Sashe 20
Auren Kwangila Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Can na hango ummu bilal ana ta miqa hannu za'a amshi Leda Bayan ga wata nan cikin qatuwar hijabinta sai kunbiya kunbiya take daita.
Dayan gefen kau sis hajara Nagani sai bin baby take kamar bindi Wai adole sotake su zama qawaye don tasamu hallatar dinner Bayan daurin aure.
Can gefe naga maman fateema da ummu arifullah suna leqa ledar juna don ganin me suka samu.
Itakau umman abdullra'uff ana gefe kan kujera sai gutsirar pizza ake ana tauna ana wani lumshe idanu (ba sabban ba🤣)
A can gefe kuma Mamman twins ce kamar tayi bindiga don bata samu komaiba, su twins sun hana🤣 basu tashi rikice mataba saida aka fara rabo, Maman twins fa ta kumbura, wazai kawo gudunmawar allura a saceta?🤣
Taro yayi taro inda aka hada malama wasila da shatara na arziqi, sai godiya take tana kwararowa auren albarka ana amsawa da amin.
Itakau Saudart dama ana gamawa tasamu ta silale daki ta kulle kanta tafada kan gado ko alkyabbar bata cireba sai kuka.
Sosai jikinta yayi Sanyi Jitake inama zata iya maida hannun agogo baya da kome daddy zaiyi da bata yarda da aurennan ba Amma inaa? Kin makara Saudart bakin alqalami ya buhe😏
Washegari kuma wato ranar Daren biki yayi daidai da ranar mother's Eve nasu Ummy.
Su baby amara qahon zuciyar biki don kau wannan Tawuce qirjin biki, shirya wa sukayi dukkansu suka wuce gidansu.
Babu yadda basuyi ba akan Saudart ma ta shirya sutafi tare Amma hausawa ma sunce shiru ma amsace don kwandon shara tasamu tasakasu ciki ta rufe.
Tafiyar su sukai suka barta ita kadai dama haka tafiso don taji dadin yin tunanin ta.
A gidansu A.A akayi mother's Eve din a garden dinsu dake can cikin gidan.
Sosai partyn ya qayattar, bawani chasu akayiba kawai zazzauna ake kowane table da kujeru hudu round dinshi ana zaune ana ci anasha ana fira ga wani sanyayan kida dake tashi a background.
A ataqaice sai 10:oopm su baby suka dawo gidan mamy kowacce agajiye liqis kuma kowa ce da burin data tanaddarwa gobe, wato ranar daurin auren.
*******************************************
Bankado kofar akayi da wani uban force kamar za'a qilleta.
"Gobene! Daga gobene fah! Gobene!! Gobene! Daga gobene haba! Gobene!"
Wani uban tsaki Ashraf yaja kamar bakin zai cire yana antayamashi wata uwa uban Harara.
"Waikai wane irin marar saiti ne zaka wani shigo na mutane daki bako sallama"
Yafada cikin Fushi
Daga hannuwa Sadeeq yayi alamun surrender yana dariya sannan yakoma bakin kofar ya kwala wata uwar sallama sannan yashigo.
Tsaki Ashraf yasake ja yana maida kanshi kwance yana cigaba da shafe shafen wayar shi.
"Ango! Ango!! Kaga ango wajen amaryar sa Saudatu tauraruwar mata, ango bada kanka asare kaje gida kacewa Ummy ya6ace, ango kasha qamshi, kana kuma cikin shan qamshi kuma zaka sha qamshi" ya qarashe zancen yana kashe mashi ido daya😜
Ashraf da tunda yafara 6a66atu yakeji kamar ya shaqeshi kowama ya huta ya juyamishi baya yana Jan tsaki.
"Ko tsakama datayi bataci ribaba, tsaki kamar wata tsohuwar karuwa, Nidai tashi su bash na falo don iskanci kawani zo ka qunqume uwar daka kamar wata sabuwar amarya"
"Bazan fitoba din! Kasan Allah Sadeeq? Wlh Allah zan mugu mugun sa6amaka, Wai ina ruwanka danine uhm? Dakai mayene dana kade har ganyena, wlh ka fita sabgata Tun kafin na shufkama rashin M"
"Tun yaushe kuma allaramma ango? Rashin m dinka ai harna saba dashi Kaga babu abinda zai tadamin hankali, oya miqe"
"Don ubanka miqar dani din" yafada cikin qulewa
"Wlh tsab kai kanka kasan ina iyawa Amma sbd kai angone Shiyasa nake ragamaka.."
"Dan ubanka karka ragamani, mtcheew dalla fita!"
"Yo ai hikenan, tunda hakan kakeso"
Yafada yana fita
Tsaki Ashraf yasake ja sannan yakoma ya kwanta, ba laifinshi bane don yaga nazo gidansu ne.
Be gama tunaninshi ba yaji ansake banko kofar, dagowar dayayi yaga su bash sunata shigowa sukai biyar da Sadeeq daya cika na shiddan.
Dafe kai Ashraf yayi yana komawa yana kwanciya, yasan yau tashi ta qare.
Nan kau suka hau tsokanarshi Tun yana Masu kumfar baki harya saduda don tsagerane suka hadu don wasu cikin su sunmafi Sadeeq qulluwa.
Haka ya zuba Masu idanu har suka gaji suka kyaleshi, shima saida yayi barcin qarya sannan suka shafamashi lfy, nan suka juya akalar firar zuwa na dinner gobe kowa na fadin albarkacin bakinshi.
Sai can wajajen dayan dare suka samu suka kwanta shikau Ashraf tuni dama barci yayi awon gaba dashi.
RANA BATA QARYA....✍
Ummin fasihu ce🧚♀
🤵🏻👰🏻AUREN KWANGILA👰🏻🤵🏻
(Contract marriage)
Allah ka yayemana wannan annobar (covid19)🤲
Allah ka ji6anci lamuranmu. Karka barmu da kanmu🤲
Story written by Ashaanty love
(Ummin fasihu)
029
RANA BATA QARYA......
Yau ranar jumu'a ce mai cike da tarihi a rayuwar wasu, jumu'ar da bazasu ta6a mantawaba.
Yau ne ranar daurin aurensu, AUREN KWANGILA.
Tunda ta farka ko matsawa Daga inda take batayiba, dama ba Sallah takeba bare ta tashi tayi.
Tana kwance ido lumshe kamar mai barci Saidai idanunta biyu tana sauraron Duk wani zirga zirga da hayaniyar mutane.
*yau ne* tafada cikin zuciyarta
*yau ba gobeba*
*yau zan zama matar aure*
*matar auren kwangila*
*matar mutumin da banajin ko digon sonshi daidai da qwayar zarra acikin zuciyata*
*matar aurenda nan da wani d'an lokaci zata zama baza wara*
*me kika yima kanki Saudart?*
*anya baki cuci kanki ba*
*anya daddy beso kanshi dayawa ba*
*inama ace mafarki ne*
*Allah yasa mafarki ne*
*Allah yasa ba gaske bane*
Hawaye suka silalo mata dukda idanun a rufe yake.
Wani nauyi taji zuciyarta nayi mata kamar an doramata qaton nutse a qirji.
Sosai hawayen keta silalowa batareda tayi wani yunqurin taresu ko sharesu ba.
Daidai nan mardeeya tashigo dama sunje amso dinkin anko dinsu ne dawowarsu kenan tabaro su baby qasa.
"Subhanalillah" tafada tana Qarasowa wajenta.
"Saudart" tafada tana dan jijjigata ganin idanunta haryanzu a rufe yake.
Banza tayi da ita Saidai hakan besa hawayen sun tsayaba.
"Sister menene? Dan Allah ki tashi, Meya faru?"
Nanma shiru saima juyamata baya datayi.
"Saudart kiyi hqr, nasan kukanki baya rasa nasaba da auren daza'a daura miki yau, Duk macen datasan ciwon kanta dole ta koka ranar aurenta ba don zata bar iyayenta kadaiba, don itama zata taka wani matsayi wanda bata ta6a takawaba a rayuwarta, nauye nauye zasu hau kanta wanda idan ba me dakkakiyar zuciya bace bazata iya dauke nauyin ba"
Kamo hannayenta tayi tariqe sannan cikin sigar rarrashi tace
"Sis kiyi hqr, Allah baya dorawa bawa abinda baya iyawa, ki kasance mai Neman tallafi a wajen Allah kuma ki kasance mai hqr, idan kinadashi ada ki Dora akai, darajar 'ya mace ke har namiji ma shine aure, ki kasance jajirttaciyar mace abun kwatance a fannin aure, ki zama abun alfahari ga mamy da daddy ke harma garemu gabaki daya, dukda aure rai gareshi idan ba'a mutu dashiba yakan mutu yabar ma'auratan don Allah aurenki yazama abin kwatance a family dinmu, babu yaji bare saki please, nafi kowa sanin yadda mamy ta kwallafa rai akan aurenki don sau ba adadi ina jinsu idan suna fira da ummina akan tanason kar aurenki yazama irin nata, tafison kiyi auren mutu-ka-raba, ya kasance yayanki duka nawajenki yadda zaki basu tarbiyya kuma su taso tare, please sister kicikama mamy wannan buri nata, ki jajirce sis, aure yanada dadi haka wani shafin idan aka bude yafi mad'aci daci, ki riqe Allah da manzonsa kuma ki riqe hqr.."
Shiru tayi ganin yadda kukan nata ya tsananta, shiru tayi tana kallon yadda take kukan, abinka ga ruwa ruwa sai itama taji digg digg hawaye sunfara digomata.
Nan aka rasa mai rarrashin wani cikinsu don hade kai wuri guda sukayi hannunsu cikin na juna sunata rizgar kuka.
Ita kukan Saudart ya Kasu kashi kashi, ga na fargabar aure da na barin iyaye gana fargabar yadda mamy zataji idan auren ya mutu.
Itakau mardeeya kukan tsantsar tausayinta take dama na mata gabadaya, wanda Daga inda kayi aure nauyi yahau kanka, gana miji, idan kuma aka hayyayafa gana 'ya'ya.
Ahaka su baby suka taddasu.
Turus sukayi abakin kofa suna kallonsu kowacce takasa motsi.
Baby ce ta fara takawa ta qarasa wajensu itama ta zauna ta rungumosu gabadaya itama ta bude nata muryar da Allah yabata tafara raira nata kukan.
Ganin hakan yasa itama Nafeesa tayi wajensu dagudu itama ta rungumosu sukaita kukan tare da wannan ya dauka sai wannan ya aje, da wannan ya aje sai wannan ya dauka.
(Nima ganin haka yasa nadan kauda kaina na matso guntun hawaye na😢 sannan na share da hanki)
Suna haka matar kawu bala tashigo, tana ganin yadda suka cure waje daya tafara sallalami tana tafa hannaye.
"Ni asiya mezan gani?"
Hakan yasasu dagowa Kowanne fuska jaga jaga da hawaye.
"Wannan wane irin sabon sakarcine zakuzo Ku cure waje daya kuna kuka? Meya faru?"
Nafeesa ta nunasu cikin muryar kuka tace "haka nisa baby mukazo muka tardasu suna kuka"
"Mtcheew Maimakon Ku rarrashesu shine kukayi joining? Ke mardeeya Meya sakaku kuka?"
"Haka nazo na isketa nima tanayi"
"Mtcheew, andaiji haushi Maimakon ki rarrasheta shine kika biyemata"
"Na rarrasheta taqi shiru"
"Mtcheew ni matsamin dalla"
Ta wuce ta kamo hannun Saudart da kanta ke duqe haryanzu tana hawaye.
"Ya isa haka baby, kiyi hqr kinji? Kowa haka yaji a lokacinshi, kiyi hqr, taho muje"
Tafada tana miqar daita tsaye suka nufi hanyar waje.
"Saura kuma Ku zauna karku tashi Ku shirya" tafada tana ficewa da Saudart.
Sun kusan mintuna goma zaune jigum jigum babu mai magana.
Can kamar an tsikari baby ta wani miqe tsaye tana kallon agogon hannunta.
"Guys har 11:30am yayi fa, Nidai bari kuga infada toilet, ato banmaga meye nawani kukaba Bayan ba aurena bane kuma ma aini farinciki yakamata nayi za'a rabani da dunqum"
Ta qarashe zancen tana Fadawa toilet.
Kallon Kansu sukayi Bayan sun rakata da kallo harta shige sai sukayi murmushi.
Bedroom din mamy anty asiya ta kaita don nan kadaine babu mutane.
Nan ta zaunar daita tanata yimata nasiha sannan Daga bisani ta hadamata ruwa mai dan gumi a jacuzzi tabata umarnin tashiga tayi wanka.
Ba musu ta shiga Bayan ta cire kayanta ta daura towel.
Ta dade sosai a toilet din sannan tafito tana tafiya kamar wanda Kwai yafashe mawa aciki.
Kayan data tadda kan gado wanda anty asiya ta fiddomata ta dauka tasa.
Dayan gefen kau sis hajara Nagani sai bin baby take kamar bindi Wai adole sotake su zama qawaye don tasamu hallatar dinner Bayan daurin aure.
Can gefe naga maman fateema da ummu arifullah suna leqa ledar juna don ganin me suka samu.
Itakau umman abdullra'uff ana gefe kan kujera sai gutsirar pizza ake ana tauna ana wani lumshe idanu (ba sabban ba🤣)
A can gefe kuma Mamman twins ce kamar tayi bindiga don bata samu komaiba, su twins sun hana🤣 basu tashi rikice mataba saida aka fara rabo, Maman twins fa ta kumbura, wazai kawo gudunmawar allura a saceta?🤣
Taro yayi taro inda aka hada malama wasila da shatara na arziqi, sai godiya take tana kwararowa auren albarka ana amsawa da amin.
Itakau Saudart dama ana gamawa tasamu ta silale daki ta kulle kanta tafada kan gado ko alkyabbar bata cireba sai kuka.
Sosai jikinta yayi Sanyi Jitake inama zata iya maida hannun agogo baya da kome daddy zaiyi da bata yarda da aurennan ba Amma inaa? Kin makara Saudart bakin alqalami ya buhe😏
Washegari kuma wato ranar Daren biki yayi daidai da ranar mother's Eve nasu Ummy.
Su baby amara qahon zuciyar biki don kau wannan Tawuce qirjin biki, shirya wa sukayi dukkansu suka wuce gidansu.
Babu yadda basuyi ba akan Saudart ma ta shirya sutafi tare Amma hausawa ma sunce shiru ma amsace don kwandon shara tasamu tasakasu ciki ta rufe.
Tafiyar su sukai suka barta ita kadai dama haka tafiso don taji dadin yin tunanin ta.
A gidansu A.A akayi mother's Eve din a garden dinsu dake can cikin gidan.
Sosai partyn ya qayattar, bawani chasu akayiba kawai zazzauna ake kowane table da kujeru hudu round dinshi ana zaune ana ci anasha ana fira ga wani sanyayan kida dake tashi a background.
A ataqaice sai 10:oopm su baby suka dawo gidan mamy kowacce agajiye liqis kuma kowa ce da burin data tanaddarwa gobe, wato ranar daurin auren.
*******************************************
Bankado kofar akayi da wani uban force kamar za'a qilleta.
"Gobene! Daga gobene fah! Gobene!! Gobene! Daga gobene haba! Gobene!"
Wani uban tsaki Ashraf yaja kamar bakin zai cire yana antayamashi wata uwa uban Harara.
"Waikai wane irin marar saiti ne zaka wani shigo na mutane daki bako sallama"
Yafada cikin Fushi
Daga hannuwa Sadeeq yayi alamun surrender yana dariya sannan yakoma bakin kofar ya kwala wata uwar sallama sannan yashigo.
Tsaki Ashraf yasake ja yana maida kanshi kwance yana cigaba da shafe shafen wayar shi.
"Ango! Ango!! Kaga ango wajen amaryar sa Saudatu tauraruwar mata, ango bada kanka asare kaje gida kacewa Ummy ya6ace, ango kasha qamshi, kana kuma cikin shan qamshi kuma zaka sha qamshi" ya qarashe zancen yana kashe mashi ido daya😜
Ashraf da tunda yafara 6a66atu yakeji kamar ya shaqeshi kowama ya huta ya juyamishi baya yana Jan tsaki.
"Ko tsakama datayi bataci ribaba, tsaki kamar wata tsohuwar karuwa, Nidai tashi su bash na falo don iskanci kawani zo ka qunqume uwar daka kamar wata sabuwar amarya"
"Bazan fitoba din! Kasan Allah Sadeeq? Wlh Allah zan mugu mugun sa6amaka, Wai ina ruwanka danine uhm? Dakai mayene dana kade har ganyena, wlh ka fita sabgata Tun kafin na shufkama rashin M"
"Tun yaushe kuma allaramma ango? Rashin m dinka ai harna saba dashi Kaga babu abinda zai tadamin hankali, oya miqe"
"Don ubanka miqar dani din" yafada cikin qulewa
"Wlh tsab kai kanka kasan ina iyawa Amma sbd kai angone Shiyasa nake ragamaka.."
"Dan ubanka karka ragamani, mtcheew dalla fita!"
"Yo ai hikenan, tunda hakan kakeso"
Yafada yana fita
Tsaki Ashraf yasake ja sannan yakoma ya kwanta, ba laifinshi bane don yaga nazo gidansu ne.
Be gama tunaninshi ba yaji ansake banko kofar, dagowar dayayi yaga su bash sunata shigowa sukai biyar da Sadeeq daya cika na shiddan.
Dafe kai Ashraf yayi yana komawa yana kwanciya, yasan yau tashi ta qare.
Nan kau suka hau tsokanarshi Tun yana Masu kumfar baki harya saduda don tsagerane suka hadu don wasu cikin su sunmafi Sadeeq qulluwa.
Haka ya zuba Masu idanu har suka gaji suka kyaleshi, shima saida yayi barcin qarya sannan suka shafamashi lfy, nan suka juya akalar firar zuwa na dinner gobe kowa na fadin albarkacin bakinshi.
Sai can wajajen dayan dare suka samu suka kwanta shikau Ashraf tuni dama barci yayi awon gaba dashi.
RANA BATA QARYA....✍
Ummin fasihu ce🧚♀
🤵🏻👰🏻AUREN KWANGILA👰🏻🤵🏻
(Contract marriage)
Allah ka yayemana wannan annobar (covid19)🤲
Allah ka ji6anci lamuranmu. Karka barmu da kanmu🤲
Story written by Ashaanty love
(Ummin fasihu)
029
RANA BATA QARYA......
Yau ranar jumu'a ce mai cike da tarihi a rayuwar wasu, jumu'ar da bazasu ta6a mantawaba.
Yau ne ranar daurin aurensu, AUREN KWANGILA.
Tunda ta farka ko matsawa Daga inda take batayiba, dama ba Sallah takeba bare ta tashi tayi.
Tana kwance ido lumshe kamar mai barci Saidai idanunta biyu tana sauraron Duk wani zirga zirga da hayaniyar mutane.
*yau ne* tafada cikin zuciyarta
*yau ba gobeba*
*yau zan zama matar aure*
*matar auren kwangila*
*matar mutumin da banajin ko digon sonshi daidai da qwayar zarra acikin zuciyata*
*matar aurenda nan da wani d'an lokaci zata zama baza wara*
*me kika yima kanki Saudart?*
*anya baki cuci kanki ba*
*anya daddy beso kanshi dayawa ba*
*inama ace mafarki ne*
*Allah yasa mafarki ne*
*Allah yasa ba gaske bane*
Hawaye suka silalo mata dukda idanun a rufe yake.
Wani nauyi taji zuciyarta nayi mata kamar an doramata qaton nutse a qirji.
Sosai hawayen keta silalowa batareda tayi wani yunqurin taresu ko sharesu ba.
Daidai nan mardeeya tashigo dama sunje amso dinkin anko dinsu ne dawowarsu kenan tabaro su baby qasa.
"Subhanalillah" tafada tana Qarasowa wajenta.
"Saudart" tafada tana dan jijjigata ganin idanunta haryanzu a rufe yake.
Banza tayi da ita Saidai hakan besa hawayen sun tsayaba.
"Sister menene? Dan Allah ki tashi, Meya faru?"
Nanma shiru saima juyamata baya datayi.
"Saudart kiyi hqr, nasan kukanki baya rasa nasaba da auren daza'a daura miki yau, Duk macen datasan ciwon kanta dole ta koka ranar aurenta ba don zata bar iyayenta kadaiba, don itama zata taka wani matsayi wanda bata ta6a takawaba a rayuwarta, nauye nauye zasu hau kanta wanda idan ba me dakkakiyar zuciya bace bazata iya dauke nauyin ba"
Kamo hannayenta tayi tariqe sannan cikin sigar rarrashi tace
"Sis kiyi hqr, Allah baya dorawa bawa abinda baya iyawa, ki kasance mai Neman tallafi a wajen Allah kuma ki kasance mai hqr, idan kinadashi ada ki Dora akai, darajar 'ya mace ke har namiji ma shine aure, ki kasance jajirttaciyar mace abun kwatance a fannin aure, ki zama abun alfahari ga mamy da daddy ke harma garemu gabaki daya, dukda aure rai gareshi idan ba'a mutu dashiba yakan mutu yabar ma'auratan don Allah aurenki yazama abin kwatance a family dinmu, babu yaji bare saki please, nafi kowa sanin yadda mamy ta kwallafa rai akan aurenki don sau ba adadi ina jinsu idan suna fira da ummina akan tanason kar aurenki yazama irin nata, tafison kiyi auren mutu-ka-raba, ya kasance yayanki duka nawajenki yadda zaki basu tarbiyya kuma su taso tare, please sister kicikama mamy wannan buri nata, ki jajirce sis, aure yanada dadi haka wani shafin idan aka bude yafi mad'aci daci, ki riqe Allah da manzonsa kuma ki riqe hqr.."
Shiru tayi ganin yadda kukan nata ya tsananta, shiru tayi tana kallon yadda take kukan, abinka ga ruwa ruwa sai itama taji digg digg hawaye sunfara digomata.
Nan aka rasa mai rarrashin wani cikinsu don hade kai wuri guda sukayi hannunsu cikin na juna sunata rizgar kuka.
Ita kukan Saudart ya Kasu kashi kashi, ga na fargabar aure da na barin iyaye gana fargabar yadda mamy zataji idan auren ya mutu.
Itakau mardeeya kukan tsantsar tausayinta take dama na mata gabadaya, wanda Daga inda kayi aure nauyi yahau kanka, gana miji, idan kuma aka hayyayafa gana 'ya'ya.
Ahaka su baby suka taddasu.
Turus sukayi abakin kofa suna kallonsu kowacce takasa motsi.
Baby ce ta fara takawa ta qarasa wajensu itama ta zauna ta rungumosu gabadaya itama ta bude nata muryar da Allah yabata tafara raira nata kukan.
Ganin hakan yasa itama Nafeesa tayi wajensu dagudu itama ta rungumosu sukaita kukan tare da wannan ya dauka sai wannan ya aje, da wannan ya aje sai wannan ya dauka.
(Nima ganin haka yasa nadan kauda kaina na matso guntun hawaye na😢 sannan na share da hanki)
Suna haka matar kawu bala tashigo, tana ganin yadda suka cure waje daya tafara sallalami tana tafa hannaye.
"Ni asiya mezan gani?"
Hakan yasasu dagowa Kowanne fuska jaga jaga da hawaye.
"Wannan wane irin sabon sakarcine zakuzo Ku cure waje daya kuna kuka? Meya faru?"
Nafeesa ta nunasu cikin muryar kuka tace "haka nisa baby mukazo muka tardasu suna kuka"
"Mtcheew Maimakon Ku rarrashesu shine kukayi joining? Ke mardeeya Meya sakaku kuka?"
"Haka nazo na isketa nima tanayi"
"Mtcheew, andaiji haushi Maimakon ki rarrasheta shine kika biyemata"
"Na rarrasheta taqi shiru"
"Mtcheew ni matsamin dalla"
Ta wuce ta kamo hannun Saudart da kanta ke duqe haryanzu tana hawaye.
"Ya isa haka baby, kiyi hqr kinji? Kowa haka yaji a lokacinshi, kiyi hqr, taho muje"
Tafada tana miqar daita tsaye suka nufi hanyar waje.
"Saura kuma Ku zauna karku tashi Ku shirya" tafada tana ficewa da Saudart.
Sun kusan mintuna goma zaune jigum jigum babu mai magana.
Can kamar an tsikari baby ta wani miqe tsaye tana kallon agogon hannunta.
"Guys har 11:30am yayi fa, Nidai bari kuga infada toilet, ato banmaga meye nawani kukaba Bayan ba aurena bane kuma ma aini farinciki yakamata nayi za'a rabani da dunqum"
Ta qarashe zancen tana Fadawa toilet.
Kallon Kansu sukayi Bayan sun rakata da kallo harta shige sai sukayi murmushi.
Bedroom din mamy anty asiya ta kaita don nan kadaine babu mutane.
Nan ta zaunar daita tanata yimata nasiha sannan Daga bisani ta hadamata ruwa mai dan gumi a jacuzzi tabata umarnin tashiga tayi wanka.
Ba musu ta shiga Bayan ta cire kayanta ta daura towel.
Ta dade sosai a toilet din sannan tafito tana tafiya kamar wanda Kwai yafashe mawa aciki.
Kayan data tadda kan gado wanda anty asiya ta fiddomata ta dauka tasa.