Sashe 54
Asma'u Husnah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ni dai Yaa Aslam ka kyale ni, wallahi nasan ba sona kake ba. Ka rabu da rayuwa ta dan Allah. Ka koma gun wacce kake so har ka aura. Ni nasan daman Sir ya gama cutata ne da ya bar maka ni. Baza ka taba ganin daraja ta ba."
Ta fada yana kuka mai tsuma zuciya.
Kallon mamaki ya tsaya yi mata, kasa jurar jin kukanta yayi mai tsuma zuciya, duk ya rikice, ya rasa ya zaiyi, ya fara magana cikin sanyin murya.
"waya fad'a miki ina da wadda nakeso bayanke? Wlhy ke kad'ai nakeso Asma'u, ban ta'bason wata d'iya mace a rayuwa ta ba kamar yanda nake sonki, ke ma kin sani ban taba soyayya da wata bayan ke ba. ki bani dama in bayyana miki irin son da nake miki."
Da 'karfi tace
"baka so na Yaa Aslam, baka so na. Ka koma wajen matar ka da kake so, ni ka kyale ni, nasan dan kaji zan aure ne kazo to kaji dadi da ka raba ni da mai so na."
Duk ya rikirkice, ya ce,
'Wallahi banda burin 'bata miki rai 'kanwata, don Allah ki fahimceni, wallahi ina sonki, naayi miki alkawarin faranta miki har iyakar rayuwatah."
Hannu biyu ta sanya ta rufe kunnenta tace
"Bana sonji Yaa Aslam don Allah ka 'kyale zuciyatah ta huta hakanan, duk abinda zakamin don kasan ina sonka ne...."
Kasa karasa maganar tayi ta kifa kanta akan kujera taci gaba da shesshe'kar kuka.
Sosai yake jin kukanta a jikinshi, ya rasa yanda zai rarrasheta, hannu ya saka ya d'agota a jikinshi, da sauri ta fara 'ko'korin zamewa, anma tsam ya rumgumeta a 'kirjinshi sosai, har saida tayi 'kara saboda ba ri'kon wasa ya mata ba,.
Kuka kawai take dan bata da wani 'karfin da zata kwaci kanta.
Aslam kuwa idonshi lumshe, ko lallashinta ya kasayi, duk jikinta ya saki ta fara rage kukan, sun dad'e a haka, kafin ya sassauta mata ri'kon ta zame ta kwanta a hankali ta rufe idonta, shima mi'kewa yayi ya fita ya barta.
Sai da ya fita daga d'akin kuma ta fashe da kukan takaici, Aslam yaa riga ya gama da ita tunda ya gane mahaukacin son da take mishi, kuka take sosai a ranta tana addu'ar Allah ya rage mata son sa
Ina son ganin comment
Follow nd vote @ Msindabawa
*MS Indabawa*
[1/18, 14:40] Maryam S Indabawa🥰: LABARIN RAYUWAR*
*Asma'u Husnah*
Part *2*
Na *Maryam S Indabawa*
*Mans*
?? *HAJOW* ??
Dedicated to *My lovelly Mum*
*111-115*
Da dare da wuri ta mishi girki kafin ya dawo, ta shige d'aki tana gama sallolinta tayi shirin kwanciya, doguwar riga ta saka iyakar gwiwa pink, mai santsi dabin jiki, tayi kyau sosai, mukulli ta saka ta rufe d'akinta ta haye gado tayi addu'a ta kwanta.
Aslam kuwa tinda ya fita da yamma yaje gidan Momy. Tambayar da Asma'u tayi ya amsa da tana lafiya.
Daga nan Asibiti ya biya, sai da akai magariba ya taho gida.
Yana driving ne amma zuciyar sa na can tunanin halin da Asma'u take ciki.
Bai son damuwar ta bai son bacin ranta. Dole ya san yadda zai dawo mata da farin cikin ta.
Sanda ya isa gidan kamar yanda ya zata, tayi barci ko motsinta bai jiyo ba, d'akinshi ya shiga ya watsa ruwa yayi shirin kwanciya sannan ya fito ya zauna yaci abincin data girka mishi, hankalinshi duk naa wurinta harya gama.
A hankali ya murd'a Kofar d'akinta, jinta yayi a rufe, kamar yadda ya zata. komawa dakinshi yayi ya dauko makullanshi yazo ya bude a hankali ya tura kofar ya shiga.
K'arasawa yayi inda take, kasa d'auke idonshi yayi a kanta, a fili yake furta,
"Alhmdlh, Allah nagode maka da ka mallaka min Asma'u. Ya Allah ka nunamin ranar da Asma'u zata gane irin son da nake mata," tsugunawa yayi saitin fuskarta yana tunanin yanzu da suna zaman lafiya ne zai kwanta da ita ne a kirjinshi yanajin lallausar fatar ta, shi kadai yasan yanayin da yakeji idan yana tare da Asma'u. Abinda ya dade yana fatan ya faru kenan.
Hannunshi yakai ya shafi fuskarta, ya d'aura hannunshi saman lebanta, bakin sa ya kai kan nata ya dan sumbace ta.
Mikewa yayi ya rufe kofar ya koma dakin sa.
Alwala ya kuma yi. Dan Kusan kwanan zaune yayi yana fad'ama Allah damuwarshi.
Washe da wuri ta gama masa duk abinda zai bukata sannan ta koma daki.
Sai da ta tabbata ya fita sannan ta fito ta gyara gidan
Daki ta koma tai wanka tai ado sosai a jikin ta da fuskar ta.
Bata san dalili ba yau dai ta tashi da farin ciki da son yin kwalliya.
Ta zauna ta karya. Kitchen ta shiga ta fara hada hadar abincin rana.
Fried rice tayi wacce ta wadata da hanta, tayi farfesun naman kaji, tayi cislow.
Cake ta kwaba tai baking sannan ta yi meat pie.
A daining ta jere su tayiwa wajen ado mai kyau.
Kitchen ta koma ta hada lemon kwakwa da madara ta saka dabinoi ta sa a firij.
Wanka ta kara tai Kwalliya sosai kamar amarya. ta saka wani papper less mai kyau da tsada wanda duk jikin sa stones ne da suka kara masa kyau sai daukar ido yake..
Red and black kala. Sosai tai kwalliya ta feshe jikin ta da turare mai kamshi sosai.
Dan kunne da sarka ta saka jajjaye, Babban falo ta koma ta zauna tana kallo.
Wajen karfe uku ta jiyo sallamar sa, amsawa tayi ba tare da ta dago ta kalle shi ba.
Shi kuwa tin da ya shigo ya zuba mata ido, dan yaga tai masa kyau.
Karasawa inda take ya zauna a gefen ta. Dagowa tayi ta zura masa manya manyan idon ta masu dimauta shi, kallon sa ta tsaya yi, sosai yayi kyau.
Yana sanye cikin Sky blue din shadda yai kyau da shi.
Fatar sa ta dada yin fresh, ya dada haske kyaun sa ya kara fitowa jikin sa ya murje. Ya dawo cikaken balaraben sa
Iska ya hura mata, wannan yasa tai saurin dawo wa cikin hayyacin ta.
Kai ya daga mata alamar 'Menene?'
Kai ta dauke daga kallon sa. Hannun ta ya kamo wanda tai masa ado da jan lalle.
Saitin bakin sa yayi da hannun ya sumbata. Zai yi magana kenan yaji ana knocking.
"Waye?"
Ya tambaya.
Mai gadi ne ya ce,
"Nine! Bakuwa kayi."
"Cene ta shigo."
Ya fada yana kallon Asma'u.
Mikewa yayi ya ce, bari na shiga na watsa ruwa.
Yana shiga tana shigowa ba kowa bace face Pretty.
Asma'u da bata san ta ba ta amsa mata sallamar da tayi tana mikewa.
Wajen zama ta nuna mata sannan itama ta zauna.
Gaisawa sukai, Pretty ta ce,
"Baki sanni ba. Ko Aslam yana nan?"
Kai Asma'u ta daga ta ce,
"Eh amman yanzu ya shiga wanka."
Ta mike ta kawo mata lemo da snack. Lemon kadai ta dan sha ta zauna jiran sa.
Sai kallon Asma'u take a ranta ta ce,
"Ashe haka Asma'un take ahh lallai doke Aslam yaso ta. Duk da yarinya ce amman tana da sura mai kyau. Allah sarki na cutar dake.'
Duk wannan maganar a zuciya take yin ta.
Sai da tai minti ashirin Asma'u taga Aslam bai shigo ba ta mike ta shiga ciki.
Yana gaban mudubi Daure da towel a kugun sa, yana ta kalkale jikin sa, Asma'u ta shiga.
Ganin sa a haka yasa tai saurin juya baya.
Kallon ta yayi yai murmushi, magana ta fara yi cikin rawar murya,
"Kayi bakuwa ana jiran ka."
Ta fada, tafiya ta fara yai saurin kamo hannun ta ya juyo da ita.
Kin juyowa tayi, shi ya juyo da ita da hannun sa.
Ido tai saurin runtsewa. Murmushi yayyi ya jata kan gado.
Zaunar da ita yayi ya saka kayansa. Sai da ya gama ya ce,
"To matsoraciyya na gama bude idon."
A hankali ta fara bude idon ganin ya saka kayan yasa ta bude su.
Mikewa tayi ta ce,
"Yaya tana jiran ka fa."
"Na sani."
Hanya tayi zata fita ya ce,
"Zo ki gyara ni man."
Ya fada yana mika mata turare.
Amsa tayi ta fefesa masa. Ta ajiye. tafiya ta fara ya ce,
"Oh!"
Juyowa tayi, ya ce,
"Comb my hair man!"
Amsar comb din tayi ta taje masa kai. Tana direwa tayi waje.
Bayan ta yabi, suka fita. Hannun ta ya kama, suka jera har zuwa falo.
Da yake Pretty ta juya ma hanyar da suke fitowa baya bai gane ita bace
Zagayawa yayi ya zauna ba tare da ya kalli bakuwar ta shi ba.
Asma'u kuma tayi hanyar sashen sa. Saboda taga yai bakuwa.
Dagowa yayi ya ce,
"Sann....."
Bai karasa fadin abinda zai fada ba yai saurin mikewa.
"Me kika zo min a gida?"
Ya fada cikin tsawa. Wanda ya janyo hankalin Asma'u.
Juyowa tayi ta tsaya kallon sa. Lokaci daya ya canja.
Fuskar sa tai jajir, da Hannu ya nuna mata kofa alamar tazo ta fice.
Zubewa tayi a kasa tana rokar sa ya tsaya ya saurare ta amman ya kafe akan sai ta fita.
Asma'u ce ta koma dakin ta kama hannun sa ta ce,
"Haba Yaa Aslam ka tsaya man."
Hannun sa ya kwace ya ce,
"Bazan tsaya naji ba. ta fice min da gani."
Kallon sa Asma'u tayi taga ransa a bace yake sosai.
Hannun Pretty ta kama zaunar da ita.
Wajen Aslam ta karasa shima ta zaunar da shi.
Kansa ta shafa masa har ya samu ya sauke ajiyar zuciya.
Kallon sa tayi, ta ce,
"Kiyi hakuri duk da bansan me ya faru a tsakanin ku ba amman ka saurare ta"
Ta fada tana mikewa. Hannun ta ya kamo, ya zaunar.
Kallon sa tayi ya gyada mata kai alamar ta zauna.
Zaman tayi, ya ce,
"Na baki minti biyu ki fadi abinda ya kawo ki, ki bar min gida na."
"Hakuri na zo na baka!"
Ta fada cikim sanyin murya.
"Indai hakuri ne ki tashi ki tafi bana bukata kara ganin kki a rayuwa ta. Rayuwar da nai dake a baya ma ban san nayi ba."
"Nasan da haka Aslam amman ka yafe min, nazo na bawa Asma'u hakuri ne."
Kallon ta Asma'u tayi cikin rashin sani ta ce
"Ni kuma? Ni da ban sanki ba."
Ta fada yana kuka mai tsuma zuciya.
Kallon mamaki ya tsaya yi mata, kasa jurar jin kukanta yayi mai tsuma zuciya, duk ya rikice, ya rasa ya zaiyi, ya fara magana cikin sanyin murya.
"waya fad'a miki ina da wadda nakeso bayanke? Wlhy ke kad'ai nakeso Asma'u, ban ta'bason wata d'iya mace a rayuwa ta ba kamar yanda nake sonki, ke ma kin sani ban taba soyayya da wata bayan ke ba. ki bani dama in bayyana miki irin son da nake miki."
Da 'karfi tace
"baka so na Yaa Aslam, baka so na. Ka koma wajen matar ka da kake so, ni ka kyale ni, nasan dan kaji zan aure ne kazo to kaji dadi da ka raba ni da mai so na."
Duk ya rikirkice, ya ce,
'Wallahi banda burin 'bata miki rai 'kanwata, don Allah ki fahimceni, wallahi ina sonki, naayi miki alkawarin faranta miki har iyakar rayuwatah."
Hannu biyu ta sanya ta rufe kunnenta tace
"Bana sonji Yaa Aslam don Allah ka 'kyale zuciyatah ta huta hakanan, duk abinda zakamin don kasan ina sonka ne...."
Kasa karasa maganar tayi ta kifa kanta akan kujera taci gaba da shesshe'kar kuka.
Sosai yake jin kukanta a jikinshi, ya rasa yanda zai rarrasheta, hannu ya saka ya d'agota a jikinshi, da sauri ta fara 'ko'korin zamewa, anma tsam ya rumgumeta a 'kirjinshi sosai, har saida tayi 'kara saboda ba ri'kon wasa ya mata ba,.
Kuka kawai take dan bata da wani 'karfin da zata kwaci kanta.
Aslam kuwa idonshi lumshe, ko lallashinta ya kasayi, duk jikinta ya saki ta fara rage kukan, sun dad'e a haka, kafin ya sassauta mata ri'kon ta zame ta kwanta a hankali ta rufe idonta, shima mi'kewa yayi ya fita ya barta.
Sai da ya fita daga d'akin kuma ta fashe da kukan takaici, Aslam yaa riga ya gama da ita tunda ya gane mahaukacin son da take mishi, kuka take sosai a ranta tana addu'ar Allah ya rage mata son sa
Ina son ganin comment
Follow nd vote @ Msindabawa
*MS Indabawa*
[1/18, 14:40] Maryam S Indabawa🥰: LABARIN RAYUWAR*
*Asma'u Husnah*
Part *2*
Na *Maryam S Indabawa*
*Mans*
?? *HAJOW* ??
Dedicated to *My lovelly Mum*
*111-115*
Da dare da wuri ta mishi girki kafin ya dawo, ta shige d'aki tana gama sallolinta tayi shirin kwanciya, doguwar riga ta saka iyakar gwiwa pink, mai santsi dabin jiki, tayi kyau sosai, mukulli ta saka ta rufe d'akinta ta haye gado tayi addu'a ta kwanta.
Aslam kuwa tinda ya fita da yamma yaje gidan Momy. Tambayar da Asma'u tayi ya amsa da tana lafiya.
Daga nan Asibiti ya biya, sai da akai magariba ya taho gida.
Yana driving ne amma zuciyar sa na can tunanin halin da Asma'u take ciki.
Bai son damuwar ta bai son bacin ranta. Dole ya san yadda zai dawo mata da farin cikin ta.
Sanda ya isa gidan kamar yanda ya zata, tayi barci ko motsinta bai jiyo ba, d'akinshi ya shiga ya watsa ruwa yayi shirin kwanciya sannan ya fito ya zauna yaci abincin data girka mishi, hankalinshi duk naa wurinta harya gama.
A hankali ya murd'a Kofar d'akinta, jinta yayi a rufe, kamar yadda ya zata. komawa dakinshi yayi ya dauko makullanshi yazo ya bude a hankali ya tura kofar ya shiga.
K'arasawa yayi inda take, kasa d'auke idonshi yayi a kanta, a fili yake furta,
"Alhmdlh, Allah nagode maka da ka mallaka min Asma'u. Ya Allah ka nunamin ranar da Asma'u zata gane irin son da nake mata," tsugunawa yayi saitin fuskarta yana tunanin yanzu da suna zaman lafiya ne zai kwanta da ita ne a kirjinshi yanajin lallausar fatar ta, shi kadai yasan yanayin da yakeji idan yana tare da Asma'u. Abinda ya dade yana fatan ya faru kenan.
Hannunshi yakai ya shafi fuskarta, ya d'aura hannunshi saman lebanta, bakin sa ya kai kan nata ya dan sumbace ta.
Mikewa yayi ya rufe kofar ya koma dakin sa.
Alwala ya kuma yi. Dan Kusan kwanan zaune yayi yana fad'ama Allah damuwarshi.
Washe da wuri ta gama masa duk abinda zai bukata sannan ta koma daki.
Sai da ta tabbata ya fita sannan ta fito ta gyara gidan
Daki ta koma tai wanka tai ado sosai a jikin ta da fuskar ta.
Bata san dalili ba yau dai ta tashi da farin ciki da son yin kwalliya.
Ta zauna ta karya. Kitchen ta shiga ta fara hada hadar abincin rana.
Fried rice tayi wacce ta wadata da hanta, tayi farfesun naman kaji, tayi cislow.
Cake ta kwaba tai baking sannan ta yi meat pie.
A daining ta jere su tayiwa wajen ado mai kyau.
Kitchen ta koma ta hada lemon kwakwa da madara ta saka dabinoi ta sa a firij.
Wanka ta kara tai Kwalliya sosai kamar amarya. ta saka wani papper less mai kyau da tsada wanda duk jikin sa stones ne da suka kara masa kyau sai daukar ido yake..
Red and black kala. Sosai tai kwalliya ta feshe jikin ta da turare mai kamshi sosai.
Dan kunne da sarka ta saka jajjaye, Babban falo ta koma ta zauna tana kallo.
Wajen karfe uku ta jiyo sallamar sa, amsawa tayi ba tare da ta dago ta kalle shi ba.
Shi kuwa tin da ya shigo ya zuba mata ido, dan yaga tai masa kyau.
Karasawa inda take ya zauna a gefen ta. Dagowa tayi ta zura masa manya manyan idon ta masu dimauta shi, kallon sa ta tsaya yi, sosai yayi kyau.
Yana sanye cikin Sky blue din shadda yai kyau da shi.
Fatar sa ta dada yin fresh, ya dada haske kyaun sa ya kara fitowa jikin sa ya murje. Ya dawo cikaken balaraben sa
Iska ya hura mata, wannan yasa tai saurin dawo wa cikin hayyacin ta.
Kai ya daga mata alamar 'Menene?'
Kai ta dauke daga kallon sa. Hannun ta ya kamo wanda tai masa ado da jan lalle.
Saitin bakin sa yayi da hannun ya sumbata. Zai yi magana kenan yaji ana knocking.
"Waye?"
Ya tambaya.
Mai gadi ne ya ce,
"Nine! Bakuwa kayi."
"Cene ta shigo."
Ya fada yana kallon Asma'u.
Mikewa yayi ya ce, bari na shiga na watsa ruwa.
Yana shiga tana shigowa ba kowa bace face Pretty.
Asma'u da bata san ta ba ta amsa mata sallamar da tayi tana mikewa.
Wajen zama ta nuna mata sannan itama ta zauna.
Gaisawa sukai, Pretty ta ce,
"Baki sanni ba. Ko Aslam yana nan?"
Kai Asma'u ta daga ta ce,
"Eh amman yanzu ya shiga wanka."
Ta mike ta kawo mata lemo da snack. Lemon kadai ta dan sha ta zauna jiran sa.
Sai kallon Asma'u take a ranta ta ce,
"Ashe haka Asma'un take ahh lallai doke Aslam yaso ta. Duk da yarinya ce amman tana da sura mai kyau. Allah sarki na cutar dake.'
Duk wannan maganar a zuciya take yin ta.
Sai da tai minti ashirin Asma'u taga Aslam bai shigo ba ta mike ta shiga ciki.
Yana gaban mudubi Daure da towel a kugun sa, yana ta kalkale jikin sa, Asma'u ta shiga.
Ganin sa a haka yasa tai saurin juya baya.
Kallon ta yayi yai murmushi, magana ta fara yi cikin rawar murya,
"Kayi bakuwa ana jiran ka."
Ta fada, tafiya ta fara yai saurin kamo hannun ta ya juyo da ita.
Kin juyowa tayi, shi ya juyo da ita da hannun sa.
Ido tai saurin runtsewa. Murmushi yayyi ya jata kan gado.
Zaunar da ita yayi ya saka kayansa. Sai da ya gama ya ce,
"To matsoraciyya na gama bude idon."
A hankali ta fara bude idon ganin ya saka kayan yasa ta bude su.
Mikewa tayi ta ce,
"Yaya tana jiran ka fa."
"Na sani."
Hanya tayi zata fita ya ce,
"Zo ki gyara ni man."
Ya fada yana mika mata turare.
Amsa tayi ta fefesa masa. Ta ajiye. tafiya ta fara ya ce,
"Oh!"
Juyowa tayi, ya ce,
"Comb my hair man!"
Amsar comb din tayi ta taje masa kai. Tana direwa tayi waje.
Bayan ta yabi, suka fita. Hannun ta ya kama, suka jera har zuwa falo.
Da yake Pretty ta juya ma hanyar da suke fitowa baya bai gane ita bace
Zagayawa yayi ya zauna ba tare da ya kalli bakuwar ta shi ba.
Asma'u kuma tayi hanyar sashen sa. Saboda taga yai bakuwa.
Dagowa yayi ya ce,
"Sann....."
Bai karasa fadin abinda zai fada ba yai saurin mikewa.
"Me kika zo min a gida?"
Ya fada cikin tsawa. Wanda ya janyo hankalin Asma'u.
Juyowa tayi ta tsaya kallon sa. Lokaci daya ya canja.
Fuskar sa tai jajir, da Hannu ya nuna mata kofa alamar tazo ta fice.
Zubewa tayi a kasa tana rokar sa ya tsaya ya saurare ta amman ya kafe akan sai ta fita.
Asma'u ce ta koma dakin ta kama hannun sa ta ce,
"Haba Yaa Aslam ka tsaya man."
Hannun sa ya kwace ya ce,
"Bazan tsaya naji ba. ta fice min da gani."
Kallon sa Asma'u tayi taga ransa a bace yake sosai.
Hannun Pretty ta kama zaunar da ita.
Wajen Aslam ta karasa shima ta zaunar da shi.
Kansa ta shafa masa har ya samu ya sauke ajiyar zuciya.
Kallon sa tayi, ta ce,
"Kiyi hakuri duk da bansan me ya faru a tsakanin ku ba amman ka saurare ta"
Ta fada tana mikewa. Hannun ta ya kamo, ya zaunar.
Kallon sa tayi ya gyada mata kai alamar ta zauna.
Zaman tayi, ya ce,
"Na baki minti biyu ki fadi abinda ya kawo ki, ki bar min gida na."
"Hakuri na zo na baka!"
Ta fada cikim sanyin murya.
"Indai hakuri ne ki tashi ki tafi bana bukata kara ganin kki a rayuwa ta. Rayuwar da nai dake a baya ma ban san nayi ba."
"Nasan da haka Aslam amman ka yafe min, nazo na bawa Asma'u hakuri ne."
Kallon ta Asma'u tayi cikin rashin sani ta ce
"Ni kuma? Ni da ban sanki ba."