Sashe 16
Asma'u Husnah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shi dai sai dai yai dariya dan son Asma'u daga Allah ne. Allah shi ya sa masa son ta a zuciyar sa yake jin bazai taba iya rayuwa ba ita ba.
Yasha fadawa Asma'u bazai taba barin ta ba ko ya ce,
"Ba zai taba daina son ta ko mata kishiya ba."
Duk kishin Asma'u sai dai ta ce,
"A'ah Yaa Aslam ka daina min irin wannan al kawarin Baka san me Allah ya tsara mana ba."
Shi in ta fadi haka wani lokacin har haushi yake ji.
Ita kuma tana tsoron ta sawa zuciyar ta haka Allah ya riga da ya tsara wani abun daban.
Tana son Aslam tana kishin sa kamar yadda shima yake son ta da kishin ta.
Dan yawancin wasu dogayen hijaban ta shi ya siyo mata dan zuwa makaranta. Daga doguwar riga sai hijabai su take sawa.
*********
Munasha ce zaune da kawar ta. Kallon ta kawar tayi ta ce,
"Wallahi ko mayya sai haka."
Munasha Ta ce,
"Da me fa?"
"Wannan yaron mana Aslam dan Allah ki kyale shi ki kama samarin harkar yanzu ba kudi basa shigo mana sosai saboda kin rage kula su wallahi."
Ido Munasha ta lumshe ta ce,
"A duniya mutum daya na taba so kuma shi insha Allahu sai na aure shi shine Nazir. Ko da na rasa shi Kuwa na rasa shi to bazan rasa Aslam ba wallahi Aslam ya min surar sa abar so ce ga kowacce mace da tasan 'da namiji. Kingan shi kuwa,"
Ta girgiza kai ta kwanta wallahi ba wanda yanzu nake sha'awa in ba shi ba. Shi kadai nake son nai tarayya da shi sai kuma my oga at top."
"Ni dai naji ki dauri kije gun Alhaji Usman kinsan babar harka ne, ko nawa kika nema zai baki kinga ko dasu masan yadda za ayi a jawo hankalin Aslam gareki."
Munasha ta ce,
"Kuma fa kin kawo magana wallahi dan Aslam zan je."
Ta mike ta fada wanka cikin minti biyar ta shirya cikin wani dan mini siket wanda ana gano kasan ta.
Sai yar half ves da ta saka ta bazo da gashin dakin ta gadon baya.
Tayi kwalliyar karuwai ta jefa cingum baki tana tauna sai kara take dashi.
Turare ta bade jikin ta dashi ta fita ta shiga mota sai guesthouse din Alhaji Usman.
Yasan da zuwan ta dan yafi sati yana jiran zuwan ta.
Yana falo a kwance yana trying number ta sai gata kamar daga sama.
Kan cinyar sa ta dane, tana masa wani kallo tana shafa shi.
Nan da nan ta burkita masa tunani tun a falo suka fara masha'ar su har suka koma daki.
A ranar a gidan ta kwana dan washe gari ma kin barin ta yayi ta tafi.
A kalla sai da tai sati biyu a gidan sannan ta tafi da milliyoyin kudi banda mota da ya mallaka mata.
Haka ta koma gidan ta da ta siya ta tadda Bulkis.
Mukkullin motarta ta da ta jefawa mata ta ce,
"Na bar miki."
Tsalle Bilki ta duka tana cewa da
"Da gaske!"
"Eh man! Kinsan ni yanzu na zama babar hajiya. Zan miki transper kudi. Amman ina son naje gida yau naga ya Baba take ciki."
Bilki ta ce,
"Sai yaushe kuma?"
"Sati daya zan yi."
Munasha ta bata amsa ta mike tana debo kayan da gida suka san ta dasu ta zuba a jaka ta shiga tai wanka ta saka wata kodadiyar atamfa dikin riga da zani.
Tana fitowa Bilki ta saka dariya ta ce,
"Amman fa da ace a haka kike da kin bada mata."
Dariya itama tayi ta ce,
"Ke dai bari baki ji yadda zanin nan ya dame ni ba."
"Wai dan Allah satin.kuwa zakiyi dan Allah kiyi kwana biyu ki dawo."
Bilkis tafada
Munasha ta ce,
"Aah bilki duk rashin iyaye na ina son su. Naje gun wani kato na yi sati biyu bare gun iyaye dan nayi sati. Aah wallahi."
Baki Bilkis ta tabe ta ce,
"Shikenan. Ki gaida su Baban."
"Zasu ji "
Ta dauki jakar ta tafi.
Napep ta tsayar ya kai ta har gida. Kannen ta sai murna suke sun san zasu samu dan abin tabawa.
Gun Babar ta taje ta gaishe ta. Baba sai addu'a take mata na samun nasarar karatu sannan ta gaida mahaifin ta.
Kayan abinci ta siyo musu bubun shikafa da katon din tafiya da macaroni.
Ta bawa Baba dubu goma Mama dubu biyar.
Daman ta fada musu tana dan siyar da abubuwa a makaranta wannan yasa suke zaton tana take samun kudi.
Duk abinda take akwai ta da ibada da biyayya ga iyayen ta.
Dan ita tazo gida ita ke yin komai haka zasu ta sa mata albarka.
Taje gidan su Nasir saurayin ta wajen kawar ta Rashida.
Anan Rashida take labarta mata Yaya ya kammala karatu sun rike shi zaiyi aiki shekara daya ya dawo.
Ba karamin murna Maimuna ta taya shi ba.
Anan suke hira da Rashida akan makaranta.
Rashida ta ce,
"Maimuna ki godewa Allah duk cikin mu ke ce kika samu jami'a mu duk sai kwaleji. Dan Allah ki dage ki fito da sakamako mai kyau. Kinga karatun nan shine gatan mu da na iyayen mu da ya'ya mu. In muka samu aiki zamu tai makawa iyayen mu. Ya'yan mu kuma mu koya musu. Dan Allah ki dage kinga sauran shekara daya da rabi kigama kinji."
Sosai Maimuna taji fadan Rashida kuma tasa a ranta zata tsaya tayi karatun ta gama lafiya.
Satin ta daya ta fara shirin komawa ita kan ta ji take kamar kar ta tafi amman kuma tana so taje ta tana din rayuwar ta tanan gaba.
Sannan tasa a ranta wannan karan zata tsaya ta fuskanci rayuwa tai karatu dan tasan tabbas karatun nan shine gatan ta.
Karuwan ci na dan lokaci ne in kuwa kana da ilimi ka samu aiki kana samun kobo da naira.
Da kuka ta tafi kannen ta suma sai kuka suke.
Tinda Munasha ta koma makaranta take karatu sosai.
Duk wanda tasan yana da kokari tai ta bibiyar sa kenan su kuma suna wulakanta ta suna zaton ba da gaske take ba.
Sai da suka ga da gaske take sannan suke koya mata.
Harka da maza kuwa tanayi jifa jifa amman yanzu kudi take tarawa bata fiya shaye shaye da siyi banza siyi wofi ba.
Kawayen ta da dama sun ja baya da ita dan ta rage kashe kudi da siyan kayan maye.
Bilkisu ce kawai suke tare itama kullum sai ta ziga ta amman bata dauka.
Wani lokacin sai taji kamar ta dauka sai kuma ta fasa.
Yau ta kama Asabar tinda Asma'u taje makaranta ta dawo ta shige daki take bacci
Yaa Aslam ya kira fin sau goma amman bata ji ba dan a silent wayar take.
Ba ita ta tashi ba sai hudu saura tin sha biyu da rabi take abu daya.
Wanka ta shiga tayi tayo alwala duk da bata sallah tana yin alwala dan alwala tana da tasiri a jikin dan adam.
Mai ta shafa ta hau kwalliya sai kace wacce zata biki.
Sosai ta fente fuskar ta da yake Asma'u akwai son kwalliya wannan yasa taje ta koya to makaranta ke hanata zama tayi.
Wani Golding codeless ta dauko ta saka.
Dinkin doguwar riga daga sama ta kamata daga kasa ta bude.
Mayafi ta dauko maroon kala, karami ta yafa jikin ta ta hade turaruka sannan ta dauki wani maroon kalar sandal ta saka.
Turare ta kuma yin wanka dashi sannan tafi daga dakin ta.
Tafiya take a hankali har ta karasa dakin Yaa Buhari.
Firij ta bude ta dauki robar ice cream din ta, ta sauka kasa.
Tafiya take a hankali tana sauka idon ta na kan wayar ta da taga missed din Yaa Aslma.
Har ta karasa ta zauna sannan ta dago kanta.
Wa zata gani!!!???
*Ina mika sakon gaisuwa ga duk masoya na. Allah ubangiji ya kara kauna da zuminci. Dukkan ku ina yin ku.*
*Nagode*
*INDABAWA*
[1/18, 14:15] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR*
*Asma'u Husnah*
Na *Maryam S Indabawa*
*Mans*
🌐 *HAJOW* 🌐
*Hakuri da Juriya Online writers*
*Gidan Amanci da albarka*
Dedicated to *My Lovelly Momy*
Allah ya gafarta miki duk kura kuren ki. Allah ya dada tsawan kwana ya sa Aljanna makoma.
*Ameen!*
86-90
*_*Manzon Allah(ﷺ)* Yana Cewa: *"Lallai Abin Sani Maji6incinsa Shine: Allah da Kuma Muminai Na Kwarai"* (Bukhari da Muslim)._*
Dagowa tayi wa zata gani. Ido ta kara budewa tana kare masa kallo.
Sanye yake cikin Shadda Cream kala, kansa ba hula gashin nan ya kwanta luf luf.
Idon sa sun kara girma da haske sai hancin sa da ya kara fito wa. Dan karamin bakin sa ya kara zama pink sai sajen dake gefen fuskar sa da ya kara fito da kyan sa.
Murmushi yake mata hakoran sa farare suka bayyana hadi da lobawar kumatun sa.
Mikewa tayi tana kallonsa sannan ta karasa gun sa. Hannun sa ta kama. Sai kuma ta saki murmushi ta ce,
"Wai mafarki nake ne?"
Hannun ta ya kamo yayi saitin bakin sa ya zura sannan ya dan ciza.
Da sauri ta kwace hannun tana yarfewa ta ce,
"Yaa Aslam da zafi fa."
Murmushi yayi ya kamo hannun yana hura mata iskar bakin sa.
Ido ta lumshe ya ce,
"To ai naga baki yadda ni din bane."
Murmushi tayi ta bude ido. Ya ce,
"Missed nawa kika gani tinda zan taho nake neman number ki amman ba a dauka ba."
"Wallahi sai yanzu na gani. Bacci nayi."
Ta bashi amsa tana zuba masa ido.
Shima idon ya zuba mata, sun dau mintina. a Haka kowa ya kasa daina kallon dan uwan sa.
Kamar yadda Asma'u tayi kyau a idon sa ita ma haka taga kyan sa.
Hannu ya dago yayi wajen idon ta dashi yace,
"Wannan da wannan da wannan suna burge ni."
Ya nuna idon ta da hancin ta da dan karamin bakin ta.
Dariya tayi ta ce,
"Su kadai ko shikenan tinda su kake so ka cire na bar maka."
Murmushi yayi ya ce,
"To ai kinga wanda na fiso gaba dayan ta nan."
Ya nuna ta. Dariya tayi ta yi kasa da kanta.
Yasha fadawa Asma'u bazai taba barin ta ba ko ya ce,
"Ba zai taba daina son ta ko mata kishiya ba."
Duk kishin Asma'u sai dai ta ce,
"A'ah Yaa Aslam ka daina min irin wannan al kawarin Baka san me Allah ya tsara mana ba."
Shi in ta fadi haka wani lokacin har haushi yake ji.
Ita kuma tana tsoron ta sawa zuciyar ta haka Allah ya riga da ya tsara wani abun daban.
Tana son Aslam tana kishin sa kamar yadda shima yake son ta da kishin ta.
Dan yawancin wasu dogayen hijaban ta shi ya siyo mata dan zuwa makaranta. Daga doguwar riga sai hijabai su take sawa.
*********
Munasha ce zaune da kawar ta. Kallon ta kawar tayi ta ce,
"Wallahi ko mayya sai haka."
Munasha Ta ce,
"Da me fa?"
"Wannan yaron mana Aslam dan Allah ki kyale shi ki kama samarin harkar yanzu ba kudi basa shigo mana sosai saboda kin rage kula su wallahi."
Ido Munasha ta lumshe ta ce,
"A duniya mutum daya na taba so kuma shi insha Allahu sai na aure shi shine Nazir. Ko da na rasa shi Kuwa na rasa shi to bazan rasa Aslam ba wallahi Aslam ya min surar sa abar so ce ga kowacce mace da tasan 'da namiji. Kingan shi kuwa,"
Ta girgiza kai ta kwanta wallahi ba wanda yanzu nake sha'awa in ba shi ba. Shi kadai nake son nai tarayya da shi sai kuma my oga at top."
"Ni dai naji ki dauri kije gun Alhaji Usman kinsan babar harka ne, ko nawa kika nema zai baki kinga ko dasu masan yadda za ayi a jawo hankalin Aslam gareki."
Munasha ta ce,
"Kuma fa kin kawo magana wallahi dan Aslam zan je."
Ta mike ta fada wanka cikin minti biyar ta shirya cikin wani dan mini siket wanda ana gano kasan ta.
Sai yar half ves da ta saka ta bazo da gashin dakin ta gadon baya.
Tayi kwalliyar karuwai ta jefa cingum baki tana tauna sai kara take dashi.
Turare ta bade jikin ta dashi ta fita ta shiga mota sai guesthouse din Alhaji Usman.
Yasan da zuwan ta dan yafi sati yana jiran zuwan ta.
Yana falo a kwance yana trying number ta sai gata kamar daga sama.
Kan cinyar sa ta dane, tana masa wani kallo tana shafa shi.
Nan da nan ta burkita masa tunani tun a falo suka fara masha'ar su har suka koma daki.
A ranar a gidan ta kwana dan washe gari ma kin barin ta yayi ta tafi.
A kalla sai da tai sati biyu a gidan sannan ta tafi da milliyoyin kudi banda mota da ya mallaka mata.
Haka ta koma gidan ta da ta siya ta tadda Bulkis.
Mukkullin motarta ta da ta jefawa mata ta ce,
"Na bar miki."
Tsalle Bilki ta duka tana cewa da
"Da gaske!"
"Eh man! Kinsan ni yanzu na zama babar hajiya. Zan miki transper kudi. Amman ina son naje gida yau naga ya Baba take ciki."
Bilki ta ce,
"Sai yaushe kuma?"
"Sati daya zan yi."
Munasha ta bata amsa ta mike tana debo kayan da gida suka san ta dasu ta zuba a jaka ta shiga tai wanka ta saka wata kodadiyar atamfa dikin riga da zani.
Tana fitowa Bilki ta saka dariya ta ce,
"Amman fa da ace a haka kike da kin bada mata."
Dariya itama tayi ta ce,
"Ke dai bari baki ji yadda zanin nan ya dame ni ba."
"Wai dan Allah satin.kuwa zakiyi dan Allah kiyi kwana biyu ki dawo."
Bilkis tafada
Munasha ta ce,
"Aah bilki duk rashin iyaye na ina son su. Naje gun wani kato na yi sati biyu bare gun iyaye dan nayi sati. Aah wallahi."
Baki Bilkis ta tabe ta ce,
"Shikenan. Ki gaida su Baban."
"Zasu ji "
Ta dauki jakar ta tafi.
Napep ta tsayar ya kai ta har gida. Kannen ta sai murna suke sun san zasu samu dan abin tabawa.
Gun Babar ta taje ta gaishe ta. Baba sai addu'a take mata na samun nasarar karatu sannan ta gaida mahaifin ta.
Kayan abinci ta siyo musu bubun shikafa da katon din tafiya da macaroni.
Ta bawa Baba dubu goma Mama dubu biyar.
Daman ta fada musu tana dan siyar da abubuwa a makaranta wannan yasa suke zaton tana take samun kudi.
Duk abinda take akwai ta da ibada da biyayya ga iyayen ta.
Dan ita tazo gida ita ke yin komai haka zasu ta sa mata albarka.
Taje gidan su Nasir saurayin ta wajen kawar ta Rashida.
Anan Rashida take labarta mata Yaya ya kammala karatu sun rike shi zaiyi aiki shekara daya ya dawo.
Ba karamin murna Maimuna ta taya shi ba.
Anan suke hira da Rashida akan makaranta.
Rashida ta ce,
"Maimuna ki godewa Allah duk cikin mu ke ce kika samu jami'a mu duk sai kwaleji. Dan Allah ki dage ki fito da sakamako mai kyau. Kinga karatun nan shine gatan mu da na iyayen mu da ya'ya mu. In muka samu aiki zamu tai makawa iyayen mu. Ya'yan mu kuma mu koya musu. Dan Allah ki dage kinga sauran shekara daya da rabi kigama kinji."
Sosai Maimuna taji fadan Rashida kuma tasa a ranta zata tsaya tayi karatun ta gama lafiya.
Satin ta daya ta fara shirin komawa ita kan ta ji take kamar kar ta tafi amman kuma tana so taje ta tana din rayuwar ta tanan gaba.
Sannan tasa a ranta wannan karan zata tsaya ta fuskanci rayuwa tai karatu dan tasan tabbas karatun nan shine gatan ta.
Karuwan ci na dan lokaci ne in kuwa kana da ilimi ka samu aiki kana samun kobo da naira.
Da kuka ta tafi kannen ta suma sai kuka suke.
Tinda Munasha ta koma makaranta take karatu sosai.
Duk wanda tasan yana da kokari tai ta bibiyar sa kenan su kuma suna wulakanta ta suna zaton ba da gaske take ba.
Sai da suka ga da gaske take sannan suke koya mata.
Harka da maza kuwa tanayi jifa jifa amman yanzu kudi take tarawa bata fiya shaye shaye da siyi banza siyi wofi ba.
Kawayen ta da dama sun ja baya da ita dan ta rage kashe kudi da siyan kayan maye.
Bilkisu ce kawai suke tare itama kullum sai ta ziga ta amman bata dauka.
Wani lokacin sai taji kamar ta dauka sai kuma ta fasa.
Yau ta kama Asabar tinda Asma'u taje makaranta ta dawo ta shige daki take bacci
Yaa Aslam ya kira fin sau goma amman bata ji ba dan a silent wayar take.
Ba ita ta tashi ba sai hudu saura tin sha biyu da rabi take abu daya.
Wanka ta shiga tayi tayo alwala duk da bata sallah tana yin alwala dan alwala tana da tasiri a jikin dan adam.
Mai ta shafa ta hau kwalliya sai kace wacce zata biki.
Sosai ta fente fuskar ta da yake Asma'u akwai son kwalliya wannan yasa taje ta koya to makaranta ke hanata zama tayi.
Wani Golding codeless ta dauko ta saka.
Dinkin doguwar riga daga sama ta kamata daga kasa ta bude.
Mayafi ta dauko maroon kala, karami ta yafa jikin ta ta hade turaruka sannan ta dauki wani maroon kalar sandal ta saka.
Turare ta kuma yin wanka dashi sannan tafi daga dakin ta.
Tafiya take a hankali har ta karasa dakin Yaa Buhari.
Firij ta bude ta dauki robar ice cream din ta, ta sauka kasa.
Tafiya take a hankali tana sauka idon ta na kan wayar ta da taga missed din Yaa Aslma.
Har ta karasa ta zauna sannan ta dago kanta.
Wa zata gani!!!???
*Ina mika sakon gaisuwa ga duk masoya na. Allah ubangiji ya kara kauna da zuminci. Dukkan ku ina yin ku.*
*Nagode*
*INDABAWA*
[1/18, 14:15] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR*
*Asma'u Husnah*
Na *Maryam S Indabawa*
*Mans*
🌐 *HAJOW* 🌐
*Hakuri da Juriya Online writers*
*Gidan Amanci da albarka*
Dedicated to *My Lovelly Momy*
Allah ya gafarta miki duk kura kuren ki. Allah ya dada tsawan kwana ya sa Aljanna makoma.
*Ameen!*
86-90
*_*Manzon Allah(ﷺ)* Yana Cewa: *"Lallai Abin Sani Maji6incinsa Shine: Allah da Kuma Muminai Na Kwarai"* (Bukhari da Muslim)._*
Dagowa tayi wa zata gani. Ido ta kara budewa tana kare masa kallo.
Sanye yake cikin Shadda Cream kala, kansa ba hula gashin nan ya kwanta luf luf.
Idon sa sun kara girma da haske sai hancin sa da ya kara fito wa. Dan karamin bakin sa ya kara zama pink sai sajen dake gefen fuskar sa da ya kara fito da kyan sa.
Murmushi yake mata hakoran sa farare suka bayyana hadi da lobawar kumatun sa.
Mikewa tayi tana kallonsa sannan ta karasa gun sa. Hannun sa ta kama. Sai kuma ta saki murmushi ta ce,
"Wai mafarki nake ne?"
Hannun ta ya kamo yayi saitin bakin sa ya zura sannan ya dan ciza.
Da sauri ta kwace hannun tana yarfewa ta ce,
"Yaa Aslam da zafi fa."
Murmushi yayi ya kamo hannun yana hura mata iskar bakin sa.
Ido ta lumshe ya ce,
"To ai naga baki yadda ni din bane."
Murmushi tayi ta bude ido. Ya ce,
"Missed nawa kika gani tinda zan taho nake neman number ki amman ba a dauka ba."
"Wallahi sai yanzu na gani. Bacci nayi."
Ta bashi amsa tana zuba masa ido.
Shima idon ya zuba mata, sun dau mintina. a Haka kowa ya kasa daina kallon dan uwan sa.
Kamar yadda Asma'u tayi kyau a idon sa ita ma haka taga kyan sa.
Hannu ya dago yayi wajen idon ta dashi yace,
"Wannan da wannan da wannan suna burge ni."
Ya nuna idon ta da hancin ta da dan karamin bakin ta.
Dariya tayi ta ce,
"Su kadai ko shikenan tinda su kake so ka cire na bar maka."
Murmushi yayi ya ce,
"To ai kinga wanda na fiso gaba dayan ta nan."
Ya nuna ta. Dariya tayi ta yi kasa da kanta.