← Book details Asma'u Husnah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 18 OF 61

Sashe 18

Asma'u Husnah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Ameen!"
sannan suka mike suka koma daki. Sallama sukai wa su Dady kowa yayi dakin baccin sa.

Duk abinda ta saba tayi sai da ta gama su sannan ta kwanta.

A haka ma sai da suka kara yin waya kafin su kwanta.

Sun jima suna waya sannan sukai sallama bayan sunyi alwala.

Washe gari lahadi yini sukai tare. Ko gajiya da zama tare ko hira basa yi.

Sai dai ka jiyo murmushin su ko kaji dariyar su.

Mami dai bar musu falon tayi, haka suka yini a gidan.

Tare suka ci abinci suka yini sallah ce ke daga su.

Bayan sunyi sallahar la'asar, ne ya ce, Asma'u ta shirya ssu fita.

Wanka ta shiga tayi, ta fito ta saka Wata doguwar riga fara an mata ado da jan stones sai Jan mayafi da jan cover shoe. Wata jar jaka ta dauka.

Turare ta fesa ta fito tai dakin Mami.
Mami na zaune tana kallo Asma'u ta shiga

Kallon ta Mami tayi ta ce,
"Sai ina kuma?"

Murmushi Asma'u tayi ta ce,
"Zan raka Yaa Aslam ne."

"Toh! A dawo lafiya."
"Allah yasa."
Ta mike tayi waje.

A kasa ta samu Ya Aslam ya na sanye da farin wando da jar riga. Takalmin kafa sa ma ja ne.

Sai tashin kamshi yake yayi kyau. Yana ganin Asma'u yasaki murmushi ya ce,
"Wow My baby tayi kyau munyi anko."

Murmushi ta yi ta ce,
"Ka fini yi."

Wayar sa ya zaro ya ce,
"Zo mu dau selfie."

Gefen sa ta karasa ta tsaya matsowa yayi jikin ta, ya dauke su.

Ya musu fin kala biyar sannan ya dinga daukar ta.

"Yaa Aslam ya isa haka."
Ta fada saboda taga ba alamar tsayawa.

"To muje."
Ya fada yana kamo hannun ta. Fita sukai ya karasa gun Baba ya amso key mota suka shiga.

Shoprite suka shiga suka wuce cinema. kallo suka danyi sannan suka fito suka shiga ciki.

Sun shiga suka nufi gun kayan sakawa. Sosai yake jidar mata dogayen riguna masu kyau da tsada.

Haka ya nufi gun takalma da jakun kuna. Sosai ya kashe mata kudi sannan suka nufi gun alawa ya siya mata ice cream.

Bayan anyi total ne aka dibi kayan akayi wajen mota dashi.

Suna tafe suna hira taji ta bugi abu tayi baya zata fadi.

Da sauri ya rikota ta fada jikinsa. Kafin ta dago taji Yaa Aslam ya dago ta yana cewa,
"Ba dai matsala ko?"

Kai ta daga masa, kamshin turaren da taa shaka shi yasa tai saurin dagowa.

Ai kuwan shine, yana sanye da bakin wando da jar riga, yayi kyau sosai dashi.

Ba kowa bane face Sir sabir.
"Sorry!"
ta furta a kasan leben ta.

Yaa Aslam ne ya kama hannun ta suka bar wajen.

Sabir kowa kallo yabi su dashi. Yana me lumshe idon sa.

Suna fita ya ce,
"Sannu Baby na ko na dauke ki ne."

Kai ta girgiza ta ce,
"A'ah nagode zan iya tafiya ai."

A hankali suka karasa gefen Mota suka shiga suka bar wajen

Suna zuwa gida ana kiran sallah isha'i

Daki suka shige sukai sallah sannan suka sauko kasa.

A kasa suka samu har Dady ya dawo. Saannu da zuwa sukai masa sannu da zuwa

Abinci suka ci sannan suka koma falo ana hira.

Sai karfe tara suka tafi makwancin su.

Washe gari Monday. Tana gama abinda zatai ta shirya cikin wata pink kalar doguwar riga. Milk mayafi da takalmi ta saka. Sai pink kalar jaka.

Batai kwalliya ba fuskar ta daga hoda sai man lebe. Wajen Dady taje. Tare suka karya. Sannan ta fito.

Yaa Aslam ta gani a falon sama. Karasa wa tayi gun sa. Yana sanye da Bakin wando sai blue kalar riga mai dogon hannu.

Yayi kyau sai tashin kamshi yake.
"Yaya nah ina kwana?"

Ta gaishe da shi tana zama a hannun kujerar da yake.
"Lafiya lou. Ya Baby na ta tashi."

Murmushi tayi ta ce,
"Lafiya Alhamdulilah."
Sannan ta mike ta sauka kasa.

Basket din abincin sa ta dauko wanda ta zuba masa komai a fulas din sa.

"Mu tafi?"
Ya fada yana tambaya.

Kai ta gyada masa, dakin Mami suka yi sukai mata sallama sannan suka wuce zasu sauka.

Mantawa tai bata je gun Yaya Buhari ba. Wannan yasa tai ce
"Ina zuwa!"

Dakin yaa Buhari ta dosa, yana kwance ko alamar tashi bai yi ba.

Kara tai masa a kunne da sauri ya mike a firgice. baya ta dan ja ta ce,
"Ina kwana?"

Ta fada tana ja da baya a hankali. Ganin ya mike yasa tai saurin fita a dakin tana dariya.

Yaa Aslam dake tsaye yana jiran ta ya ga ta fito har ta sauka shima yabi bayan ta yana murmushi dan yasan tayi tsokanar da ta saba.

A bakin mota ya ganta a tsaya budewa yayi ta shiga ya rufe sannan ya shiga bangaren sa.

Tafiya suke a hankali suna hira abinsu. Har kofar department din su ya kai ta sannan ya kara mata kudi akan wanda Dady ya bata.

Sallama yai mata ya ce,
"Sai ya dawo daukar ta."

Sai da ta ga tafiyar sa sannan ta nufi ajin daukar darasin su.

Tana shiga taga Zainab zaune, karasawa tayi gun ta suka gaisa.

Batai minti biyar da zuwa ba sai ga Sir Sabir nan ya shigo.

Sanye yake da Milk din shadda ana mata aiki da milk din zare. Yayi kyau dashi.

Kasa tayi da kanta tuna haduwar su jiya. Lectures yake musu da yayi tambaya zai yi pointing din ta.

Tin tana jin kunya har ta sake tana bashi amsa. A haka suka gama lectures din.

Da zai fita ya duka zai dauki wayar sa, yai mata magana a hankali cewar ta same shi a office.

Wata faduwar gaba taji ta doke ta. A hankali ta daga kai ta kalle shi. Ita yake kalla saurin kawar da kan ta tayi tana wasa da yatsun ta.

Waje ya fita. Wata ajiyar zuciya ta sauke, ita bata san hadin ta da malamin nan ba amman dai tana ji yana burge ta ko dan saukin kansa.

Da kamar baza taje ba sai kuma ta ce da Zainab zataje ta dawo.

Fita tayi ta nufi office din nashi jiki a sanyaye.

Knocking tayi ya bata izinin shiga. Da sallama, ta shiga office din ta tsaya daga bakin kofa. Kallon sa tayi sau daya ta dauke idon ta.

Yana zaune a kan kujera gaban sa, farfesun kifi ne da Doya da kwai.

Kamshi ya cika office Din ci yake kamar baya son ci fuskar sa kuwa sai bata ta yake kamar mai cin magani.

Kallonsa ya maida kan ta ya kasa dauke ido daga kallon ta. Yana son yarinyar nan amman bai san ta inda zai fara ba.

Kawar da tunanin da yake yayi ya ce,
"Zo nan!"

Da kamar baza taje ba sai kuma ta dan matsa.

Kallon ta ya kara yi ya rasa mene dalilin kiran nata.

Kai ya dan shafa, ya ce,
"Zo kici!"

Kai ta girgiza ta ce,
"Na koshi."

Fuska ya bata, ya ce,
"Zamu bata inda zan na baki abu kina kinci. Maza zo kici."

Matsawa tayi ta zauna a kasa ba dan zata cin ba. Fulas din ya matsar mata dashi ya ce,
"Bismillah!"

Agogon hannun ta kalla sannan. Ta ce,
"Zan je nayi Assignment fa."

Ta yi maganar murya a shagwabe dan har ga Allah ta riga da ta saba da shagwaba in tana abu. bama in tana bukatar abu.

Sabir kuwa jin muryar da take magana da ita yasa nan da nan tsigar jikin sa ta mike.

*INDABAWA*
[1/18, 14:17] Maryam S Indabawa🥰: *Asma'u Husnah*

Na *Maryam S Indabawa*
*Mans*

🌐 *HAJOW* 🌐
*Hakuri da Juriya Online writers*
*Gidan Amanci da albarka*

Dedicated to *My Lovelly Momy*

*96-100*

*KARE GIDA DA ALQUR'ANI DA ZIKIRAI DA SALLAH: Yana Daga Cikin Abinda Ke Taimakawa Wajen Tarbiyyantar da Yara Shine tsare Gidan Ta Hanyar Yawan Karatun Alqur'ani da Zakirai Musammam Zikiran Safe da Yamma Da Kuma Yin Sallolin Nafila a Cikin Gidan.

Sabir kuwa a jin muryar da take magana da ita yasa nan da nan tsigar jikin sa ta mike.

Idon sa ya kada yai ja, lumshe ido yayi ya bude, ya ce,
"In in jiya da wa na ganki?"

Yayi tambayar ba tare da yasan lokacin da ta fito ba.

Kallon sa tayi ta ga ya canja amman bata kawo komai ba. Dan haka ta ce,
"Ni da Yayanah ne!"

Kai ya gyada kawai ya dauki waya yana dane dane.

Kallon sa tayi ta kuma narke murya ta ce,
"Naje?"

Kallon ta ya tsaya yi, kafin ya ce,
"Kunyi waya da Maryam!"

Kai itama kawai ta gyada masa. A zahirin gaskiya baya son ta tafi ta bar shi amman dole ta tafi.

Dan haka ya dinga mata tambayoyi. Sannan ya bata izinin tafiya.

Tana tashi ya bita da kallo har ta fita ta rufo kofar idon sa na kan ta.

Ido ya lumshe, yana me dafe zuciyar sa.

Tana komawa ta bawa Zainab labarin abinda ya faru da yadda suka hadu jiya.

Zainab dariya tayi ta ce,
"Wai ke baki gane wani abu ba."

Asma'u ta ce,
"Me zan gane me ya faru?"

Dariya kawai Zainab tayi ta ce,
"Allah bazan fada miki ba. In kin gano ka zo kiban labari."

Share maganar Asma'u tayi dan ta san Zainab akwai jan rai an kana son abu.

Daga haka suka zauna aka shiga wani lecture din.

Karfe hudu dai dai Yaa Aslam yazo, kiran Asma'u yayi bata dauka ba. Yasan tana massalaci. Dan haka ya fito ya zauna daga kasan bishiya.

Yana zaune ya hango Sir Sabir ya taho a cikin motar sa.

Kallon ssa yayi ya dan saki tsaki sannan ya dauke idon sa. Ya rasa dalili shi dai kawai gayen bai masa ba.

Shima kuma ta bangaren Sir din ya ganshi sai dai shi a duk sanda suka hadu sai yaji wata faduwar gaba

Yana zaune a haka Munasha ta gano shi. Gunsa ta nufa tana canja salon takun ta.

A hankali ta karasa gun tai masa sallama. Dagowa yayi ya na kallon ta daga sama zuwa kasa.

Ita kuma sai gyara tsayuwa take. Baki ya yamutse, kamar yaga kashi ya dauke kai.

Wani iri taji amman duk da haka ta dake ta ce,
"Sannu fa!"
Chapter 18 · 0% Book details