← Book details Asma'u Husnah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 60 OF 61

Sashe 60

Asma'u Husnah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hararar sa tayi ta ce,
"Eh ai ka min sannun, wallahi Yaa Aslam baka bina ahankali koda yaushe da karfi kake yi min,"

Ta fada tana turo baki. Dan tsotsar bakin yayi, sannan ya ce,
"kiyi hakuri ba laifaina bane,"

Mikewa tayi ta shiga dakin ta. Duba su Aayan tayi taga suna bacci.

Falo ta dawo ta  hau kan kujera tamike kafa. Biyo ta yayi yana mata tausa.

Ido ta lumshe, ya ce,
"Ba tin yau ba na fada miki a irin jinsin matan da kike. Ku kalilan ne, wannan yasa kike jin jiki a duk lokacin da nai kwana biyu ban kusance ki. bare yanxu wata uku fa. Ai dole. Ni kam naji dadi na. Na samu yar baiwa, wace ko da yaushe take a budurwar sabuwa."

Ido ta bude tana kai masa duka. Hannun ta ya kama, ya fara kissing na ta. Nan da nan jikin ta yai sanyi.

***************

Tsakanin Aslam da Asma'u zamane suke yinsa na kaunar juna da soyayya, yaransu sun girma sunyi wayo yanzu watansu 9 amma idan ka gansu zaka zaci sun shekara daya dan suna gudun ko ina.

Sosai suke Samu kulawa daga wajen iyayen su da Kakkanin su.

Dan in suka ga Momy ko Mami har wani shagwaba suke musu dan sun san abinda suke so shi za ai musu.

Zaman lafiya mai hade da soyayya da kaunar juna shi yake wanzuwa tsakanin Aslam da Asma'u.

Su Yan biyu na da shekara hudu Asma'u ta sake samun ciki.

A lokacin har an saka su a makaranta. Yara kyawawa da su abin sha'awa.

Wannan cikin alhamdulilah ba wani laulayi sai kwadayi.
Daga ta ce, kaza take so sai ta ce kaza.

Aslam kuwa yau shine dafa wancan soya wancan dan in ita tayi bata iya ciki.

Duk da haka tana kokari wajen kula da gidan da mai gidan ta.

Wannan karan ma yan biyu ta haifa duk mata. Akasa wa hassana Fatima, suke kiran ta Nabihah sai usaina Amina ake kiran ta da Nabinah.

********--------*********
*BAYAN SHEKARA 12*
Sanye take cikin wani tamfatsatsen leshi mai kyau baki da ja. sai kamshi take zubawa, falo ta fito babu kowa, ta tagar baya ta leka.

Hangon su tayi, Aslam na zaune rike da jarida. yana sanye da three quarter da yar karamar rigar shan iska. Sai  Aayan da Ayman suna buga ball. Sun saka kayan ball a jikin su. Da ka kalle su zaka ga kamar su daya da Aslam ba abinda suka baro shi. Kamar ya'yan labara bawa ko da yake baban su jinin larabawar ne.

Gefe kuma Nabibah da Nabinah ne, sai Autar su, Husnah wacce shekarar ta hudu, suke kiran ta  da Nawal.

Sun zaune suna duba littafi. Suna sanye da farin dogon wando da pink riga.

Kansu an musu parking da pink ribon. Kafar su ma pink cover shoe ne.

Can Aslam ya mike yai Cikin gida. yana shigowa ya hangota tsaye tana kallon yaransu ta window, bayanta yaje ya rungumeta akoda yaushe son Asma'u yake ji yana shigarsa sosai gata dai haihuwarta uku yaranta biyar amma har yau bata gundurarsa.

Juyowa tayi ta rumgume shi ita ma. kissing nasa ta fara ko ta ina. Ganin tsaiwar baza ta dauke su ba yasa ya dauketa cak a kafadarsa yayi cikin dakinsa da ita.

A Kan gado Ya kwantar da ita yafara yi mata wasanni masu rikitarwa.

Sosai suka shayar da juna su zumar soyayya tsadadda   sannan sukayi wanka suka fito, kwalliya suka sake tasaka yellowar atamfa shi kuma yasa blue kalar shadda.

Mayafi ya dauko mata suka fice daga gidan. Hanyar cikin gari taga sun nufa.

Kallon sa tayi tace,
"sai ina?"

Murmushi yayi ya ce
"Rufe idon ki!"

Idon ta ta rufe. Parking yayi ya fito ya bude mata site din da take.

Hannun ta ya kama ya ja ta. Dai da suka tsaya samnam ya ce,
"Open ur eyr my queen."

Ido ta bude, wani katon asibiti ta gani a gaban ta.

Kai ta daga, ta ga an rubuta *ASMAAAF CLINIC*

Ido ta bude ta ce,
"Means?"

Murmushi yayi ya ce,
" *ASMAAAF* Means, Asma'u, Suleiman, Muhammad Aslam, Amina, Asma'u, Fatima."

Rumgume shi tayi, ta ce,
"Yayi kyau!"

Murmushi yayi ya ce,
"Naki ne!"

Kallon sa tayi da mamaki ya ce,
"Kin wuce haka a guna Asma'u. Kece farin ciki na rayuwa ta cikar buri na. Banda abinda zan saka miki da shi sai dai ina miki addu'a Allah ya biya miki bukatun ki na alheri Allah ya hada mu a gidan Aljanna dani dake da yan uwan mu musulmai baki daya."

Rumgume shi ta yi sai kuma kuka, ba wanda ta tino sai da Dady da ya ke ce mata Ko baya raye ya bar mata farin ciki. Farin cikin ta kuma sune Aslam da Yaa Buhari da Mamin ta.

Lallai yau ta dada yadda Yaa Aslam da Yaa Buhari da Mamin ta sune farin cikin ta. Tana kara godiya ga Allah da ya mallaka mata Uwa kamar Mami.

Ya bata Yaya kamar Yaa Buhari mai burin ganin farin cikin ta. da kyautata mata kullum burin sa ganin ta bata da damuwa tana cikin farin ciki da walwala

Sannan ya bata Miji Yaya kamar Yaa Aslam wanda samun kamar sa sai an tona. Kullim.cikin kaunar ta da nuna kata kyautar ta yake. Bai da buri sai.na yaga ya kyautata mata. To.ita kuwa mai zatayi in ba addu'a gare au ba. Tare da Dadyn ta da Mami da Yayun nata.

Daga nan gida suka yi. Suna komawa ta shiga kitchen. Ita ce girka wancan dafa wancan.

Dan karamar walima ta hada musu a gidan aka ci aka sha akai hoto. Sannan ssuka zauna kamar yadda sukai akai hira anan kuma. A zauna ai karatun al kur'ani wanda duk dare kan a kwanta da asuba in an tashi sai anyi izifi daya gaba dayan su. daga nan  za ai ta bada labari bama Husnah da kullum sai ta basu labarin Dadyn ta.

Wanda suke ji daman yanan ja suma ya nuna musu tashi kalar soyayyar. Duk akn su sun san Dady kuma kullum akai sallah sai an masa addu'a Allah jikan sa.Nawal kuwa da ba wayo takan ce
"Ummu ki ka' ni gun Dadyn ki."

Sai dai Asma'u tai murmushi ta ce,
"Zamu je gun sa amman sai munyi aiki na gari a rayuwar mu. Dan Dady mutum kirki ne."

Abibda Dady ya roka ta cika masa dan yaran sun tashi da son sa da masa addu'a in kaji ana labarin Dadyn Asma'u sai kazata yana da rai wani abun.

Sun jima sannan kowa ya je ya kwanta.
Sai da tai wanka sannan ta fito daure da towel Aslam ne yashigo dakin.

Tsayawa yai abakin kofa ya harde hannu a kirji.
Kallon ta yake yadda kugun ta yake juyawa. murmushi tayi ya karasa wajen ta.

Turare take shafawa ya karasa,
kugunta ya rike yace
"shekaru goma sha uku kenan amman har yanzu kina nan a yadda kike, ko ma nace kinfi da dadi."

Ya karasa maganr yana rada mata wani abu.
Juyowa tayi ta daura hannun ta asaman kafadar sa, ta ce,
"Kai ma haka!"

Bakin su ya hada, ya fara bara wani irin zazzafan kiss.
Sai da yayi iya yin sa sannan ya dago ya ce,
"Kece Farin cikina Husnah"

Ido ta lumshe, tayi lamo a jikin sa.

Ya ce,
"Yau xamu samowa Nawal kani ko kanwa, tinda naga kamar tsarawa kike duk sai sunyu four to five years ko."

Duka ta kai masa tana shigewa jikin sa.  Nan ya shiga ga nuna mata zallar so.

*ALHAMDULILAH

*Dukkan godiya sun tabbata ga Allah da ya bani ikon rubuta wannan littafin lafiya. Ina kara godiya ga Allah.*

Duk abinda na rubuta ba dai dai ba Allah ubangiji ya yafe mun. Wanda na rubuta dai dai Allah ya bamu lada baki dayan mu. Ameen

Ina godiya gareki Mahaifiya ta abar alfahari.
Wannan littafin kacokan naki ne, uwa ta gari.

*Mahaifiyatah*
Banda kamarki a duniyarnan, Allah ya barni dake ya kuma kara miki tsawancin kwana, Allah ya biyaki ya saka miki da gidan Aljanna.
*Ameen*

*Mahaifinah*
Allah ya kara haskaka kabarinka mahaifina, Ya sadaka da rahamarsa
*Ameen*

*Kannenah*
Abin alfahari na. Allah ubangiji ya muku albarka. Allah ya kara mana zumunci.
*Ameen*
*My Nusy and Yasmeen (Autah)*

*Anty nah*
Anty Rash ina godiya gareki. Godiya ta baza ta taba karewa a gareki ba.
Ke daban ce. Allah ubangiji ya saka miki da mafificin alheri. Allah karawa iyayen ki lafiya da nisan kwana. Allah kawo miji na gari. Allah baki zuri'a daiyiba.
*Ameen*
soyayyar ki ta daban ce a cikin zuciyata. Allah ya bar mana zumunci.
*Ameen*

*Hajiya Nafisa,*
Maman mu maganin kukan mu Allah ya ja da rai Ya raya zuria
*Ameen*

*My Barrister*
Barrister Sady. Nagode sosai jin jina gareki. Allah ubangiji ya bar zumunci Allah ya biya miki dukkan bukatun ki na alheri.
*Ameen*

*HAJOW*
*Hakuri da juriya Online writer's*
Hajiya Nafisa (Momyn mu)
Alawiyya Ado (Antyn mu)
Sadiya Mohd (My Barrister)
Fatima Mohd Kibiya (Sisinah)
Maryam Ipteen (My swt Namesake)
Maryam kabir Bako (My sis)
Aina'u Gyaranya (Anty nahh)
Hauwa Mohd (My slimsmall)
Rukayya Zubair (Rukkybae)
Maryam Aliyu (My Namesake love)
Sumaiyya secret writer (sisinah)
Rukayya Isa
Nusaiiba Ummu Aysh
Amina Abdulmajeed (Mamah nah)
Sadiya Alhassan Ummu Affan
Hindatu
Sadiza Sardauna
Ameerah Gwadabe
dukkan ku ina kaunar ku Allah yabar zununci ina yin ku. Allah kara basira Ameen.

*Sauran marubuta*
Ina kaunar ku gaba daya. Allah ya kara mana hadin kai basira da ilimi.
*Ameen*
Na gaishe ku.

*Masoya nah*
A koda yaushe ina godewa Allah da ya bani masoya kamar ku.

Banda bakin godiya sai dai ina muku fatan alheri kamar yadda kuke sona da littafai na da labarai na nima ina son ku gaba daya.

Allah ubangiji ya sada mu a gidan Aljjana.
Kuna da yawa sosai.
Amman bazan manta da ku ba yan
*INDABAWA HAUSA NOVEL*
*HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITTERS*
*RASH KARDAM HAUSA NOVEL 1 & 2*
*RAZ NOVELLA*
*DOKIN KARFE WRITTERS FANS*
*KHALEESAT HAIDAR FCBUK*
*ZAMA NA AMANA 2*
*MARYAM SALISU MAI DALA*
*INA ZAKI DAMU FANS*
*SURAIYYAHMS FANS*
*ZEE MAKAWA NOVEL 2*
*HAUSA NOVEL*
*KASAITUTUN MATA*
*MARAHMAD CHATTING*
*ZUWAIRAT NOVEL FANS*
DA SAURAN SU DAI.
Chapter 60 · 0% Book details