita akeyi.

Sai bayan an sauko sallar juma'a aka daura auren *ABUBAKAR SADEEQ UMAR* da *AMEENATU AUWAL (BABY)* akan sadaki mai daraja

Zokuga bakin ango, kasa rufe baki yayi don farinciki, mutane sai bashi hannu suke suna masu fatan zama lfy

Shima ashraf anci gayu cikin milk din yan ciki da babban riga kana ganinshi kaga aminin ango yayinda shikuma ango ke sanye da all white Wato komai nashi farine kama daga babbar rigarshi da yanciki zuwa takalmi zuwa hula kai komai nashi farine acewarshi yau farar ranace dole yayi shigar nuna hakan

Daga wajen daurin auren suka wuce reception inda akaci akasha cikin farinciki da aminci

Nanfa aka bude babin tsokana atsakanin angon da abokan ango, to dayake angon A ne shima sai caftar tayi dadi don duk abinda ka fada saiya samomaka amsarshi

Ashraf kau Kwata Kwata hankalinshi baya Kansu yakoma ga sarkin fushi Wato saudart da tun jiya tayimashi fushi don ya dauketa daga party, shi yanzu wani abin nata Dariya yake bashi don yanzu tazama wata rigimmamiyar qarfi da yaji, abu kadan sai kumburi

Tun dazu yake kiranta taqi dagawa, ganin bazata amsa dinba yasashi qyaleta yana cije lower lip dinshi

A bangaren saudart kau batama San yanayi ba don wayarta na cikin jakarta dake dakin ummy itakuma tana wajen Amarya da izuwa yanzu tayi laqwas, haka kawai taji jikinta yayi sanyi tun lokacin da labarin daurin aurenta ya risketa

Nanfa akazo aka zagayeta anata callara mata guda a kunne ana mata wakar tazama dauko riga

Tun baby na cijewa harta kasa riqe kukanta tashiga yin kayanta wurjanjan

Saudart ita abinma dariya yabata don bata manta yadda baby ke cika bakin babu abinda zaisata kuka ranar aurenta, ca6 kamar wani auren dole? Sai gashi tana kuka bilhaqqi da gaskiya

Dayake mutane duk sunsan shaqiyancinta babu wanda ya tausaya mata alokacin don kowa dariya yake mata yana qara tunzurata, saida akazo daukarta sannan tafara bawa mutane tausayi don kuka take sosai ta maqale umminta wai babu inda zata ita tafasa auren.

Dayawa sun tausayamata yayinda wasu irin su abokan wasanta sai qara tunzurata suke da waqar 'ke kikace kinaso'

Acikin masu tausaya mata harda saudart don sosai abin ya tuna mata da itama ranar aurenta hakan yasa take dauke hawayenta akai akai

Dakyar aka 6am6are Amarya jikin ummy da itama ke hawayen mixed feeling tana godewa Allah daya nunamata auren autarta lfy dakuma jimamin rabuwa da yarta wanda kowacce uwa mai aurar da diya keji

Haka aka fito daita akasata cikin galleliyar motar daaka tanadar ta daukar Amarya, cikin motar harda saudart don qin sakin hannunta baby tayi ta wani maqalemata dole saida ita aka shiga motar saudart na ayyana darun da za'asha idan zata taho

A wani qanqararren gida suka shiga, ba qarya gidan yabada don ya qawatu iya qawatuwa

Tarbar mutunci danginsu sadeeq sukayiwa su Amarya, gidan babu abinda ke tashi sai guda

Itade baby kanta na qasa fuskarta lullu6e da mayafi yayinda haryanzu take riqe da hannun saudart gamm

Saida aka rakasu hat dakinta dake sama yasha kayan alatu sannan ala barsu don suyi shirin walima

Chanza shiga duk sukayi inda Amarya taci adonta cikin maroon materials riga da skirt aka doramata alkyabba milk colour asama wanda hular ta rufe mata rabin fuska

Saudart dai shadda purple tasa riga da zane pieces sannan ta dora zumbuleliyar hijabinta wanda yanzu ya zamemata jiki don rabon datasa gyale harta manta don baban kishi be bari idanma zatasa saidai tasa cikin gida tayimashi kwalliya amma bawai tafita dashi ba

Sosai walimar ta qayatar, ango da Amarya sunfito sharr dasu kamar ka sace, ango shima dakkakiyar shadda milk yasha wanda sukayi ango shida dukan abokanshi, fuskarshi sai fidda annuri take

Ansha wa'azuzuka masu ratsa jiki sannan aka dora da zikiri mai antaya mutane shauqi sannan aka rufe da addu'a

Saida aka gama sannan aka maida Amarya dakinta dama kuma magrib tayi

Sosai baby ta tashi hankalinta ganin bata ga wulgin saudart ba, koina an duba ko sama ko qasa babu ita hakan yasa baby kuka sosai dukta tada hankalin mutane

Itakau saudart dama tun fitowarsu taga ashraf cikin zugan abokanshi, to tun kafin taron ya watse tabishi suka gudu bayan sun gama sassanta tsakaninsu

Baby kau taci kuka dakyar aka samu aka rarrasheta, qawayenta kau saida aka rako ango sannan suka samu suma suka fece tareda abokan ango, akabar daga Amarya sai ango (zakici ubanki ne😎)

*Agurguje*

Akwana atashi lokaci yacigaba da tafiya, kwanaki na zama sati, sattitika na zama watanni

Watan haihuwar saudart Yakama yayinda izuwa yanzu dukta chanza kammani saboda yadda cikin ya hurata

Ranar wata laraba ta tashi da naquda aka garzaya da ita asibiti

Saida ta wahala sosai sannan ta sulli6o danta masha Allah mai kamada ubanshi

Zokaga murna wajen wannan ahalin

Ashraf baki har qeya anyi da, anzama daddy

Sosai akayi hidima ga haihuwar wanda baby bata wani yi abin kirkiba awurin saboda qaramin cikinta dake bata wahala don mai laulayine sosai
Chapter 110 · 0% Book details