← Book details Asma'u Husnah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 32 OF 61

Sashe 32

Asma'u Husnah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Washe gari da zazzabi mai zafi ta kuma ta shi. Dan ko 'kasa kasa sauka tayi.

Tana kwance Momy ta shigo dakin da break din ta a hannu.

Ganin ta a kwance yasa tai zaton ko bacci take wannan yasa ta fita bata tashe ta ba.

Wanka taje tayi ta shirya dan ta tafi gida.

Mami na falo Buhari na gefen ta ya zuba ta gumi.

Ajiyar zuciya ya sauke ya kalli Mami ya ce,
"Mami munje anyiwa Asma'u visa har dake ma zaku tafi tare. Amman na je na fadawa Uncle Abubakar kan a matso da biki na kusa. In lokacin ya yi Mami ke sai ki dawo. Ki bar Asma'u acan dan ta samu nutsuwa."

Kai Mami ta gyada masa dan gwara Asma'u bata nan za ai bikin Aslam da ace tana nan abin bazai mata ba dadi ba.

Buhari ya ce,
"To Mami jibi ne tafiyar."

Mami ta ce,
"Allah nuna mana."

"Ameen!"
ya asma.

Ya ce,
"Asma'u bata sauko ba ko jikin ne."

"Jeka duba ta. Wallahi ni bana son na ganta a irin wannan halin wallahi."
Mikewa yayi yai sama.

Yana zuwa ya tura kofar dakin. Tana kwance bata motsa ba.

Sai da ya shiga ya zauna a gefen ta sannan ya dago ta.

Idon ta ta bude wadan da sukai ja dasu. Dan wani irin ciwon kai ke damun ta wanda ya taba mata har idon ta. Dan idon ta wani zafi da nauyi yai mata.

Ido ta mayar ta lumshe saboda zafin da taji yana mata. Cikin karfin haki ta ce,
"Yaa Buhari ina kwana?"

Bai amsa ba ya jingina ta da gado. Tea ya hada mata mai kauri sai farfesun kayan cikin da aka yi ya dinga bata a baki.

Sosai taci dan rabon ta da abinci tin jiya da rana.

Sai da ta koshi duk idon ta a rufe sannan ya bata magani.

Mami dake ta taga tana ganin abinda suke hawaye ya wanke mata fuska.

Daki ta shiga tayi kuka sosai sannan ta mike ta wanke fuska tayi dakin Asma'u.

Lokacin da ya kwantar da ita kenan. Tana jin muryar Mami ta mike tana mika mata hannu.

Hannun ta Mami ta kama ta kwantar da ita akan cinyar ta tana shafa kanta.

A hankali a hankali har tayi bacci. Kallon ta Mami tayi. Asma'u ta rame ta kara gaske, sannan ta zama shiru shiru dan ko magana bata son yi.

Hawaye ne ya zubowa Mami tai saurin gogewa. Momy ce ta shigo cikin shirin ta.

Zama tayi a gefen Mami ta ce,
"Amina nifa bazan zauna ina ganin Asmaa'u a wannan halin ba sannan na kasa taimakon ta. Ko ba halin da Aslam ya canja bane yasa ta a wannan halin nasan kasance war sa da ita zata rage damuwa. Zanje nasan yadda zanyi sai munyi  waya,"

Ta mike, kallon Mami tayi ta ce,
"Na miki transfer kudi, na kayan abincin wannan watan ne. Ki kula da Asma'u sai kinji ni."

Momy ta fita tana kwadawa Buhari kira dan zai kai ta airport.

Momy na fita Mami ta saki kuka. Su kuma tasu jarabar kenan.

Allah ya dauke musu jigon su, rumfar su. Sai kuma wannan Allah ya daukewa Asma'u Aslam.

"Allah ka bamu ikon cinye wannan jarabawar.'

Mami ta fada tana shafa kan Asma'u.

Pls don't forget to vote
*LABARIN RAYUWAR*
    *Asma'u Husnah*

*part 2*

*INDABAWA*
[1/18, 14:27] Maryam S Indabawa🥰:  *LABARIN RAYUWAR*
    *Asma'u Husnah*

*part 2*

Na *Maryam S Indabawa*
*Mans*

🌐 *HAJOW* 🌐
*Hakuri da Juriya Online writers*
*Gidan Amanci da albarka*

Dedicated to *My Lovelly Momy*

Ina taaya Amrah A Mashi (Princess Amrah) murnar kammala littafin ta na (Amrah make so) Allah ubangiji ya kara basira . Siss daban kike. Ina kaunar ki saboda Allah da zuciya daya

*11-15*

Da yamma Mami na zaune a falo. Asma'u kwance akan cinyar ta.

Zazzabin ne ya kara zafi sai hawaye da take zubarwa. Duk da ta sha magani amman jikin nan kamar wuta.

Suna zaune ssuka jiyo sallamar Sir Sabir. Mami ce ta amsa masa ya shigo.

Sai da suka gaisa cikin girmamawa sannan ya dubi Asma'u ya ce,
"Mami yau kuma *Husnah* autan cin ne ya motsa."

Tinda ya ambaci Husnah, Asma'u ta bude ido tana kallon sa. Shima kallon ta yake.

Mami ce, ta ce,
"Ba lafiya ne, kaga muje asibitin amman jikin kamar dada mata ciwon ake."

"Ya Salam! Me yake damun ta?"
Ya tambaya.

"Uhmm da muka je akai mata BP sai yace jinin ta ya hau. Kaga kullum jikin da zazzabi take kwana take tashi ga ciwon kai."

"Ya salam! Mami kar dai har yanzu Asma'u bata daina sa dumuwar rashin Dady ba."
Mami ta ce,
"To gata nan dai."

"Mami dan Allah ku taso muje asibiti na duba ta."
Mami ta ce,
"To bari na kira Buhari."

Waya ta kira shi nan da nan sai ga shi. Gaisawa sukai da Sabir sannan ya kama Asma'u suka nufi Asibiti.

Office din shi kai tsaya suka nufa. BP ya kara gwada mata. Ba karamin mamaki.ya bashi ba tesult din. Dan ya tsora ta sosai.

Ruwa ya kara juna mata sannan suka fita shi da Buhari ya ke fada masa yadda jinin ta hau.

Buhari bai yi mamamki ba dan yasan aabinda haka ma zai iya faru da Asma'u in ya tuna irin shakuwar da soyayyar dake tsakanin Asma'u da Aslam.

Magani ya kara rubuta mata. Sannan ya karbo suka dawo.

Mami tana zaune ta zubawa Asma'u ido suka dawo. Maganin suka ajiye mata.

Sabir ya kalle ta ya ce,
"Mami ki daina sa damuwa komai zai warware. Allah zai bata lafiya."

Mami ta ce,
"Allah bata sauki."

Tana farkawa Mami ta bata dankali ta ci. Sai magani da dakyar ta amsa ta sha.

Cikin ikon Allah kafin su koma gida jikin ta ya danyi kwari.

Suna komawa. Sabir yai musu sallama ya tafi gida da tunanin Asma'u a ransa.

Washe gari, su Mami da Asma'u suka daga kasa mai tsarki.

Momy na dira gida ta tadda Dady zaune ya zuba tagumi shima al amarin ba karamin damun sa yayi ba.

Dan Aslam sai goma ko sha daya yake dawowa gida.

Yanzu ko zaman hira basa yi. Sai Waya da Pretty duk yinin da suke tare.

Momy ce ta zauna a gefen ta cire masa tagumin da ya zuba. Kallon sa tayi ta ce,
"Dady me ya faru?"

Dagowa yayi ya ce,
"Komai ma. Ya su Asma'un?"

Ajiyar zuciya Mami ta sauke sannan ta masa bayani duka abinda yake faru.

Sannan ta daura da cewa,
"Dady baka ga Asma'u ba. Wallahi bata da lafiya sosai har jinin ta ya hau. Yarinya karama Dady. Kuma na tabbata har da Aslam a sanadin wallahi."

Momy ta fada ranta a bace. Ta ce,
"Kaga yadda Asma'u ta rame kuwa."

Dady ya ce,
"Inna illahi wainna illahir rajiun. Wallahi Aslam ban san me yake damun sa ba. Amman ko jiya da nai masa magana ko aufan bai ce min ba. Ni dai abinda za'ayi kawai a daura auren nan da yana so da baya so."

"Nima haka nace, amman Amina ta ce, aah abi komai a hankali. Ba asan me Allah ya tsara ba."

Kai Dady ya jinjina ya ce,
"Wallahi ba hannu na a cikin auren nan da yake so yayi. Nawa ido ne."

Momy ma ta ce,
"Nima haka amman Aslam bansan me yake damun sa ba. Allah ya shirya shi. Nasan ba kudi ke rudar sa ba ko kyau. Dan Asma'u ba za a. fada mata kyau ko ilimi ba wallahi."

"Nima haka baki ga yadda nake masa sha'awar auren yarinyar nan ba. Ko dan halaiyar ta. ga ilimin ta, na tabbata bazai taba samun yarinya kamar Asma'u ba."

"Ai shikenan tinda haka ya zaba Allah ya kyauta "

"Ameen!"
Dady ya amsa. Ya ce
"Ki kira su kiji ya jikin nata."

"Toh!"
A lokacin ne ta buga taji sun koma asibiti ma.

Sosai Momy ke tausayyawa Asma'u kuma ta dau alkawarin sai ta rama abinda Aslam yai mata.

A kwana a tashi har bikin Aslam ya rage sati daya.

Tin saura sati biyu kawar ta ta rakata asibiti akai mata wani dinki.

Yadda zata dawo kamar budurwa. Sosai take gyara kan ta.

Kamar yadda sukai da boka kan zataje in biki ya rage sati haka ce ta faru.

Da taje ce mata yayi zai mata rubutu a jiki a wanke a bawa Aslam yaci a abinci ko a lemo.

Ba kunya haka Pretty ta tube ya gamai mata rubutu daga nan kuma sukai masha'ar su.

Sosai Pretty taji haushin bata mata aiki da yayi dan ita dan Aslam tayi.

Shi kuwa bokan ta jin dadin da ta kara ya kara saukar masa da wata matsananciyar sha'awar ta.

Barin ta zai yi ta dana na dan lokaci dan ya kumai wa kan sa alkawarin bazai taba barin Pretty ba sai ta zama matar sa.

Haka ya kara hada mata wasu tsafe tsafen nasu sannan ta koma gida da murna.

Sosai take cigaba da kara gyara kanta duk dan ta burge Aslam.

A kwana a tashi har an fara shagalin bikin Aslam da Fauziyya (Pretty).

Event an tsara wajen guda biyar. Sosai Aslam ya saki kudi.

Momy da Dady kuwa kamar ba bikin dan ta ake ba dan ba abinda ta tsara zatai.

Haka nan ko su Mami bata fadawa ba dan kar Asma'u ma ta sani.

Ranta a matukar bace yake akan bikin nan dan shi kansa Aslam din tausayi yake bata.

Asma'u kuwa tinda lokacin bikin Aslam.ya kama take fama da faduwar gaba. Ga wasu mafarkai da take da Aslam.

Duk ta kara lalacewa, Ita aba ba jiki ba dama. dan ma addu'a da suke ita da Mami ba sanya.

Dan sai su kwana suna mika kukan su ga Allah.

Kullum suna waya da Buhari da Zainab haka ma Sir Sabir yana kira su gaisa.

Yau ma kamar kullun bayan sun dawo daga harami tayi wanka tazo falo ta zauna.

Tagumi ta saki tana tunanin Aslam lokacin da suke zaune a garden a ranar da Dadyn ta ya sanar da ita batun ya bada ita ga Aslam.

Lokacin da suke zaune ya yi murmushi ya ce da ita,
"Alhamdulilah nagodewa Allah.Zuciya ta ke kadai takewa na amince rike ta har abada."
Chapter 32 · 0% Book details