← Book details Auren Kwangila Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 63 OF 111

Sashe 63

Auren Kwangila Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Umarni ummy taba baby kan taje su hadamashi break su kawo nan ta fadama sadeeq shima yaje gida ya huta hakanan ita zata zauna dashi.

Da to duk suka amsa suka fita inda sadeeq yawuce da baby gida.

Jawo kujera ummy tayi ta zauna kusada gadon tana kallon dan nata abubbuwa namata yawo a zuciya tana tuhumar kanta na tsauraramashi.

Tasan yadda Ashraf ke taka tsantsan da gudun 6acin ranta, koyaya ra chanza fuska saiya shiga taitayinshi.

Irin wadannan yaran ne da suke tsoron 6acin ran iyayensu ko yayane, basu qaunar suga 6acin rai a tattare dasu komai qanqantarshi.

Wataqila she's so harsh on him, wataqila ta tsauraramashi dayawa.

Amma kuma ko menene tayimashi shi yaja, tasan yanada kwakwarar hujja na daukar fansa kan Alhaji shamsu saidai bataga hujjarshi na hadawa da innocent diyarshi ba.

Bataga dalilin dayasa zai jata a abinda batada masaniya akai ba, ya lallatamata rayuwa da wani banzan dalili nashi.

Ta tausayawa halin daya shiga amma hakan bazaisa taso kanta dayawa ba, bazata ta6a bari sucigaba da zaman cutarwa ba, bazata tilastawa saudart zama dashiba koda kuwa hakan na nufin zai wahala fiyeda haka.

Tasan yafara sonta, tun a reaction dinshi sanda ta nemi ya kawomata takardarta.

Tasan be iya son abuba kuma yana matuqar wahala idan ya kwallafama abu rai besamu ba.

Saidai hakan vazai sa taso kanta ba ta tauye haqqin diyar wasu.

Yadda takejin son nata dan da tausayinshi haka suma iyayen nata sukeji koma fiyeda hakan.

Ajiyar zuciya tasake saukewa tana qara kallon face din ashraf zuciyarta na saqa da warwara....✍

Manage🙏

Ummin fasihu ce🧚🏻‍♀️

🤵🏻👰🏻AUREN KWANGILA🤵🏻👰🏻
(Contract marriage)

Story written by Ashaanty love💖
(Ummin fasihu)

072

Ahankali yafara bude idanunshi dayaji sun qaramashi extra nauyi.

Dishi dishi yafara gani dafarko sannan yafara ganin clearly.

Bin dakin yashiga yi da kallo yanason gane a ina yake.

Idanunsu suka sarke dana Ummy dake kallonshi shima.

Gabanshi ne yafadi wanda hakan yasashi yunkurin tashi da sauri.

Saurin tashi ummy tayi itama tana dafashi.

"Easy, kabi sannu you're still weak" tafada cikin kulawa tana jingina mashi pillow abaya don ya jingina.

Ahankali ya jingina da pillon yana bin ummy da kallo kamar yanason tabbatarwa kanshi ita dince.

"Ya jikin?" Tafada softly

Gyada kai kawai yayi yana kallonta

Shafa kanshi tayi tana dan murmushi

"Allah ya qara sauqi kaji? Bari nakira Dr" ta tashi tanufi waje yabita da kallo harta fice.

Ajiyar zuciya ya sauke yanajin kamar anyi lifting wani qaton dutse daga saman qirjinshi.

Bin dakin yashigayi da kallo wanda ya tabbatarmashi hospital yake.

Ajiyar zuciya yasake saki yana komawa ya jingina sosai da pillon dake bayanshi yana tuna abinda yafaru jiya.

Shi kadai yasan abinda yakeji jiyan nan don qirjinshi inbanda zafi babu abinda yake, jiyake kamar ana iza wutane a qirjinshi amma yanzu alhamdullilah yarage sosai sai dan abinda ba'a rasa ba.

Bude kofar da'akayi yasashi dagowa yana kallon kofar.

Baby ce tashigo riqeda basket din abinci abayanta kuma sadeeq ne cikin wasu kayan da alamun yayi wanka ne riqeda qatuwar leda dake shaqe da kayan itace.

Da sauri baby ta qaraso bakin gadon ta ajiye basket din ta kamo hannun ashraf murmushi fall fuskarta.

"Yaya you're awake?" Tafada cikin murna

Guntun murmushi kawai yayimata yana dan lumshe idanu.

Qarasowa shima sadeeq yayi yana fadin

"Inyee gawa taqi rami? Ai harna fara cinikin gero shine dan baqinciki ka tashi?" Yafada shima yana ajiye ledar hannunshi kan locker dake kusada gadon ashraf.

Murmushi kawai ashraf yayi don haryanzu beda kuzari sosai.

"To saika fasa don yayana ko turwa ta shafa mashi lfy a taurin rai, sai yafara shan naka gumbar kafin asha tashi" inji baby tana murgudamashi baki.

Dan waro idanu sadeeq yayi yana rufe bakinshi da tafin hannu

"Iyee? Dama fatan dakike mani kenan? Kodayake ke zaki kwan ciki, kizama bazawara nabarki da maray..."

Waro idanun da baby tayi yasashi saurin sakama zancenshi full stop yana wulwulga idanu cikin rashin gaskiya.

Ashraf dai kallonsu yake kallon tuhuma, ganin haka yasa baby saurin duqawa ta ciro flask din cikin basket din tana yaqe.

"Yaya bari ba hadamaka tea" tafada tana dorawa kan dayan lockern dake dayan 6aren

"Nikuma na hadama fruits" inji sadeeq yana satan kallon baby dake antayamashi harara qasa qasa yana qumshe dariya.

Shidai ashraf bece komaiba sai binsu kawai dayake da kallo

Suna haka kofar ta bude ummy da Dr suka shigo.

"A'a? Tare kuka dawone?" Inji ummy tana qarasowa

"Eh wlh, zuwa nayi nai wanka na shirya nakoma na daukota" inji sadeeq yana dan sosa qeya.

"To yayi, tea kike hadawa?" Ta tambayi baby dake riqe da mug din shayin tana jujjuya tea din da spoon

"Eh ummy" tafada tana kallon Dr dake duba Ashraf.

Saida yagama yan gwaje gwajenshi sannan ya ciromashi magungunnanshi yace abashi yasha idan ya karya sannan ya ciremashi empty drip din yafita.

Bowl aka fara kawomashi yayi brush aciki don beda qarfin dazai tashi yaje toilet sannan aka bashi tea din don yasha.

Kauda kai yayi kawai yana satan kallon ummy qasa qasa.

Itama kauda kai tayi don tasan abinda yake nufi.

Ganin haka yasa jikinshi yin sanyi ganin kamar still tana fushi dashi.

Dagowa yayi yamiqa hannu zai amshi mug din ummy tarigashi amsa taja kujera ta zauna gabanshi ya debo a spoon tadan hura sannan takaimashi a baki.

Dagudu ya bude bakin yana bin fuskarta da kallo, harara ta gallamashi tana sakamashi spoon din abaki, murmushi ya su6ucemashi yayi saurin sunkuyar dakai yanayi.

Agefe kau baby sai antayama sadeeq harara take shikuma yana dariya marar sauti harda gwalo.

Haka ummy taita feeding dinshi harya qoshi sannan ta dago dan cewa sadeeq yabata magungunnan sai gani tayi yanata dariya marar sauti kamar sabon kamu.

Kallon baby tayi ganin direction dinta yake kallo taga ashraf ma ita take kallo wanda itama saida taga ummy zata waigo tayi saurin maida kallonta kan ashraf din.

Maida kallonta tayi ga sadeeq daya nutsu yanzu sai muzurai yake.

"Kaikuma lafiyarka?" Ta tambayeshi

Dan sosa kanshi yayi a kunyace

"Lfy lau ummy" yafada yana satar kallon baby dake qumshe dariyarta

"To allah yasa, miqomin magungunnan kekuma miqomin ruwa"

Duk juyawa sukayi su aiwatar da abinda tace baby sai danne dariyarta take.

Ballar mashi magungunnan tayi tabashi yasha yanajin sanyi a zuciyarshi don abubuwan datake mashi sun nuna tabar fushi dashi.

Excusing kanshi sadeeq yayi ya fita waje yana hararar baby ta gefen idanu itakuma tamashi gwalo ta gefen baki tana murmushi.

Juyowa dazatayi suka hada idanu da ashraf tayi saurin kauda kai gabanta na faduwa.

Ta6e baki kawai yayi shima ya janye idanunshi.

Riqesu akayi asibitin ganin yanayin rashin qarfin jikin nashi.

Da yamma saiga matar kawu zaharadini da shi kanshi kawun nashi sunzo ganinshi.

Anan ne suka ke6e da ummy tabashi labarin komai.

Yayi mammaki shima matuqa don shi rabonshi dajin ko labarin shamsu qolo tun suna mutunci da margayi Alhaji Auwal.

Saida suka tattauna sosai sannan suka tafi can gab da magrib.

Saudart kau a 6angarenta abin yayi affecting dinta itama sosai.

Takoma wata shiru daita ranta kodayaushe a jagule.

Duk yadda daddy yaso wartsakar daita yagaza don wannan karan takasa controlling din kanta.

Haka zata wuni a daki ba uhm ba uhm uhm, abinci saidai abiyota dashi kuma dakyar yake samu taci.

Idan ya takuramata da tambayoyi sai taita mashi kuka.

A cikin kwana biyu duk ta chanza tafita hayyacinta.

Saida yayi kwanaki uku sannan aka sallamashi daga asibiti, lokacin yaji sauqi sosai.

Direct gidan ummy suka wuce.

Sosai Ashraf ya wartsake saidai haryanzu cutarnan ta son Saudart babu abinda ya ragu saima abinda yaqaru.

Kwana daya da sallamoshi Kawu ibrahim ya diro garin kano don shima tuni labari yakaimasu a wudil.

Sudai su baby basusan dalilinshi nazuwa ba amma sunsan baya rasa nasaba da case din Auren Ashraf.

Ranar sun hadu da Kawu zahradini da ummy da kawu ibrahim sunyi heart-to-heart discussion akan yadda zasu 6illowa al'amarin.

*WASHEGARI*

Bayan azahar suka shirya dukkansu wato Kawu ibrahim, Kawu zahradini, Ummy, baby da Umma suka nufi gidan *MAMY*

💖💖💖💖💖💖💖💖

Jin ringing din doorbell yasa su dagowa daga cin abincin dasuke.

"Habeeb, jeka duba" inji Abba yana sipping din juice.

Ajiye fork din hannunshi yayi yana goge bakinshi da tissue sannan ya sauko daga dining din yanufi kofar.

Budewa yayi yayi tozali da maigadi

"Baba Audu" inji habeeb yana murmushi

"Na'am habibullahi" shima ya amsa yana washe baki

"Kashigo" yafada yana matsawa

"A'a dama baqi kukayi"

"Baqi? Ina?" Yafada yana leqa bayanshi.

"Suna can garage, suna neman iso ne" yabashi amsa

"Ok inazuwa" yakoma ciki yafadawa su mamy.

"Baqi? Jeka ka shigo dasu" inji mamy

"No, kaisu falon baqi seems harda maza tunda kikaga sun fara aikowa" inji Abba.

Wucewa habeeb yayi don aiwatarda yadda yace din.

Tare suka tafi da maigadin har parking space din.

Ganin baby cikinsu yasashi washe baki yana qarasawa wajensu da sauri

"Laa aunty?" Yafada yana washe baki

Shafa mashi kai tayi tana murmushi
"Sheikh habibullah" tafada cikin sigar tsokana kamar yadda tasaba kiranshi a dan zamanta gidan lokacin biki.

Murmushi yayi sannan yajuya gasu ummy ya duqa har qasa yana gaidasu.

Amsawa duk sukayi cikin jindadi ummy na kallonshi tana hango kammaninshi da saudart sosai.

Iso yayi musu suka bishi har falon baqi suna tafe baby na tsokanarshi shikuma yana murmushi don dama shi becika maganaba ko a lokacin data zauna gidan idan ta tsokaneshi saidai ya sunkuyar dakai yana murmushi hakan yasa take kiranshi sheikh ko ustaz.

Saida suka zauna sannan yajuya yafita, chan saiga aminullah yashigo da kayan motsa baki.

Shima yadda habeeb ya gaidasu haka shima yayi amma banda baby sai harararta dayayi yana murmushi.

"Inyee lallai ka riqu, ni bazaka gaidani ba?" Tafada tana harararshi don dama shine abokin fadanta.

Gwalo yaimata yafice da sauri ganin tayi kamar zata tashi.

Duk dariya sukasa don sosai yaran suka burgesu.

Ana haka sukaji sallamar Abba, hakan yasa suka maida kallonsu a qofar dukkansu suna amsa sallamar.

Cikeda nutsuwa da dattako Abba yashigo Mamy abayanshi suka shigo suna sakeyin sallama.

Amsawa duk suka sakeyi suna murmushi.

Saida suka zazzauna sannan aka shiga gaishe gaishe cikin girmamawa.

Sai anan Mamy ta lura da baby lokacin da itama ta zamo tana gaidasu.

"Laa kamar baby" inji mamy

Murmushi baby tayi
"Nice mamy"
Chapter 63 · 0% Book details