Sashe 22
Asma'u Husnah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sanye take da wata jar doguwar riga tayi rolling da bakin mayafi.
Hannun ta rike da waya fuskar ta ba makeup amman tayi kyau tana murmushi dimple din ta ya lotsa.
Ba karamin kyau tayi ba, da sauri yai saving hoton sannan ya kura mata ido.
Kasa dauke idon sa yayi daga kallon hoton. Ido ya lumshe, Sannan ya bude ya saki wani murmushi.
Mikewa yayi ya shige cikin gidan. Wanka yayi ya shirya cikin Blue din shadda, ba karamin kyau yayi ba.
Mikewa yayi ya fita. Mamah ya gani a falo. Karasa wa yayi ya ce,
"Mamah zan fita."
Kallon sa tayi taga ya canja cikin lokaci kadan.
Kallon sa tayi ta ce,
"To a dawo lafiya."
"Ameen!"
ya asma ya fita.
Kallo Mamah tabi shi da shi har ya fice.
Shoprite ya nufa kai tsaye daga gida. Ciki ya shiga, ya fara shopping hankalin sa kwance.
Kamar daga sama ya hango ta tana dibar kaya ita ma,
Ido ya goge ya ga da gaske dai ita din ce.
Tsayawa yayi da dibar kayan ya dinga binta da kallo. Sanye take da Ash kalar doguwar riga, sai bakin mayafi da ta yafa da jaka da takalmi duk bakake. Binta ya dinga yi da kallo har ta gama tayi wajen biya.
Da sauri shima yayi gun. Yana zuwa ta karasa itama.
ATM card din sa ya mika aka zara, juyowar da zai yi suka hada ido.
Da sauri tai kasa da kai, ta dan durkusa ta ce,
"Sir Ina yini?"
Kallon ta ya dan karayi ya amsa da
"Lafiya lou, ya hutu."
"Alhamdulilah!"
Ta bada amsa kan ta a kasa.
"Masha Allah. Bayar a lisaafa miki."
Mikawa tayi ya tsaya yana jiran a gama ya biya.
Anan gamawa ya mika masa card din sa ya ce, ya dauka a ciki.
Kallon sa Asma'u tayi ta ce,
"Lah Sir da kudi aguna."
Kallon ta yayi ya ce,
"Ai na sani. Na dai biya miki ne kawai."
Dan durkusa wa tayi ta ce,
"Nagode!"
Daukar mata ledar yayi ya dauki tashi suka fita.
A Napep take dan haka ta ce, fita zatayi zata hau mota.
"Muje na rage miki hanya."
Ya fada yana yin wajen motar sa.
Ba dan taso ba tabi bayan sa. Shi ya bude mata mazaunin ta sannan ya koma ya shiga bangaren sa.
Motar ya tayar suka fita sannan ya dan kalle ta ya ce,
"Ina zamuyi?"
"Jan bulo. 3rd gate wajen forestry."
kai ya gyada suka dau hanya.
A hankali suke tafiya kamar baya son tukin duk dan kar su rabu.
Kallon ta ya danyi yaga hankalin ta na kan Wayar ta da take dannawa.
Kai ya dauke ya cigaba da tuki. Kiran ta akai ta daga tana satar kallon sa tayi sannan ta dauka.
A hankali tayi sallama, daga dayan bangaren ya Amsa.
"Baby nah kina ina ne?"
Dan taga missed din sa ganin suna tare da Sir Sabir ne ya sa bata kira sa bba.
"Naje shoprite ne, ya kake ya aiki?"
Ta tambaye shi.
"Lafiya Alhamdulilah! Me da me kika siyo?"
"Uhmm in naje gida zan nuna maka su."
"Ok sai kin dawo. Ki kular min da kan ki."
"To nima ka......."
Sai kuma tayi shiru. Ganin Sabir na kallonta.
Kasa tayi da kanta ta ce,
"Sai na koma"
Ta katse wayar. Sabir kuwa jin tana waya da namiji ba karamin tada masa da hankali yayi ba.
Har suka je unguwar ta nuna masa layin sannan suka karasa kofar gidan.
Horn yayi mai gadi ya bude masa gate suka shiga.
Mami suka gani zaune a barander dake kofar falo.
Fitowa tayi tai masa godiya. Kallon wajen da Mami tayi ta ce,
"Kazo ku gaisa da Mami."
"Ok!"
Ya fada yana fitowa.
A hankali cikin nutsuwa suka karasa wajen da Mami take.
Suna zuwa ya durkusa ya gaishe da Mami.
Bayan sun gaisa ne, Asma'u ta ce,
"Mami wannan shine Sir Sabir lecturer mu ne, mun hadu a shoptite kinga shi ya biya min kudin siyayya ta ma ya rage min hanya kuma."
Kai Mami ta gyada ta ce,
"Kai Sabir har da wahala haka. Angode to Allah saka da alheri "
Asma'u ta kalla ta ce,
"Ki kawo masa lemo man."
"A'ah Mami wallahi Alhamdulilah."
yai maganar kan sa a kasa dan kunyar Mami yake ji sosai.
"A'ah Sabir kar muyi hka da kai."
Ta kalli Asma'u ta ce,
"Je ki dauko masa."
Mikewa Asma'u tayi tayi cikin gida. Bata jima ba ta dawo rike da 5alive na kwali sai kofi a hannun ta da plate da ta zubo cake a ciki.
Ajiyewa tayi akan table din dake wajen. Mikewa mami tayi ta ce,
"Ka saki jiki kaci kaji."
Tayi cikin gidan. Zama Asma'u tayi akan kujera ta nuna masa dayar ta ce,
"Bismillah!"
Mikewa yayi ya zauna ta zuba masa lemo.
Lemon kadai ya sha sanna ya mike ya ce, zai tafi.
Har cikin falo ta raka sa yayi wa Mami sallama sannan suka fito har bakin mota ta raka shi.
Sabir kuwa sosai yaji dadin irin tarbar da Mami tai masa.
Sosai ya dinga murna dan ya ga gidan su Asma'u.
Da haka ya tafi gida ransa kamar takarda dan farin ciki.
Yana komawa ya zauna a falon suka dinga hira da Mamah.
Mamah dai sai mamakin canjin sa take dan ya jima bai zauna sun yi hira kamar haka ba.
Suna zaune Abbi ya dawo. Nan suka zauna suna ta hira har akai sallah magariba suka je sukai sallah suka dawo.
A falo suka zauna suka ci abinci sannan suka ci gaba da hira har lokacin baccin su yayi suka mike suka yi dakin nan su.
Yana shiga daki ya tura mata da sakon sai da safe da kalamai masu dadi.
Ban daki ya shiga yayi wanka ya fito ya haye gadon sa.
Online ya hau ya dinga kallon ta a online amman ya kasai mata magana.
Haka ya shiga gallery ya maida hoton ta kamar TV.
Da shi yayi bacci.
*INDABAWA*
[1/18, 14:19] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR*
*Asma'u Husnah*
Na *Maryam S Indabawa*
*Mans*
🌐 *HAJOW* 🌐
*Hakuri da Juriya Online writers*
*Gidan Amanci da albarka*
Dedicated to *My Lovelly Momy*
*116-120*
AN Ruwaito a Cikin Littafin Ibn-Sunni, da Sanadi Me Rauni, Daga *Abi-Sa'eedil Khudry (ra)* Yace: *Manzon Allah(ﷺ)* Ya Kasance Idan Rana Ta Fito Yana Cewa:_
*{ﺍﻟَﺤْﻤَﺪُ ﻟِﻠَّﻪ ﺍﻟَّﺬِﻱ ﺟَﻠَّﻠَﻨَﺎ ﺍﻟْﻴَﻮْﻡَ ﻋَﺎﻓِﻴَﺘَﻪُ ، ﻭَﺟَﺎﺀَﻧَﺎ ﺑِﺎﻟﺸَّﻤْﺲِ ﻣِﻦْ ﻣَﻄْﻠَﻌِﻬَﺎ ، ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﺇِﻧِّﻲ ﺃَﺻْﺒَﺤْﺖُ ﺃَﺷْﻬَﺪُ ﻟَﻚَ ﺑِﻤَﺎ ﺷَﻬِﺪْﺗَﻪُ ﻋَﻠَﻰ ﻧَﻔْﺴِﻚَ ، ﻭَﺷَﻬِﺪَﺕْ ﺑِﻪِ ﻣَﻼﺋِﻜَﺘُﻚَ ﻭَﺣَﻤَﻠَﺔُ ﻋَﺮْﺷِﻚَ ﻭَﺟَﻤِﻴﻊُ ﺧَﻠْﻘِﻚَ ﺃَﻧَّﻪُ ﺃَﻧْﺖَ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﺍﻟَّﺬِﻱ ﻻ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻ ﺃَﻧْﺖَ ﻗَﺎﺋِﻤًﺎ ﺑِﺎﻟْﻘِﺴْﻂِ ، ﻻ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻ ﺃَﻧْﺖَ ﺍﻟْﻌَﺰِﻳﺰُ ﺍﻟْﺤَﻜِﻴﻢُ ، ﺷَﻬَﺎﺩَﺗِﻲ ﻣَﻊَ ﺷَﻬَﺎﺩَﺓِ ﻣَﻼﺋِﻜَﺘِﻚَ ﻭَﺃُﻭﻟِﻲ ﺍﻟْﻌِﻠْﻢِ ﻭَﻣَﻦْ ﻟَﻢْ ﻳَﺸْﻬَﺪْ ﺑِﻤِﺜْﻞِ ﻣَﺎ ﺷَﻬِﺪْﺕُ ، ﻓَﺎﻛْﺘُﺐْ ﺷَﻬَﺎﺩَﺗِﻲ ﻣَﻜَﺎﻥَ ﺷَﻬَﺎﺩَﺗِﻪِ ، ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﺃَﻧْﺖَ ﺍﻟﺴَّﻼﻡُ ﻭَﻣِﻨْﻚَ ﺍﻟﺴَّﻼﻡُ ﻭَﺇِﻟَﻴْﻚَ ﻳَﺮْﺟِﻊُ ﺍﻟﺴَّﻼﻡُ ، ﺃَﺳْﺄَﻟُﻚَ ﻳَﺎ ﺫَﺍ ﺍﻟْﺠَﻼﻝِ ﻭَﺍﻹِﻛْﺮَﺍﻡِ ﺃَﻥْ ﺗَﺴْﺘَﺠِﻴﺐَ ﻟَﻨَﺎ ﺩَﻋْﻮَﺗَﻨَﺎ ، ﻭَﺃَﻥْ ﺗُﻌْﻄِﻴﻨَﺎ ﺭَﻏْﺒَﺘَﻨَﺎ ، ﻭَﺃَﻥْ ﺗَﺰِﻳﺪَﻧَﺎ ﻓَﻮْﻕَ ﺭَﻏْﺒَﺘِﻨَﺎ ، ﻭَﺃَﻥْ ﺗُﻐْﻨِﻴﻨَﺎ ﻋَﻤَّﻦْ ﺃَﻏْﻨَﻴْﺘَﻪُ ﻋَﻨَّﺎ ﻣِﻦْ ﺧَﻠْﻘِﻚَ ، ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﺃَﺻْﻠِﺢْ ﻟِﻲ ﺩُﻧْﻴَﺎﻱَ ﺍﻟَّﺘِﻲ ﻓِﻴﻬَﺎ ﻣَﻌِﻴﺸَﺘِﻲ ، ﻭَﺃَﺻْﻠِﺢْ ﻟِﻲ ﺩِﻳﻨِﻲ ﺍﻟَّﺬِﻱ ﻫُﻮَ ﻋِﺼْﻤَﺔُ ﺃَﻣْﺮِﻱ ، ﻭَﺃَﺻْﻠِﺢْ ﻟِﻲ ﺁﺧِﺮَﺗِﻲ ﺍﻟَّﺘِﻲ ﻓِﻴﻬَﺎ ﻣُﻨْﻘَﻠَﺒِﻲ}*
_*"Alhamdulillahil Lazi Jallalanal Yauma Ãfiyatahu, Wa Jã'a Bish Shamsi, Min Ma'dli'aha, Allãhumma Asbahtu Ash'hadu Laka Bimã Shahidta Bihi Li Nafsika, Wa Shahidat Bihi Malã'ikatuka Wa Hamalatu Arshika Wa Jami'a Khalqika, Innaka Antallahu Lã'ilaha Illã Antal Qa'imu Bil Qisdi, Lã'ilãha Illã Antal Azizul Hakeem, Aktub Shahãdaty Ba'ada Shahãdati Malã'ikatika Wa Ulul Ilmi. Allãhumma Antass Salãm wa Minkas Salãm Wa Ilaikas Salãm, As'aluka Yã Zal-Jalãli Wal Ikrãm An Tastajiba Lanã Da'awatana, Wa An Tu'u'diyanã Ragbatanã, Wa An Tu'u'diyana Amman Agnaitahu Annã Min Khalqika. Allãhumma Aslihli Deeni Allazi Huwa Ismati Amri, Wa Aslihli Dunyayal Laty Feeha Ma'ashy, Wa Aslihly Ãkhiraty Allaty Ilaihã Munqalaby".¹*_
Asma'u kuwa tana komawa ciki ta hau daukar kayan da ta siyo tana nunawa Yaa Aslam.
Hiran suka sha sannan ta mike tayi alwala.
Aslam ganin karatun su Asma'u yazo gangara ya sa yayi takakiya yazo har kano.
Asma'u bata san da zuwan sa ba. Sai da ta dawo daga gidan su Zainab sannan ta ganshi.
Murna kamar me taji dadin ganin sa.
Daki ta shiga danyin wanka. Amman tindata fito vata sake ganin sa ba.
Sai da su Dady ta ganshi da ta sauko da akai sallah isha'i.
Sai kus kus taga suna yi da Dady wannan yasa ma batayi wajen su ba.
Tare duk suka ci abinci, suna gamawa tayi dakin ganin akwai maganar da suke da Dady.
Tana shiga dakintai wanka ta haye gado. faduwar gaba taji tana yi, da haka har bacci ya dauke ta.
Can cikin bacci taji karar wayar ta. Mikewa tayi tana salatin annabi. sannan ta dauko wayar.
Number Yaa Aslam ce. Dauka tayi cikin sanyin murya ta masu bacci.
"Baby na har kinyi bacci?"
Ya tambaye ta.
Kai ta gyda masa ta ce,
"Eh kai fa?"
Ya ce,
"Yanzu dai zan kwanta na ce bari naji ya Baby na take."
Murmushi tayi ta ce,
"Ina lafiya "
"To sai da safe ko?"
Kai ta gyada nasa ta ce,
"Allah tashe mu lafiya. "
Ta kashe wayar ta kwanta.
Washe gari kuwa tana gama abinda zatai ta kule a daki.
Mami ce ta shigo ta ce, Dady na neman ta.
Wata faduwar gaba ta ji. Haka ta mike ta dauki mayafin rigar dake jikin ta ta nufi falon Dady
A hanya ta hadu da Yaa Aslam shima zai je dakin.
Kallon sa tayi ta dauke kai sannan ta durkusa ta gaishe shi.
Amsawa yayi yana binta da wani kallo mai cike da tsantar kauna.
Kai ta kawar tai saurin shigewa dakin Dady
Bayan ta yabi yana murmushi wanda shi kadai yasan ma'anar sa.
Asma'u na shiga tayi gefen Dady, gaishe shi tayi sannan ta kalli Yaa Buhari dake dakin shima ta gaishe shi.
Mami ce ta shigo ta zauna. Gyaran murya Dady yayi sannan ya ce,
"Ayi salati ga Annabi (SAW)."
Bayan anyi akai addu'a ga wanda da suka riga mu gidan gaskiya sannan.
Ya kalli Asma'u ya ce,
" *Husnah* ba komai ne ya tara mu anan gun ba sai wani abun da nake son na sanar dake, abin nan kowa ya sani ke kadai ce kawai baki sani ba."
Shiru yayi yana kallon Asma'u wacce duk ta gama tsorata bata san me zai faru ba.
Hannun ta rike da waya fuskar ta ba makeup amman tayi kyau tana murmushi dimple din ta ya lotsa.
Ba karamin kyau tayi ba, da sauri yai saving hoton sannan ya kura mata ido.
Kasa dauke idon sa yayi daga kallon hoton. Ido ya lumshe, Sannan ya bude ya saki wani murmushi.
Mikewa yayi ya shige cikin gidan. Wanka yayi ya shirya cikin Blue din shadda, ba karamin kyau yayi ba.
Mikewa yayi ya fita. Mamah ya gani a falo. Karasa wa yayi ya ce,
"Mamah zan fita."
Kallon sa tayi taga ya canja cikin lokaci kadan.
Kallon sa tayi ta ce,
"To a dawo lafiya."
"Ameen!"
ya asma ya fita.
Kallo Mamah tabi shi da shi har ya fice.
Shoprite ya nufa kai tsaye daga gida. Ciki ya shiga, ya fara shopping hankalin sa kwance.
Kamar daga sama ya hango ta tana dibar kaya ita ma,
Ido ya goge ya ga da gaske dai ita din ce.
Tsayawa yayi da dibar kayan ya dinga binta da kallo. Sanye take da Ash kalar doguwar riga, sai bakin mayafi da ta yafa da jaka da takalmi duk bakake. Binta ya dinga yi da kallo har ta gama tayi wajen biya.
Da sauri shima yayi gun. Yana zuwa ta karasa itama.
ATM card din sa ya mika aka zara, juyowar da zai yi suka hada ido.
Da sauri tai kasa da kai, ta dan durkusa ta ce,
"Sir Ina yini?"
Kallon ta ya dan karayi ya amsa da
"Lafiya lou, ya hutu."
"Alhamdulilah!"
Ta bada amsa kan ta a kasa.
"Masha Allah. Bayar a lisaafa miki."
Mikawa tayi ya tsaya yana jiran a gama ya biya.
Anan gamawa ya mika masa card din sa ya ce, ya dauka a ciki.
Kallon sa Asma'u tayi ta ce,
"Lah Sir da kudi aguna."
Kallon ta yayi ya ce,
"Ai na sani. Na dai biya miki ne kawai."
Dan durkusa wa tayi ta ce,
"Nagode!"
Daukar mata ledar yayi ya dauki tashi suka fita.
A Napep take dan haka ta ce, fita zatayi zata hau mota.
"Muje na rage miki hanya."
Ya fada yana yin wajen motar sa.
Ba dan taso ba tabi bayan sa. Shi ya bude mata mazaunin ta sannan ya koma ya shiga bangaren sa.
Motar ya tayar suka fita sannan ya dan kalle ta ya ce,
"Ina zamuyi?"
"Jan bulo. 3rd gate wajen forestry."
kai ya gyada suka dau hanya.
A hankali suke tafiya kamar baya son tukin duk dan kar su rabu.
Kallon ta ya danyi yaga hankalin ta na kan Wayar ta da take dannawa.
Kai ya dauke ya cigaba da tuki. Kiran ta akai ta daga tana satar kallon sa tayi sannan ta dauka.
A hankali tayi sallama, daga dayan bangaren ya Amsa.
"Baby nah kina ina ne?"
Dan taga missed din sa ganin suna tare da Sir Sabir ne ya sa bata kira sa bba.
"Naje shoprite ne, ya kake ya aiki?"
Ta tambaye shi.
"Lafiya Alhamdulilah! Me da me kika siyo?"
"Uhmm in naje gida zan nuna maka su."
"Ok sai kin dawo. Ki kular min da kan ki."
"To nima ka......."
Sai kuma tayi shiru. Ganin Sabir na kallonta.
Kasa tayi da kanta ta ce,
"Sai na koma"
Ta katse wayar. Sabir kuwa jin tana waya da namiji ba karamin tada masa da hankali yayi ba.
Har suka je unguwar ta nuna masa layin sannan suka karasa kofar gidan.
Horn yayi mai gadi ya bude masa gate suka shiga.
Mami suka gani zaune a barander dake kofar falo.
Fitowa tayi tai masa godiya. Kallon wajen da Mami tayi ta ce,
"Kazo ku gaisa da Mami."
"Ok!"
Ya fada yana fitowa.
A hankali cikin nutsuwa suka karasa wajen da Mami take.
Suna zuwa ya durkusa ya gaishe da Mami.
Bayan sun gaisa ne, Asma'u ta ce,
"Mami wannan shine Sir Sabir lecturer mu ne, mun hadu a shoptite kinga shi ya biya min kudin siyayya ta ma ya rage min hanya kuma."
Kai Mami ta gyada ta ce,
"Kai Sabir har da wahala haka. Angode to Allah saka da alheri "
Asma'u ta kalla ta ce,
"Ki kawo masa lemo man."
"A'ah Mami wallahi Alhamdulilah."
yai maganar kan sa a kasa dan kunyar Mami yake ji sosai.
"A'ah Sabir kar muyi hka da kai."
Ta kalli Asma'u ta ce,
"Je ki dauko masa."
Mikewa Asma'u tayi tayi cikin gida. Bata jima ba ta dawo rike da 5alive na kwali sai kofi a hannun ta da plate da ta zubo cake a ciki.
Ajiyewa tayi akan table din dake wajen. Mikewa mami tayi ta ce,
"Ka saki jiki kaci kaji."
Tayi cikin gidan. Zama Asma'u tayi akan kujera ta nuna masa dayar ta ce,
"Bismillah!"
Mikewa yayi ya zauna ta zuba masa lemo.
Lemon kadai ya sha sanna ya mike ya ce, zai tafi.
Har cikin falo ta raka sa yayi wa Mami sallama sannan suka fito har bakin mota ta raka shi.
Sabir kuwa sosai yaji dadin irin tarbar da Mami tai masa.
Sosai ya dinga murna dan ya ga gidan su Asma'u.
Da haka ya tafi gida ransa kamar takarda dan farin ciki.
Yana komawa ya zauna a falon suka dinga hira da Mamah.
Mamah dai sai mamakin canjin sa take dan ya jima bai zauna sun yi hira kamar haka ba.
Suna zaune Abbi ya dawo. Nan suka zauna suna ta hira har akai sallah magariba suka je sukai sallah suka dawo.
A falo suka zauna suka ci abinci sannan suka ci gaba da hira har lokacin baccin su yayi suka mike suka yi dakin nan su.
Yana shiga daki ya tura mata da sakon sai da safe da kalamai masu dadi.
Ban daki ya shiga yayi wanka ya fito ya haye gadon sa.
Online ya hau ya dinga kallon ta a online amman ya kasai mata magana.
Haka ya shiga gallery ya maida hoton ta kamar TV.
Da shi yayi bacci.
*INDABAWA*
[1/18, 14:19] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR*
*Asma'u Husnah*
Na *Maryam S Indabawa*
*Mans*
🌐 *HAJOW* 🌐
*Hakuri da Juriya Online writers*
*Gidan Amanci da albarka*
Dedicated to *My Lovelly Momy*
*116-120*
AN Ruwaito a Cikin Littafin Ibn-Sunni, da Sanadi Me Rauni, Daga *Abi-Sa'eedil Khudry (ra)* Yace: *Manzon Allah(ﷺ)* Ya Kasance Idan Rana Ta Fito Yana Cewa:_
*{ﺍﻟَﺤْﻤَﺪُ ﻟِﻠَّﻪ ﺍﻟَّﺬِﻱ ﺟَﻠَّﻠَﻨَﺎ ﺍﻟْﻴَﻮْﻡَ ﻋَﺎﻓِﻴَﺘَﻪُ ، ﻭَﺟَﺎﺀَﻧَﺎ ﺑِﺎﻟﺸَّﻤْﺲِ ﻣِﻦْ ﻣَﻄْﻠَﻌِﻬَﺎ ، ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﺇِﻧِّﻲ ﺃَﺻْﺒَﺤْﺖُ ﺃَﺷْﻬَﺪُ ﻟَﻚَ ﺑِﻤَﺎ ﺷَﻬِﺪْﺗَﻪُ ﻋَﻠَﻰ ﻧَﻔْﺴِﻚَ ، ﻭَﺷَﻬِﺪَﺕْ ﺑِﻪِ ﻣَﻼﺋِﻜَﺘُﻚَ ﻭَﺣَﻤَﻠَﺔُ ﻋَﺮْﺷِﻚَ ﻭَﺟَﻤِﻴﻊُ ﺧَﻠْﻘِﻚَ ﺃَﻧَّﻪُ ﺃَﻧْﺖَ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﺍﻟَّﺬِﻱ ﻻ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻ ﺃَﻧْﺖَ ﻗَﺎﺋِﻤًﺎ ﺑِﺎﻟْﻘِﺴْﻂِ ، ﻻ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻ ﺃَﻧْﺖَ ﺍﻟْﻌَﺰِﻳﺰُ ﺍﻟْﺤَﻜِﻴﻢُ ، ﺷَﻬَﺎﺩَﺗِﻲ ﻣَﻊَ ﺷَﻬَﺎﺩَﺓِ ﻣَﻼﺋِﻜَﺘِﻚَ ﻭَﺃُﻭﻟِﻲ ﺍﻟْﻌِﻠْﻢِ ﻭَﻣَﻦْ ﻟَﻢْ ﻳَﺸْﻬَﺪْ ﺑِﻤِﺜْﻞِ ﻣَﺎ ﺷَﻬِﺪْﺕُ ، ﻓَﺎﻛْﺘُﺐْ ﺷَﻬَﺎﺩَﺗِﻲ ﻣَﻜَﺎﻥَ ﺷَﻬَﺎﺩَﺗِﻪِ ، ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﺃَﻧْﺖَ ﺍﻟﺴَّﻼﻡُ ﻭَﻣِﻨْﻚَ ﺍﻟﺴَّﻼﻡُ ﻭَﺇِﻟَﻴْﻚَ ﻳَﺮْﺟِﻊُ ﺍﻟﺴَّﻼﻡُ ، ﺃَﺳْﺄَﻟُﻚَ ﻳَﺎ ﺫَﺍ ﺍﻟْﺠَﻼﻝِ ﻭَﺍﻹِﻛْﺮَﺍﻡِ ﺃَﻥْ ﺗَﺴْﺘَﺠِﻴﺐَ ﻟَﻨَﺎ ﺩَﻋْﻮَﺗَﻨَﺎ ، ﻭَﺃَﻥْ ﺗُﻌْﻄِﻴﻨَﺎ ﺭَﻏْﺒَﺘَﻨَﺎ ، ﻭَﺃَﻥْ ﺗَﺰِﻳﺪَﻧَﺎ ﻓَﻮْﻕَ ﺭَﻏْﺒَﺘِﻨَﺎ ، ﻭَﺃَﻥْ ﺗُﻐْﻨِﻴﻨَﺎ ﻋَﻤَّﻦْ ﺃَﻏْﻨَﻴْﺘَﻪُ ﻋَﻨَّﺎ ﻣِﻦْ ﺧَﻠْﻘِﻚَ ، ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﺃَﺻْﻠِﺢْ ﻟِﻲ ﺩُﻧْﻴَﺎﻱَ ﺍﻟَّﺘِﻲ ﻓِﻴﻬَﺎ ﻣَﻌِﻴﺸَﺘِﻲ ، ﻭَﺃَﺻْﻠِﺢْ ﻟِﻲ ﺩِﻳﻨِﻲ ﺍﻟَّﺬِﻱ ﻫُﻮَ ﻋِﺼْﻤَﺔُ ﺃَﻣْﺮِﻱ ، ﻭَﺃَﺻْﻠِﺢْ ﻟِﻲ ﺁﺧِﺮَﺗِﻲ ﺍﻟَّﺘِﻲ ﻓِﻴﻬَﺎ ﻣُﻨْﻘَﻠَﺒِﻲ}*
_*"Alhamdulillahil Lazi Jallalanal Yauma Ãfiyatahu, Wa Jã'a Bish Shamsi, Min Ma'dli'aha, Allãhumma Asbahtu Ash'hadu Laka Bimã Shahidta Bihi Li Nafsika, Wa Shahidat Bihi Malã'ikatuka Wa Hamalatu Arshika Wa Jami'a Khalqika, Innaka Antallahu Lã'ilaha Illã Antal Qa'imu Bil Qisdi, Lã'ilãha Illã Antal Azizul Hakeem, Aktub Shahãdaty Ba'ada Shahãdati Malã'ikatika Wa Ulul Ilmi. Allãhumma Antass Salãm wa Minkas Salãm Wa Ilaikas Salãm, As'aluka Yã Zal-Jalãli Wal Ikrãm An Tastajiba Lanã Da'awatana, Wa An Tu'u'diyanã Ragbatanã, Wa An Tu'u'diyana Amman Agnaitahu Annã Min Khalqika. Allãhumma Aslihli Deeni Allazi Huwa Ismati Amri, Wa Aslihli Dunyayal Laty Feeha Ma'ashy, Wa Aslihly Ãkhiraty Allaty Ilaihã Munqalaby".¹*_
Asma'u kuwa tana komawa ciki ta hau daukar kayan da ta siyo tana nunawa Yaa Aslam.
Hiran suka sha sannan ta mike tayi alwala.
Aslam ganin karatun su Asma'u yazo gangara ya sa yayi takakiya yazo har kano.
Asma'u bata san da zuwan sa ba. Sai da ta dawo daga gidan su Zainab sannan ta ganshi.
Murna kamar me taji dadin ganin sa.
Daki ta shiga danyin wanka. Amman tindata fito vata sake ganin sa ba.
Sai da su Dady ta ganshi da ta sauko da akai sallah isha'i.
Sai kus kus taga suna yi da Dady wannan yasa ma batayi wajen su ba.
Tare duk suka ci abinci, suna gamawa tayi dakin ganin akwai maganar da suke da Dady.
Tana shiga dakintai wanka ta haye gado. faduwar gaba taji tana yi, da haka har bacci ya dauke ta.
Can cikin bacci taji karar wayar ta. Mikewa tayi tana salatin annabi. sannan ta dauko wayar.
Number Yaa Aslam ce. Dauka tayi cikin sanyin murya ta masu bacci.
"Baby na har kinyi bacci?"
Ya tambaye ta.
Kai ta gyda masa ta ce,
"Eh kai fa?"
Ya ce,
"Yanzu dai zan kwanta na ce bari naji ya Baby na take."
Murmushi tayi ta ce,
"Ina lafiya "
"To sai da safe ko?"
Kai ta gyada nasa ta ce,
"Allah tashe mu lafiya. "
Ta kashe wayar ta kwanta.
Washe gari kuwa tana gama abinda zatai ta kule a daki.
Mami ce ta shigo ta ce, Dady na neman ta.
Wata faduwar gaba ta ji. Haka ta mike ta dauki mayafin rigar dake jikin ta ta nufi falon Dady
A hanya ta hadu da Yaa Aslam shima zai je dakin.
Kallon sa tayi ta dauke kai sannan ta durkusa ta gaishe shi.
Amsawa yayi yana binta da wani kallo mai cike da tsantar kauna.
Kai ta kawar tai saurin shigewa dakin Dady
Bayan ta yabi yana murmushi wanda shi kadai yasan ma'anar sa.
Asma'u na shiga tayi gefen Dady, gaishe shi tayi sannan ta kalli Yaa Buhari dake dakin shima ta gaishe shi.
Mami ce ta shigo ta zauna. Gyaran murya Dady yayi sannan ya ce,
"Ayi salati ga Annabi (SAW)."
Bayan anyi akai addu'a ga wanda da suka riga mu gidan gaskiya sannan.
Ya kalli Asma'u ya ce,
" *Husnah* ba komai ne ya tara mu anan gun ba sai wani abun da nake son na sanar dake, abin nan kowa ya sani ke kadai ce kawai baki sani ba."
Shiru yayi yana kallon Asma'u wacce duk ta gama tsorata bata san me zai faru ba.