← Book details Asma'u Husnah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 29 OF 61

Sashe 29

Asma'u Husnah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Pretty ce ta shigo ta fada jikin ta. Kallon ta Mahaifiyar tata tayi ta ce,
"Pretty ni ai nayi fushi kwana biyu ko neme na bakya yi."

Kai ta dan sosa ta ce,
"Sorry Mommah!"

"Shikenan waye ne tun jiya yake zaryar neman ki a gidan nan."

Kallon mahaifiyar tayi ta ce,
"Wani ne, shine wanda nake son aura."

Murmushi uwar tayi ta ce,
"Kai Alhamdulilah amman naji dadi amman na bar shi a waje tin jjiya yake zarya fa."

"Kar ki damu Mommah nima nasha wahala akan sa."
Mommahn ta ce,
"Ah ai kam kema gasa abin ki."

Pretty ta mike ta ce,
"Kisa a kawon abinci bangare na."

Ta fice. Dakin ta ta nufa ta zauna. Wayar ta ta dauko ta kunna.

Text din Aslam ne suka dinga shiga wayar.

Sai da ta gama karantawa taga yadda ya hauka ce sannan ta sheke da dariya.

Kiransa tayi. Lokacin yana jikin motar sa dan bai dade da dawowa daga massalaci ba.

Yana ganin kiran ta yai saurin dauka. Ya ce,
"Haba Baby na ina kika shiga ne haka?"

Murmushi tayi ta ce,
"Kana ina ne?"

Gidan ya kalla sannan ya ce,
"Ina cikin gidan ku fa."

"Oh ai ban sani ba yanzu na dawo. Ka sa a nuna maka site dina sai ka shigo."

Nan da nan ya tambaya aka nuna masa ya nufi wajen da sauri dan bai da abinda yake burin gani kamar Pretty.

Tana zaune a kan kujera gaban ta kayan abinci ne kala kala.

Yana shigowa ta mike ya mata masifar kyau. Yana sanye da Brown wando sai milk din riga.

Wajen sa ta nufa ta kamo hannun sa. Murmushi ya sakar mata ya karaso cikin dakin.

Zama sukai a kujera mai daya ta zauna akan cinyar sa.

Fuskar sa take shafawa a hankali kafin ta daura kan ta a kkirjin sa.

Aslam kuwa wata ajiyaar zuciya ya dinga saukewa dan ko ba komai ya samu abinda ransa ya matsa masa ya zo ya nema.

Duk da zuciyar sa tana can ga Asma'u amman wani bangaren tunanin sa yana ga Pretty ya rasa dalili.

Kallon sa ta danyi ta ce,
"Wai da gaske kai ne?"

Kallon ta yayi ya ce
"Ga alama nan kuwa."

Kai ta gyada ta ce,
"Ya batun soyayyar mu."
Wani murmushi ya saki ya ce,
"Sai yadda kika ce."

"Da gaske?"
Ta tambaye shi tana wasa da sumar kan sa.

Kai ya gyada mata. Murmushi tayi ta ce,
"Aure nake so muyi nan da sati biyu."

"Sati biyu kawai "
Ya tambaye ta.

Kai ta gyada masa, ya ce,
"An gama. Nawa ne zai ishe ki siyan kayan lefe da komai da komai."

Kai ta dan daga ta ce,
"Ka bari zuwa gobe zan duba."

"Shikenan! Ki fada min goben fa. Dan nima na matsu."
murmushi tayi ta rumgume shi.

Shima rumgume tan yayi. Kiss ta fara masa, jiki da jini tini shima ya hau biye mata.

Kiran sallah da yaji ana yi shi yasa yai saurin tsayawa daga abinda yake yi.

Mikewa yayi. Kallon sa tayi ta ce,
"Lafiya?"

Nuni yai mata da waje sannan ya ce,
"Kiran Sallah ake."

Tsaki tayi ta ce,
"Ni na zata ma wani abun ne."

Ta koma ta zauna Kallon ta yayi yai murmushi ya ce,
"Bari naje na dawo."

Ya fice ranar dai har goma suna tare da Pretty da kyar ta kyale shi ya tafi.

*INDABAWA*
[1/18, 14:22] Maryam S Indabawa🥰:  *LABARIN RAYUWAR*

*Asma'u Husnah*

Na *Maryam S Indabawa*
*Mans*

Facebook @Maryam sulaiman
Wattpad @Msindabawa
Instagram @Maryam S Indabawa

🌐 *HAJOW* 🌐
*Hakuri da Juriya Online writers*
*Gidan Amanci da albarka*

Dedicated to *My Lovelly Momy*

*151-155*

An Kar6o Daga *Aisha (ra)* Tace: Na Tambayi *Manzon Allah(ﷺ)* Game da Waige a Cikin Sallah? Sai Yace: *"Wata Fisga ce Shedan Yakeyi a Cikin Sallar Bawa"*. (Bukhari)._

_A Hadisin *Tirmizi* Kuma Ya Ingantashi: *"Kashedinka da Yin Waiwaye a Cikin Sallah, Domin Halaka ne, Idan Ya Kasance Babu Makawa Sai Kayi, To Kayi A Cikin Sallar Nafila"*._

Yana shiga gida ya tadda Momy zaune a falo.

Kallon sa tayi ya karasa gun ta.

Gaishe ta yai ya dan zauna. Kallonsa tayi ta ce,
"Aslam lafiyar ka kuwa. Kwana biyun nan ina kake zuwa da har kake kai dare haka a waje."

Kai yayi kasa da shi. Dan ka idar sa da anyi isha'i yana gida.

"Ba magana nake maka ba. Ka fadan inda kake zuwa."
Shiru ya karayi.

"Wallahi Aslam zan batar maka in baka fadan ina kake zuwa ba."
kai ya dan sosa ya ce,
"Daman ina son nai miki maganar ne, wajen wata budurwa ta wacce nake son aura nake zuwa."

Tsaki Momy tayi ta ce,
"Wai ni sa'ar ka ce da kake min wasa bayan kasan ba lokacin wasa bane yanzu."

Shiru yayi yana tunanin ta inda zai fara.
"Wai ba magana nake maka bane, ko so kake na kira mahaifin ka na fada masa."

Kai ya girgiza ya ce,
"Momy da gaske nake."

Momy ta ce,
"Da gaske kake kamar ya?"

Kai ya sosa ya ce,
"Momy daman mun gama maganar aure da 'yar gidan tsohon ministern man fetur ne akan nan da sati biyu zamuyi aure."

Kallon sa Momy take tama kasa cewa komai.

Dagowa yayi ya kalle ta, ta ce,
"Eh ka dago ka kalle ni ai nifa bangane mai kake fadi ba."

"Eh Mami yar sa Pretty ita nake so nake son muyi aure nan da sati biyu dan har nace ta fadawa Mahaifin ta ma."

Kallon mamaki Momy kewa Aslam dan gani take kamar ba Aslam din ta ba.

Aslam din ta mai hankali da nutsuwa amman ji wannan inda yake mata wani shirmen zance.

Amman kuma fa zancen kamar akwai kamshin gaskiya.

Da kyar Momy ta iya bude baki ta ce,
"Asma'un fa?"

Kai ya girgiza ya ce,
"Momy ni yanzu ga wacce Nake son na aura."

Kallon sa Momy tayi ta ce,
"Aslam kana cikin hayyacin ka kuwa."

Kai ya gyada mata. Momy ta ce,
"Me ya hada ku da Asma'un taka."

Kai ya girgiza ya ce,
"Wallahi Momy ba komai."

"Amman saboda me zakai mata haka."
Kallon Momy yayi ya kasa bata amsa.

Shima bai san abinda yake fadi ba. Ji yake kamar bashi yake maganar ba.

"Aslam kasan me kake fadi kuwa. Asma'un taka kake son ka ce min ka fasa aura ko kuwa."

Kai ya gyada mata. Momy ta ce,
"Inna illahi wainna illahir rajiun."

Sai da ta fada sau uku sannan ta dago ta kalli Aslam sosai dan taga ko ya fara shaye shaye ne.

Har mikewa tayi tana shinshina sa da duba sa.

Ganin ba alamar shaye shaye yasa ta kuma mike tayi wajen sa tana duba shi.

Tabbas Aslam din ne dai 'dan ta. Komawa tayi ta zauna tana rike kan ta.

Sanna ta dago ta ce,
"Wallahi Aslam ba da yawu na ba a auren da kake son kayi. Ba ruwana kaje ka nemi wata uwar bani ba."

Ta mike ta bar masa falon. Mikewa yayi jiki a sanyaye yayi dakinsa.

Daki ne guda kai kace dakin wata amaryar ne. Babu abinda babu a ciki.

Kan kujera ya fada, yana dafe kan sa. Ya zai yi.

Wayar sa da tin dazu take kara ya dauko ya duba.

*Soul mate* shine abinda ya bayyana akan wayar.

Ajiyewa Yayi ba tare da ya dauka ba. Dayar wayar sa ce ta hau ringing itama yana dauka naga *My* ya bayyana akai.

Shima ajiyewa yayi bai dauka ba. Haka ta gama kiransa amman bai dauka ba.

Shi kansa wani zafi yake ji, baya son damuwar Asma'u amman mai yake damun sa yake neman sa ta a damuwa.

Dan ya tabbata Asma'u tana cikin damuwa fiye da tunanin mai tunani.

Har ya dau wayar zai kira sai kuma ya fasa ya kira Pretty waya sukai sosai. Dan har sha biyu suna waya sanna sukai sallama yai wanka yazo ya fada gado.

Shi kansa yasan bai da lafiya. Dan rashin Asma'u ba karamin tashin hankaline a rayuwar sa ba.

Pretty kuwa tana can har an fara shirye shiryen aure.

Dan komai da take bukata tai masa list din su.

Haka nan kudaden da za a kashe wajen taro duk ta masa suma list

Sosai ta tsuga kudi dan komai na karya take so yayi mata.

Waya kowa tayiwa kawayen ta kan cewa nan da sati biyu bikin ta. Dan har kalar ankon da za a sak"a ta fitar dashi.

*********************************************************************
Asma'u ce kwance, akan gadon kai daga ganin ta kasan ba lafiya ba.

To rabon ta da abinci kwana biyu kenan.

Hankalin ta ya kasa kwanciyya da rashin kiran da Yaa Aslam bai mata ba gashi ta kira shima bai daga ba. Ta kira Momy ma ita ma bata daga ba.

Tana kwance idon ta jajir dan rabon ta da bacci shima yau kwana biyu ne.

Ga wata faduwar gaba da take yawan yin ta. Ta rasa ta me ce.

Ido ta lumshe hawayen da ya taru suka zubo akan fuskar ta.

Juyi tayi tana me fashewa da kuka. Ba wanda ya fado mata sai Dady.

A duniya ta san indai Yaa Aslam ya na nan ba zatai kukan mutuwar Dady ba.

To yanzu in Yaa Aslam din ya mutu tayi yaya kenan. Ko in ya barta tayi ya kenan.

Tana tunanin taji an bude kofa. Da sauri ta goge hawayen idon ta.

Yaa Buhari ne, ya shigo hannun sa dauke da Leda.

Kan gadon ya karasa ya dan zauna kafin ya dago ta.

Jikin ta ya taba yaji har lokacin da zazzabin.

Kallon ta yayi ciki tausayawa ya ce,
"Sannu Asma'u. Ya jikin?"

Murmushi yake tai masa ta ce,
"Yaya nifa yanzu normal nake ji na."

"Da gaske?"
Ya tambaya yana mata murmushi shima.

Kai ta gyada masa. Murmushi yayi ya mika mata ledar hannun sa ya ce,
"Ungo wannan to ki daure kici kinji Kanwata."

Amsa tayi idon ta na kawo kwalla. Ta ce,
"Tnc bro."

"Ina zuwa. Akwai wani suprise da zan miki "
Ya mike ya fita.

Bayan sa ta bi da kallo yana fita ta fashe da kuka.

Mami ce ta shigo dakin da yake Buhari bai rufe kofar ba bataji shigowar ta ba.
Chapter 29 · 0% Book details