← Book details Asma'u Husnah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 27 OF 61

Sashe 27

Asma'u Husnah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Jama'a sun cika gidan makil da mutane. kowa sai mutuwar Dady yake ji, Dady mutumin kirki me kawaici da Hakuri da taimako.

Dan haka kowa abin alherin sa yake fada da masa addu'a.

Mami karfin hali kawai take domin tasan ta rasa farin cikin ta. Ta yi asara da baza ta taba maida kamar ta ba.

Dan rashin Dady a garesu ba karamin gibi bane.

Ana ta amsar gaisuwa Mami kuwa ta yi nisa cikin tunani, ga Asma'u, ba wanda tafi ji.kamar Asma'u.

Asma'u kuwa da magariba ta farfado. Tana ta shi tasa kuka ina Dadyn ta.

Sai kuma ta kuma fashe wa da Kuka ta ce,
"Momy dan Allah ku kaini wajen Mami da Dady dan Allah Momy Dady bai mutu ba ko? Momy kada kice min ya mutu."

Sai wani kukan Momy ma sai da tayi hawayen dan ba karamin tausaywa Asma'u tayi ba.

Allura Dr ya karai mata ganin tana neman fita daga hayyacin ta.

Sai da Dady yai kwana uku aka sallamo Asma'u, gida suka taho da Momy dake wajen ta in kaga Asma'u zaka ga ta rame sosai sai kace wacce ta dade tana jinya.

Aslam da tare suke jinya a asibiti shima duk ya rame ya yi duhu.

Tare suka dawo, Asma'u na zuwa gida tayi wajen Mami, ta rumgume ta tana wani kuka mai ban tausayi.

Kuka sosai suka yi sannan Mami ta dago ta tana kallon ta.

Ta rame har abin yai yawa.
Buhari ya ce,
"Mami ga Asma'u nan bata cin abinci ko tea taki amsa ta sha."

Kai Mami ta girgiza ta jata jikin ta tana shafa bayan ta ahankali a hankali.

Zainab da tinda akai mutuwar take zarya daga asibi zuwa gidan yau ma tana gidan.

Dakin Asma'u suka shiga, Asma'u da ta kasa daina zubar hawaye daga idon ta.

Abinci Yaa Buhari ya dauka ya kai mata ya ce taci amman sam taki ci.

Yaa Asalm ya fadawa. Aslam da kansa ya shigo gidan ya shiga har dakin ta ya tadda ta kwance akan gado.

Zama yayi a gefen ta ya dago ta. Tana ganin shine ta fada jikinsa tana sakin wani kuka mai ban tausayi.

Rumgume ta yayi yana lalashin ta da kalamai masu nuni ga ban hakuri har tayi shiru sai ajiyar zuciya da take saukewa.

A hankali ya dinga bata baki har ta yadda ya dinga bata abinci a baki.

Ci take tana yamutsa fuska dan ba dadin sa take ji ba. Har wani daci yake mata a baki.

Idon ta kuwa ya kasa tsayar da hawaye, a haka ta dan ci ta ce ta koshi.

Tin daga lokacin kullum Asma'u na gefen Mami, dan ko bacci ta koma kullum tana gefen ta.

Kullun kuwa Asma'u da zazzafi take kwana ta tashi. Amman da Mami ta ce zata bata da lafiya zata ce ta ji sauki.

Ranar bakwai kuwa Asma'u kamar me kuka ta dinga yi dan har numfashin ta daukewa ya dinga yi.

Yaa Aslam da Sir Sabir su suka tsaya akan ta.

Da kyar suka samu numfashin ta ya dawo dai dai.

Bayan bakwai kowa ya watse sai Momy da Aslam.

Suma ana yin kwana goma Momy ta fara shirin tafiya. Hakuri sosai ta dinga bawa Mami.

Sannan ta zaunar dasu gaba daya, ta kara basu hakuri sannan ta bawa Mami kudi masu yawa.

Haka Momy ta tafi gidan ba dadi daga Buhari sai Aslam da Mami da Asma'u.

Asma'u da ta zama shiru shiru ko magana batayi. In anyi abu sai dai ta kalli mutum ta dauke ido.

Aslam kuwa kullum ya zauna sai ya san yadda zai sa tayi dariya.

Aslam shike sa Asma'u yin hira ta dan sauko.

In kuwa ba haka ba sai dai ta zauna tai ta zubar hawaye.

Yau ma kamar kullum tana kwance akan gado, ba abinda take sai zubar hawaye tana tunanin Rayuwar su da Dady.

Murmushi ta dan saki sai kuma, kuka da ya kwace mata.

Aslam dake tsaye a kofar ya na kallon sanda tai murmushi sannan kuka yazo ya karaso gun ta da sauri.

"Haba *Husnan Dady* yanzu haka zamu ta rayuwa kenan kullum kin ki ki sake, kina tunanin Dady zai ji dadi a halin da kike ciki. Haba *Husnah* a ko da yaushe Dady bai da magana da ya wuce yasan ko bayan ransa *Husnah* baza tai kuka ba saboda yasan damu. To menene amfanin namu da mu na nan zaki na kuka. Haba *Husnah* dady ba abinda yake nema gun ki sai addu'ar ki. Dan Allah ki daina wannan kuka. In ba haka ba ni bazan iya jurar ganin kukan ki ba zan tafi in hakan kike so."

Hawayen ta, ta goge ta ce,
"Na daina Wallahi Yaa Aslam na daina. Kar ka tafi ka barni."

Murmushi Aslam yayi ita kuwa duk da hawayen da take yi gogewa wani ne yake kara daduwa.

Jikin sa ya jata yana lallashin ta.

*Hmmm kulli Nafsin xa'ikatul Maut.*
*wannan haka yake*

*Karki kuce saboda na sa Dady ya mutu. Haka rayuwa take, muma wata rana sai mutuwa.*

*Hmmm kuyi hakuri haka tsarin littafin yake. In ba haka ba wani abu bazai faru ba. Nagode*

*Nusaiba S Indabawa*
Ki daure ki karanta littafin nan.

Lol wai ita indai nayi littafi wani ya mutu bata karantawa saboda tausayi.

*To sisto ki karanta dan nasan kina son karantawa. Mutu a kuma dole ce. Ke yanzu ina Dady, ya rasu. Sai dai muyi masa addu'a Allah ya kara masa rahama Ameen!*

ALLAH KA JIKAN DUKKAN MUSULMAI. KA JIKAN YAN UWAN MU, DA KAKANNIN MU, DA IYAYEN MU DA YAYUN MU DA KANNEN MU DAMU KAN MU IN TAMU. TAZO

AMEEN!

*INDABAWA*
[1/18, 14:21] Maryam S Indabawa🥰:  *LABARIN RAYUWAR*

*Asma'u Husnah*

Na *Maryam S Indabawa*
*Mans*

🌐 *HAJOW* 🌐
*Hakuri da Juriya Online writers*
*Gidan Amanci da albarka*

Dedicated to *My Lovelly Momy*

141-145

An Kar6o Daga *Abi-Zarrin (ra)* Yace: *Manzon Allah(ﷺ)* Yace: *“Idan 'Dayanku Zai tsayar da Sallah Kada Ya Goge Kasa, Domin Rahama ce Take Fuskantarsa”.* (Mutane Biyar Suka Ruwaitoshi) da Sanadi Ingantacce._

Aslam yayi na mijin kokari wajen sauyawa Asma'u rayuwa.

Dan kullum cikin daukar Asma'u ya kai ta wajen shakatawa ko ya kai ta shopping.

Banda fina finen da yake siyo mata na ban dariya.

Sai da yayi wajen wata biyu a kano sannan ya koma saboda wajen aikin sa.

Duk da tafiyar sa duk wata kulawar da yake bata bai daina ba sai daduwa dda ta karayi.

Sabir kuwa har Mamah ya kawo gida tai wa su Mami gaisuwa.

Haka Maryam ma takanas ta zo kano dan Asma'u. Asma'u ma taji dadi.

Haka nan Maimuna ma tazo tai mata ta'aziyya da yan department din su.

Da kyar Asma'u ta koma asibiti, ta cigaba da rayuwar ta.

Sabir ma yana zuwa akai akai yana duba su ya gaida Mami.

Pretty ce zaune kamar an mata allura ta mike ta dauki ATM din ta da kudi ta zuba a jaka.

Fita tayi ta tsaida mai Napep ta shiga. Tasha kai tsaye ta nufa.

Tana zuwa ta hau motar Niger.

Suna sauka Pretty ta tafi hotel.

Sai da tai bacci ta huta tai wanka sannan ta ci abinci.

Mikewa tayi sai kace wacce zata tashi sama.

Fita tayi daga hotel din ta tsaida mai napep. Yana tsayawa ta fada masa inda zata sannan ta hau suka tafi.

Yana tsayawa ta biyashi kudi sannan ta shige wajen.

Waje ne kamar jeji haka ta kutsa kai. Sai da tayi tafiya mai nisa sannan ta karasa wajen

Yar bukka ce, shi kuma yana zaune a gefen ta.

Jikin sa ba komai sai ganye da yayi tufa da shi.

Kalar fatar jikin mutumin baka kirin, haka nan jikin mutumin sai tashin wari yake.

Idanun sa jajir kansa gashi ne yayi yawa dan sai a iya kitso ma akan shi.

Yana zaune gefen sa tukwane ne. Tin da Pretty ta karasa wajen yake binta da wani fiti nan nen kallo.

To kayan dake jikin ta ne kai ba zakai tunanin yar musulmi bace.

Zama tayi nesa dashi dan ita ma tana kyamar sa.

"Sannu boko na kan tudu."
Ta fada tana kallon sa.

Bakin sa ya bude wanda hakoran dake ciki sun zama ja dasu.

"Kinji shiru ko?"
Ya tambaye ta.

Kai ta daga masa, murmushi yayi ya ce,
"Eh kamar yadda na fada miki aikin yana da wahala ne,"

"Toh! Malam......"
Tsawa ya daka mata. Ya ce,
"Kar ki kara ce min Malam."

"Dan Allah ka taimaka min wallahi zuciya ta zata iya bugawa in ban samu Aslam ba ka taimaka min."
Kai ya daga ya ce,
"Na fada miki aikin yana da wuta. Dan Aljannin da zai miki aikin ya ce, sai ya tara da ke tukkuna."

Ido ta zaro ta ce,
"Aljannin."

Kai ya gyada mata. Ya ce
"kar ki damu ki kwantar da hankalin ki. Ta jikina zai yi amfani dake,"

Ya fada yana lashe lebe. Kallon sa tayi a zabure ta nuna shi da yatsa, ta ce,
"Kai!"

Kai ya gyada ya ce,
"Eh ni."

Wani kallo ta watsa masa ta mike tabar wajen.

Tana fita tayi gidan kawar ta wacce ta hada ta da bokan.

Tana zuwa ta zube mata abin da ya faru, dariya kawar tata ta hau yi ta ce,
"Amman wallahi har kin ban kunya, dan aljanni ya neme ki shine me?"

"Ke dallah shine fa zai kusance ni. Haba kinsan fa ya yake, warin jikin sa ma kadai ya ishe ni."
Pretty ta fada tana toshe hanci sai kace a gaban sa take.

"Kinga ki ajiye duk wannan a gefe wallahi in har yayi abunda ya bukata ko to bukatar ki ta gama yi. Kin samu Aslam dan shi da wannan kwailar yarinya har abada dan nasan ko kallo baza ta ishe shi ba."

Kallon ta Pretty tayi. Ta cigaba da magana.
"Muma duk Boka yayi abinda kike tsoron yi dashi. Kuma ya kusan ce kinki zaki ji abinda baki taba ji ba.

Kallon ta Preetty tayi a ranta tana son samun Aslam amman kuma tana kyamar ta yadda zata je wajen Boka.

A haka kawar tai ta zuga ta har taji zata je dan biyan bukatar ta.

Gida ta tafi tana tunanin taje ko kar taje.

Wata zuciyar na cewa taje wata kuma tana hanata zuwa.
Chapter 27 · 0% Book details