← Book details Asma'u Husnah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 19 OF 61

Sashe 19

Asma'u Husnah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Yauwah!"
Ya fada kamar bai san wanda yai maganar ba dan kansa yana can kallon gefe.

Zatai magana kenan ya daga mata hannu. Sannan ya mike ya tsaya a gaban ta.

"Me kike nema ne?"
Ya tambaye ta yana juya mata baya,

Kallon sa ta tsaya yi tana hadiyar yawu.
"Wallahi sai na dan dani zumar gayen nn."

Ta fada a ranta. Tana kallon sa hadi da hadiyar yawu sai kace ta ga nama.

"Uhmm uhmm daman!"
Sai kuma tayi shiru.

Murmushi yayi mai sauti sannan ya juyo gare ta.
"Haba yan mata. Ki rike ajin ki na 'ya mace man. Nasan irin ku nasan kalar ku muna dasu daa yawa wadan da ke bibiyar mu. Ba wai son mu kuke haka kawai ba akwai wani abu a ranku. In da 'yar mutumci ce taga mutum tana son sa, ta san ta yadda zata tusa kanta gare shi har yasan da ita. Ba kamar ke da kikazo kika samen gaba da gaba ba. Kuma dan Allah kalli shigar ki. Wannan ba shigar ya'yan kirki bace, ko da zan so mace. Ba zan so macen da bata da kamun kai ba wacce ta gama tallata surar ta ga mazan waje ba."

Shiru yayi sannan ya ce,
"Kalle ki dan Allah kin kalli kan ki a mudubi kuwa kafin ki fito."

Kanta take kalla sai a lokacin taga shirga dake jikin ta ba mai kyau ba.

Kanta ya sha gashin doki har gadon baya, sannan ta saka riga da wando sun dame ta.

Sai wani dan karamin mayafi da ta yafa ta saka takalmi mai tsini.

Bilkis ce ta kara so gun ta ce,
"Kai Munasha kina wuta fa."

Shiru Maimuna tai mata, kallon su yayi ya ce,
"Yanzu wannan dawa kikai koyi, kinsan wadan da kikai koyi dasu ko, to turawa ne, Bayan Allah madaukakin sarki ya ce,
"Kada ku rike da al'adun yahudu da nasara kuma ya ce kada ku koyi abubuwan su wajen shiga sauya suna. Duk wanda ya jibanta al amaransa zuwa ga yahudu da nasara Allah (SWT) ya ce, ka zamto daga cikin su. Wato ya zamo su.' (Ma'ida 51)
"Kinga ko anan kinyi abu nawa irin nasu. Ji shigar ki. ji wani suna da aka kira ki dashi.
Manzon Allah (SAW) Yace,
'Duk wanda ya kwaikwayi wasu to shima ya zama shi.'
Haka nan Manzon Allah (SAW) ya ce,
'Mutun na tashi ranar alkiyama da wanda yake so.'
In kana son Allah da mazon sa kana yin abinda suka ce dasu zaka tashi. Haka nan in kana son wasun su, to da su zaka tashi.
Haka nan aya ta 57 a cikin suratul ma'ida. Allah madaukakin sarki yaba cewa,
"Yaku wadan da kukai imani karku riki wadan da suka rike adddinin mu da wasa da rudu' (yahudu da nasara) su ne suka rike addinin mu da wasa. Kar mu rike kafiri a cikin masoya (mudai dai yi mu'amala) muji tsoron Allah in mun kasance mumunai.
kiji tsoron Allah ki koma ga Allah dan daga shigar ki ya nuna min ke wace, kada ki manta daman sai da shaidan ya ce,
'Wallahi sai ya samu rabon sa.'
Wallahi ba kowa ke saka mana wadan nan ra'ayuyu kan ba in ba shi ba duk dan ya dulmiyar damu. Kiji tsoron Allah ki daina duk abinda kike. Duniya ba matabbaciyya bace, haka rayuwar mu a koda yaushe mai iya karewa ce."

Ya juya kenan yaga Asma'u da Zainab suna tsaya suna sauraran su. Kuka Maimuna ta fashe da shi ta zube a kasa. Da sauri Asma'u ta karasa gun ta ta dago ta.

Kallon Asma'u tayi idon tana fitar da kwalla. Kuka take sosai sai da kyar Asma'u ta lallashe ta tayi shiru.

"Asma'u daman mutum kan hadu da mutum in Allah yaso. haduwa ta ga Aslam shine shiriya ta da izinin Allah. Nagode Yaa Aslam nagode insha Allahu bazan kara aikata abubuwan sabo ba."

Sosai Yaa Aslam yaji dadi.
"Ba komai. Kiji tsoron Allah dai a duk inda kike."

Ya kalli Asma'u ya sakar mata murmushi. Zainab ya kalla ya ce,
"A'ah In-low ashe kina nan."

Murmushi tayi ta dan durkusa ta gaishe shi.

Gaba sukai shi da ita suna hira. Har take basa labarin yadda Maimuna ta dinga damun Asma'u akan sa.

Dariya yayi ya ce,
"Allah sarki. Ita kuma me tayi."

Zainab ta ce,
"Ai kasan Asma'u in yan mutuncin suna nan akwai saukin kai."

Sukai dariya gaba daya. Ya ce,
"Lallai kam. Amman dadi na da Asma'u akwai hakuri sai dai in aka kai ta karshe basan ya zata yi ba kuma,"

"Wallahi kuwa ba ruwan kowa nata ne, kowa tana iya zama da shi. Allah Asma'u bata da temper kowa sai taka ta yadda zata saka farin ciki da karatun ya. Bata da abokin fada bata da riko."

Murmushi yayi jin halayar Asma'u wanda shima ya san da su

Asma'u tana can lallashin Maimuna har sai da ta ga ta daina kukan ta nutsu sannan sukai sallama.

Bilkis kuwa duk da abinda Aslam ya fada ya ratsa ta amman bata jin zata daina abubuwan da take yi

Gun Maimuna tayi ta ce,
"Maunas......"

Bata karasa fada ba ta dakatar da ita ta ce,
"Bana son sunan nan ki kira ni da Maimuna in zaki iya"

Ta mike tayi gun motar ta tashiga ta fita daga makarantar a guje.

Baki Bilkis ta tabe ta shiga motar da Maimuna ta tabi bayan ta.

Asma'u kam suna tsaye ita da Aslam da Zainab.

Zainab na tsokanar ta da tini an kwace mata Yaa Aslam dinta.

Duka ta kai mata ta ce,
"Ai ba mai iya kwace shi sai Allah yaso."

Yaa Aslam ya ,
"Allah ma bazai so na ni na kine ke kadai."

Gira ta daga ta kalli Zainab ta ce,
"Kinji ko?"

Murmushi tayi tace,
"Allah tabbatar da alheri."

"Ameen!"
Duk suka amsa sannan sukai sallama ta shiga motar gidan su itama suka shiga ita da Yaa Aslam suka tafi.

A mota ma labarin yadda sukai da Maimuna ne yadda ya je gun ta a makaranta da lokacin da ta tambaye ta aikin sa da suna sa.

Dariya take shi kuwa ya hade rai. Kallon sa tayi ta ce,
"Me kuma nayi?"

Motar ya faka a gefen hanya ya kalle ta ya ce,
"Wai ke bakya kishi nane, daga nan baza ki gane me take nufi ba. Amman kin wani sake da ita."

Murmushi tayi ta ce,
"To Yaa Aslam ai sai mutum bai san matsayin sa a gun masoyin sa ba zai tsaya kishi. Ni da nasan ko da duk matan duniyar nan zaka aura sona daban ne a zuciyar ka haka nan kaunar da kake min baza ta taba tafiya ba kuma bame iya samun rabin ta daga wajen ka. Kada fa ka manta mukullin zuciyar ka nice. Tayya zan bude har wata ta shiga."

Dariya yayi ya lakace hancin ta fe,
"Ni dai ana kishi na dan baki san wasu mantan bane."

Murmushi tayi ta ce,
"Ina kishin ka man nafi kowa kishin ka da kishin masoyin sa saboda ni kadai nasan wane irin masoyi ne dani. Ina son ka. Ina kaunar ka bazan so wata ta rabe ka ba ni kadai nasan kishin da nake maka a cikin zuciya ta."

*INDABAWA*
[1/18, 14:17] Maryam S Indabawa🥰: *Asma'u Husnah*

Na *Maryam S Indabawa*
*Mans*

🌐 *HAJOW* 🌐
*Hakuri da Juriya Online writers*
*Gidan Amanci da albarka*

Dedicated to *My Lovelly Momy*

*101-105*

*KARATUN AL KUR'ANI A GIDA. Domin Karatun Alqur'ani Yanada Matukar Tasiri Wajen Bada Kariya Ga Shedanu a Gida. Sannan Yana Taimakawa Wurin Halartar Mala'iku Cikin Gidan Da Saukar Rahamar da Bata da Iyaka da Kuma Samar da Natsuwa da Yalwar Zuciya da Hutu ga Ma'abota Wannan Gida; Haka Shima Ambaton Allah (Zikiri) Duk Yana Haifar da Wannan Abubuwan.*

Haka rayuwar Asma'u ta cigaba da tafiya cikin kwanciyyar hankali da samun soyayya daga wajen iyayen ta da masoyin ta kuma yayan ta.

Cikin satin biyun da yazo yi ba karamin shakuwa ssuka kara ba. Kullum shi zai kai ta makaranta ya kuma dauko ta.

Makarata sam ta daina yi dan haka kullum tana gaba da Sir Sabir ya shiga da ita yake yin tozali.

Yanzu Maimuna ta shiryu dan gidan ta ma da motar da take hawa duk ta siyar ta fara business sosai take karatu tana kuma taimakawa iyayen ta.

Dan duk karshen wata zataje gida. Haka duk zigar kawayen ta yan harka taki ta dauka.

Dan har sam ta canja ta koma ga Allah kullum hijabai take sawa har kasa.

Kasuwancin ta kuwa Allah yasa mata albarka dan a hostel duk abinda kake nema kaje gunta zaka samu banda kaya da take rabawa bashi da anyi albashi aba ta kudin ta.

Sosai suke mutunci da Asma'u da Zainab. Suna kara koya mata abinda bata iya ba tinda ita lab science take karanta.

Yau satin Yaa Aslam uku kenan a kano ya kasa komawa dan bai son ya tafi ya bar Asma'un sa.

Suna zaune a garden kamar yadda suka saba in sun dawo gida da wuri.

Aiki ya gama koya mata sannan ya kalle ta yai murmushi.

"Lafiya?"
ta tambaye shi.

Murmushi ya kara. Fuska ta shagwabe ta ce,
"Yaa Aslam Mene wai?"

Dariya yayi. Sai ta bata fuska kuma.
"Ayyah sorry yan mata na. Kinsan me?"

Da sauri ta girgiza kai. Ya ce,
"Wallahi kina yar karama na tuna lokacin da kullum kina saman cinya ta a zaune, ko bacci sai a guna zakiyi. Yanzu kuma kalle ki yadda kika girma kika zama mace."

Sai yayi dariya. Fuska ta bata ta ce,
"Allah Yaa Aslam din nan ko? Wai shekara nawa ma ka bani."

Ido yayo waje dasu ya ce,
"Tab! Allah yarinyar nan ko dan kinga ina kula ki ko?"

"Kaji ka Yaya. Wai ina zaune a cinyar ka ko nai bacci a gun ka. Yanzu fa ka daina la'akari da da ma wallahi dan nasan ka gamai min wayoo ne kawai kaga yarinta ta."
ta fada tana turo ba

Dariya yayi ya ce,
"Wallahi *Husnah* ke a autar ma ko ta karshe ce, rashin wayon ki rigimar ki ko?"
Chapter 19 · 0% Book details