Sashe 28
Asma'u Husnah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A haka ta kwana da tunanin wata haryar da zata mallaki Aslam.
Ganin bata da wata hanya yasa ta amince da zata koma gun sa.
Mikewa tayi ta shiga wanka ta shirya cikin shigar banzar da ta saba yi.
Abin hawa ta hau ya kai ta inda zata je. Ya dire ta tayi cikin jejin.
Yana zaune kamar ko da yaushe, yana ganin ta ya saki fara'a.
Karasawa tayi tana jin damuwar zuwan nata. Kallon ta yayi ya ce,
"Ya kin amince ne?"
Kai ta gyda masa dariya yayi ya ce,
"To ai kin kyauta. Ki shiga daga cikin zan kira shi in zo zaki ganshi."
Mikewa tayi tai ciki. Kallo ya bita dashi yana lashe leben sa.
Can ya mike yayi cikin dakin da ta shiga yana wata irin tafiya.
Sun dauki a kalla fin awa hudu zuwa biyar sannan Bokan ya fito yana gumi. Wajen zaman sa ya zauna.
Can kuma sai ga pretty nan ta fito. Fuskar ta tai jajir da ita.
Kallon malamin tayi ta bar wajen. Gida ta je ta dade tana dirje jikin ta sannan ta fito ta kwanta a kan gado.
Ido ta lumshe tana cewa, Amman Malamin nan yayi. Dama ace Aslam ne.
Ta yi juyi akan gado ta ce,
"Asma'u kike ko Husnah ina tausaya miki duk randa na samu Aslam kin mutu."
Cikin ta taji yana kukan yunwa ta mike ta fita gari dan samun abunda zata ci.
Asma'u ce zaune a garden tana sanye da threequatern wando da riga karama a jikin ta. Sai hijab din ta da yake har kasa. ta rafka uban ta gumi. Ba wanda ta tino in ba Dady ba.
Hawaye taji yana bin fuskar ta da sauri ta goge hawayen tina maganar Aslam da ya ce,
" *Husnah* dan Allah kimin alkawarin ba zaki kara kukan akan Dady ba sai addu'a. wallahi kukan ki yana taba zuciya ta kamar yadda nasan ki cikin wani hali inda nima nake tsintar kai na a ciki. Ki daina kuka dan Allah ko bayan ido na kar kiyi kuka. In kuwa kikai kuka bazan taba yafewa kai na akan amanar ki da Dady ya bani ba."
Murmushi ta dan saki na tunawa da Yaa Aslam. Tana da tabbacin Ya Aslam din ta zai rike ta amana dan tasan yana daga cikin masoyan ta na farko a duniya.
Duk abinda yasan zai sa ta farin ciki shi yake buri shi yake mata. Ko baya son abu in tana so zai san yadda zai yi ya so abin.
Sabir da yana tsaye yana kallon irin murmushin da take sai yaji wani dadi.
Hawaye kuma ya dawo zubo mata tina in kuma ta rasa Aslam fa.
Kuka sosai take yi har Sabir ya tsaya gaban ta bata ganshi ba.
Handkerchief ya mika mata. Amsa tayi tana goge hawayen fuskar ta ba tare da ta ga wanda ya bata ba.
Zama yayi daga gefe ya ce,
"Haba *Husnah* mene na kuka kuma. Ki dauki hakuri kowa hakuri yake ki na wa Dady addu'a."
Kai ta daga tare da kallon sa. Shima kallon ta yake yana sanye cikin dark blue din wando da bakar riga. Sosai yayi kyau.
Murmushi ya sakar mata. Itama murmushin ta sakar masa.
Hira ya fara janta yana bata abin dariya. Sun jima suna tare sannan suka shiga wajen Mami.
Mami dake zaune rike da casbaha, tana ganin Asma'u ta gane tayi kuka.
Murmushi tayi ta mika mata hannu tayi gun ta. Ta ce,
" *Asma'un Dady* kukan ki kayi ko?"
Kai ta girgiza tana murmushi. Murmushin itama Mami tayi ta ce,
"Hakuri dai zamu nayi. Muma Allah bamu wucewa lafiya."
"Ameen!"
Suka amsa.
Hira Sabir da Mami suke ita kuma tana can a whatsapp suna chat da Yaa Aslam.
Hakuri yake kara bata tare da kwantar mata da hankali.
Suna yi tana satar kallon Sabir kamar yadda shima yake satar kallon ta.
Ita dai Sir Sabir yana burgeta, akwai shi da saukin kai ga fara'a.
Haka nan nature sa na burgeta. Ido ta lumshe sai kuma fuskar Aslam ta bayyana yana mata murmurshi
Itama murmushin tayi ya zame ta kwanta akan kujera.
*INDABAWA*
[1/18, 14:22] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR*
*Asma'u Husnah*
Na *Maryam S Indabawa*
*Mans*
🌐 *HAJOW* 🌐
*Hakuri da Juriya Online writers*
*Gidan Amanci da albarka*
Dedicated to *My Lovelly Momy*
*146-150*
Kwanan Pretty biyu sannan ta koma gun malamin ta.
Tana zuwa ya hau mata albishir da aikin ta yayi kamar me. Murna ta farayi.
Malamin ya ce,
"Sai dai akwai wani hanzari ba gudu ba. Shine ki kula sosai sannan kafin aure kiyi kokari ki dawo dan akwai wani abu da za a karayi miki."
Godiya tayi masa, ya ce,
"Kar ki damu da kin je gida zaki tadda abin mamaki."
Kudi masu yawa ta zube masa ta tashi tana masa godiya shi kuwa a ransa tinda ya kusan ce ta yaji a duniya ba wacce yake so kamar ta.
Yayi Alkawari da duk daren dadewa sai ya mallake ta ta zama tasa gaba daya.
Ya bata dama ne ta je wajen Aslam din amman yayi alkwarin shi da kansa zai raba su dan ya same ta.
Ita kuwa Pretty gida tayi tana ta murna.
**********************************************
Aslam ne zaune a dakin sa yana waya da Asma'u.
Duk wayar da suke kara kwantar mata da hankali yake, sosai take samun nutsuwa in tana tare da Aslam.
Sai dai kwanan nan tana yawa mafarkai akan Aslam, wanda in ta zauna ita kadai tai ta kuka ta rasa kukan mene, amman tasan tana tsoron rasa Aslam ne.
Kwanan nan ta dan rame ta kara rage walwala duk da yadda take so ta sake ko dan tana sawa Mamin ta nishadi amman kasawa take.
Bama in da dare bayan sun ci abincin dare. Ba wanda yake fado mata sai dady shi yasa da sauri take tafiya daki ta sha kuka.
In ba Aslam ne ya kira ta ya kwantar mata da hankali ba.
Dan Aslam ko ta chatting yana gane a irin mood din da take bare kuma yaji muryar ta.
Aslam dake kwance idon sa lumshe yana yiwa Asma'u tadi mai dadi da sanya ta nishadi har yaji tayi bacci.
Wayar ya bari a kunnen sa yana jin yadda numfashin ta ke sauka a hankali a hankali.
Yana kwancen nan bai tashi yayi alwala yayi shirin bacci ba bare addu'a bacci ya dauke shi.
Ya jima yana baccin can kuma sai ya mike.
Dakin ya fara kalla. Ba abinda yaji yana so ya ji ko ya gani in ba Pretty ba.
Abokin sa Mohd da Pretty tasan shi ta dalilin sa ya kira a waya.
Abokin sa dake kwance yana bacci dan lokacin wajen karfe uku ne yaga kiran sa.
Dauka yayi dan shi ya zata ma ba lafiya ba.
Aslam ne ya katse masa tunanin dalilin kiran sa ta hanyar ce masa,
"Mohd dan Allah number Pretty nake so yanzun nan."
Mohd cire wayar yayi daga kunnen sa ya kara kallon me kiran nasa.
To kawai ya fada ya kashe wayar. Mamaaki yake me Aslam zai yi da number Pretty bayan ko sunan ta bai son ji bare wani abu da ya shafe ta.
Baki ya tabe ya ce,
"Shi yasani."
Number ya tura masa ya koma bacci. Aslam kuwa yana ganin number yai ta kira amman a kashe.
Ranar har asuba bai kuma ba yana ta kiran wayar. Kiran sallah shi ya sa ya hakura ya mike yai wanka yai alwala ya tafi massalaci.
Yana fita Asma'u ta kira saboda jin bai kira ta ba.
Amman shiru bai dauka ba. Tayi tsammanin yaje masallaci shi yasa ta bar kiran nasa.
Aslam kuwa yana dawowa daga massalaci ko ta kan wayar sa bai bi ba. Ya shiga bayi ya kara wanka ya fito ya shirya cikin Wando baki sai riga ruwan kasa.
Yayi kyau dashi. Turare ya dauka ya feshe jikin sa dashi.
Falo ya fita ya tadda Momy na hada musu wajen karyawa.
Gaisawa suka sannan ya mike ya fita kamar wanda ake hankada shi.
Sauri kawai yake yaje yaga Pretty, gudu yake sosai har ya karasa gidan su,
Horn yayi aka bude masa gate din fitowa yayi bayan yai parking ya akai a kira masa Pretty
Wanda ya aika cikin gidan yazo ya ce, masa Pretty bata nan.
Cikin mota ya koma ya zauna. Wani iri yake jin sa. Ranar ji yake in har bai ga Pretty ba bazai iya rayuwa ba.
Duk ransa yana son yasan halin da Asma'u take ciki da ya fara tunanin Asma'u sai kuma Pretty ta fado masa.
Duk da Asma'un ba gushewa take a zuciyar sa ba amman ya rasa dalili.
Haka ya yini a harabar gidan su Pretty sallah ce kadai ke tayar da shi.
Da ya dawo zai tambaya ko Pretty ta dawo. Cikin lokaci kan kani ya canja ya koma wani iri.
Ranar sai karfe goma ya koma gida bayan ya tabbatar da Pretty bata nan.
Jiki a salube ya dawo gida. Momy kuwa da hankalin ta ya gama tashi na ganin tin safe basuyi waya da shi ba kuma in ta kira ba ya dauka ya daga mata hankali.
Yana dawowa ta hau tambayar ko lafiya. Ce mata yai bai da lafiya, wannan yasa ta kai shi daki ta hada masa ruwan wanka sanna ta kai masa abinci.
Wankan yayi ya ci abinci. A ransa yana tunanin yau ko a wane hali Asma'u take.
Har ya mike zai dauko waya ya kira ta kuma sai ya fasa ya koma ya kwanta.
Tunanin sa daya Pretty. Haka ya kwana ya tashi. Dan ko baccin kirki bai samu yayi ba.
Washe gari ma tin safe ya kuma dirar wa gidan su Pretty.
Pretty kuwa tana hanya dawowa ggida ana sallah la'asar aka kawo ta kofar gidan su.
Motar Aslam ta gani a cikin gidan su. Matsawa tayi wajen motar ta kalla ta kuma kalla.
Tabbas motar Aslam ce kenan da gaske dai abinda Malam ya fada mata.
Wani tsalle ta doka ta yi cikin gidan bangaren ta, ta shiga tai wanka ta fito tayi falon gidan.
Mahaifiyar ta ce zaune cikin shigar kasaita. Tana kallo.
Ganin bata da wata hanya yasa ta amince da zata koma gun sa.
Mikewa tayi ta shiga wanka ta shirya cikin shigar banzar da ta saba yi.
Abin hawa ta hau ya kai ta inda zata je. Ya dire ta tayi cikin jejin.
Yana zaune kamar ko da yaushe, yana ganin ta ya saki fara'a.
Karasawa tayi tana jin damuwar zuwan nata. Kallon ta yayi ya ce,
"Ya kin amince ne?"
Kai ta gyda masa dariya yayi ya ce,
"To ai kin kyauta. Ki shiga daga cikin zan kira shi in zo zaki ganshi."
Mikewa tayi tai ciki. Kallo ya bita dashi yana lashe leben sa.
Can ya mike yayi cikin dakin da ta shiga yana wata irin tafiya.
Sun dauki a kalla fin awa hudu zuwa biyar sannan Bokan ya fito yana gumi. Wajen zaman sa ya zauna.
Can kuma sai ga pretty nan ta fito. Fuskar ta tai jajir da ita.
Kallon malamin tayi ta bar wajen. Gida ta je ta dade tana dirje jikin ta sannan ta fito ta kwanta a kan gado.
Ido ta lumshe tana cewa, Amman Malamin nan yayi. Dama ace Aslam ne.
Ta yi juyi akan gado ta ce,
"Asma'u kike ko Husnah ina tausaya miki duk randa na samu Aslam kin mutu."
Cikin ta taji yana kukan yunwa ta mike ta fita gari dan samun abunda zata ci.
Asma'u ce zaune a garden tana sanye da threequatern wando da riga karama a jikin ta. Sai hijab din ta da yake har kasa. ta rafka uban ta gumi. Ba wanda ta tino in ba Dady ba.
Hawaye taji yana bin fuskar ta da sauri ta goge hawayen tina maganar Aslam da ya ce,
" *Husnah* dan Allah kimin alkawarin ba zaki kara kukan akan Dady ba sai addu'a. wallahi kukan ki yana taba zuciya ta kamar yadda nasan ki cikin wani hali inda nima nake tsintar kai na a ciki. Ki daina kuka dan Allah ko bayan ido na kar kiyi kuka. In kuwa kikai kuka bazan taba yafewa kai na akan amanar ki da Dady ya bani ba."
Murmushi ta dan saki na tunawa da Yaa Aslam. Tana da tabbacin Ya Aslam din ta zai rike ta amana dan tasan yana daga cikin masoyan ta na farko a duniya.
Duk abinda yasan zai sa ta farin ciki shi yake buri shi yake mata. Ko baya son abu in tana so zai san yadda zai yi ya so abin.
Sabir da yana tsaye yana kallon irin murmushin da take sai yaji wani dadi.
Hawaye kuma ya dawo zubo mata tina in kuma ta rasa Aslam fa.
Kuka sosai take yi har Sabir ya tsaya gaban ta bata ganshi ba.
Handkerchief ya mika mata. Amsa tayi tana goge hawayen fuskar ta ba tare da ta ga wanda ya bata ba.
Zama yayi daga gefe ya ce,
"Haba *Husnah* mene na kuka kuma. Ki dauki hakuri kowa hakuri yake ki na wa Dady addu'a."
Kai ta daga tare da kallon sa. Shima kallon ta yake yana sanye cikin dark blue din wando da bakar riga. Sosai yayi kyau.
Murmushi ya sakar mata. Itama murmushin ta sakar masa.
Hira ya fara janta yana bata abin dariya. Sun jima suna tare sannan suka shiga wajen Mami.
Mami dake zaune rike da casbaha, tana ganin Asma'u ta gane tayi kuka.
Murmushi tayi ta mika mata hannu tayi gun ta. Ta ce,
" *Asma'un Dady* kukan ki kayi ko?"
Kai ta girgiza tana murmushi. Murmushin itama Mami tayi ta ce,
"Hakuri dai zamu nayi. Muma Allah bamu wucewa lafiya."
"Ameen!"
Suka amsa.
Hira Sabir da Mami suke ita kuma tana can a whatsapp suna chat da Yaa Aslam.
Hakuri yake kara bata tare da kwantar mata da hankali.
Suna yi tana satar kallon Sabir kamar yadda shima yake satar kallon ta.
Ita dai Sir Sabir yana burgeta, akwai shi da saukin kai ga fara'a.
Haka nan nature sa na burgeta. Ido ta lumshe sai kuma fuskar Aslam ta bayyana yana mata murmurshi
Itama murmushin tayi ya zame ta kwanta akan kujera.
*INDABAWA*
[1/18, 14:22] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR*
*Asma'u Husnah*
Na *Maryam S Indabawa*
*Mans*
🌐 *HAJOW* 🌐
*Hakuri da Juriya Online writers*
*Gidan Amanci da albarka*
Dedicated to *My Lovelly Momy*
*146-150*
Kwanan Pretty biyu sannan ta koma gun malamin ta.
Tana zuwa ya hau mata albishir da aikin ta yayi kamar me. Murna ta farayi.
Malamin ya ce,
"Sai dai akwai wani hanzari ba gudu ba. Shine ki kula sosai sannan kafin aure kiyi kokari ki dawo dan akwai wani abu da za a karayi miki."
Godiya tayi masa, ya ce,
"Kar ki damu da kin je gida zaki tadda abin mamaki."
Kudi masu yawa ta zube masa ta tashi tana masa godiya shi kuwa a ransa tinda ya kusan ce ta yaji a duniya ba wacce yake so kamar ta.
Yayi Alkawari da duk daren dadewa sai ya mallake ta ta zama tasa gaba daya.
Ya bata dama ne ta je wajen Aslam din amman yayi alkwarin shi da kansa zai raba su dan ya same ta.
Ita kuwa Pretty gida tayi tana ta murna.
**********************************************
Aslam ne zaune a dakin sa yana waya da Asma'u.
Duk wayar da suke kara kwantar mata da hankali yake, sosai take samun nutsuwa in tana tare da Aslam.
Sai dai kwanan nan tana yawa mafarkai akan Aslam, wanda in ta zauna ita kadai tai ta kuka ta rasa kukan mene, amman tasan tana tsoron rasa Aslam ne.
Kwanan nan ta dan rame ta kara rage walwala duk da yadda take so ta sake ko dan tana sawa Mamin ta nishadi amman kasawa take.
Bama in da dare bayan sun ci abincin dare. Ba wanda yake fado mata sai dady shi yasa da sauri take tafiya daki ta sha kuka.
In ba Aslam ne ya kira ta ya kwantar mata da hankali ba.
Dan Aslam ko ta chatting yana gane a irin mood din da take bare kuma yaji muryar ta.
Aslam dake kwance idon sa lumshe yana yiwa Asma'u tadi mai dadi da sanya ta nishadi har yaji tayi bacci.
Wayar ya bari a kunnen sa yana jin yadda numfashin ta ke sauka a hankali a hankali.
Yana kwancen nan bai tashi yayi alwala yayi shirin bacci ba bare addu'a bacci ya dauke shi.
Ya jima yana baccin can kuma sai ya mike.
Dakin ya fara kalla. Ba abinda yaji yana so ya ji ko ya gani in ba Pretty ba.
Abokin sa Mohd da Pretty tasan shi ta dalilin sa ya kira a waya.
Abokin sa dake kwance yana bacci dan lokacin wajen karfe uku ne yaga kiran sa.
Dauka yayi dan shi ya zata ma ba lafiya ba.
Aslam ne ya katse masa tunanin dalilin kiran sa ta hanyar ce masa,
"Mohd dan Allah number Pretty nake so yanzun nan."
Mohd cire wayar yayi daga kunnen sa ya kara kallon me kiran nasa.
To kawai ya fada ya kashe wayar. Mamaaki yake me Aslam zai yi da number Pretty bayan ko sunan ta bai son ji bare wani abu da ya shafe ta.
Baki ya tabe ya ce,
"Shi yasani."
Number ya tura masa ya koma bacci. Aslam kuwa yana ganin number yai ta kira amman a kashe.
Ranar har asuba bai kuma ba yana ta kiran wayar. Kiran sallah shi ya sa ya hakura ya mike yai wanka yai alwala ya tafi massalaci.
Yana fita Asma'u ta kira saboda jin bai kira ta ba.
Amman shiru bai dauka ba. Tayi tsammanin yaje masallaci shi yasa ta bar kiran nasa.
Aslam kuwa yana dawowa daga massalaci ko ta kan wayar sa bai bi ba. Ya shiga bayi ya kara wanka ya fito ya shirya cikin Wando baki sai riga ruwan kasa.
Yayi kyau dashi. Turare ya dauka ya feshe jikin sa dashi.
Falo ya fita ya tadda Momy na hada musu wajen karyawa.
Gaisawa suka sannan ya mike ya fita kamar wanda ake hankada shi.
Sauri kawai yake yaje yaga Pretty, gudu yake sosai har ya karasa gidan su,
Horn yayi aka bude masa gate din fitowa yayi bayan yai parking ya akai a kira masa Pretty
Wanda ya aika cikin gidan yazo ya ce, masa Pretty bata nan.
Cikin mota ya koma ya zauna. Wani iri yake jin sa. Ranar ji yake in har bai ga Pretty ba bazai iya rayuwa ba.
Duk ransa yana son yasan halin da Asma'u take ciki da ya fara tunanin Asma'u sai kuma Pretty ta fado masa.
Duk da Asma'un ba gushewa take a zuciyar sa ba amman ya rasa dalili.
Haka ya yini a harabar gidan su Pretty sallah ce kadai ke tayar da shi.
Da ya dawo zai tambaya ko Pretty ta dawo. Cikin lokaci kan kani ya canja ya koma wani iri.
Ranar sai karfe goma ya koma gida bayan ya tabbatar da Pretty bata nan.
Jiki a salube ya dawo gida. Momy kuwa da hankalin ta ya gama tashi na ganin tin safe basuyi waya da shi ba kuma in ta kira ba ya dauka ya daga mata hankali.
Yana dawowa ta hau tambayar ko lafiya. Ce mata yai bai da lafiya, wannan yasa ta kai shi daki ta hada masa ruwan wanka sanna ta kai masa abinci.
Wankan yayi ya ci abinci. A ransa yana tunanin yau ko a wane hali Asma'u take.
Har ya mike zai dauko waya ya kira ta kuma sai ya fasa ya koma ya kwanta.
Tunanin sa daya Pretty. Haka ya kwana ya tashi. Dan ko baccin kirki bai samu yayi ba.
Washe gari ma tin safe ya kuma dirar wa gidan su Pretty.
Pretty kuwa tana hanya dawowa ggida ana sallah la'asar aka kawo ta kofar gidan su.
Motar Aslam ta gani a cikin gidan su. Matsawa tayi wajen motar ta kalla ta kuma kalla.
Tabbas motar Aslam ce kenan da gaske dai abinda Malam ya fada mata.
Wani tsalle ta doka ta yi cikin gidan bangaren ta, ta shiga tai wanka ta fito tayi falon gidan.
Mahaifiyar ta ce zaune cikin shigar kasaita. Tana kallo.