← Book details Asma'u Husnah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 17 OF 61

Sashe 17

Asma'u Husnah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

" *Husnah* kinyi kyau. Wallahi kin fi kyau a fili akan hoto. Hoto yana ragen kyan ki. Kinga yadda kika kara girma kuwa. Allah ko yanzu ai mana aure nasan zamu samu babies ko?"

Ya karasa fada yana mata rada a kunne. Mikewa tayi zata bar gun ya kamo hannun ta.

Komawa tayi ta zauna ta yi kasa da kanta. Murmushi yayi ya ce
"Ko ba zata iya samu bane."

Duka ta dan kai masa, ta ce,
"Kai Yaa Aslam ko gaisawa ba miyi ba."

Ta fada dan ta kautar da maganar. Dariya yayi ya ce,
"Wayo ko? To ina yini Baby nah, ya kika tashi daga bacci kin yi mafarki na. Na miki kiss ko? Na miki....."

"Haka ake gaisuwar" tai saurin katse shi. Kai ya dan sosa, ya ce,
"Ya ake yi. Kinsan in ina tare dake komai yakan bace min."

Murmushi tayi tace,
"Wannan Yayan nawa."

Shima ya ce,
"Wannan Kanwar tawa."

Sukai dariya gaba dayan su. Sannan ta ce,
"Yaya ya hanya?"

"Lafiya Alhamduliah! Sai kika ganni ko?"
Kai ta gyada ya ce,
"An rage mana sati daya ne, shine na taho."

"Amman naji Dadi, ina Momy da Dady "
ta tambaya.

Ya ce,
"Suna nan lafiya suna gaishe ki Dady ya bada sako a baki."

Murmushi tayi ta ce,
"To nagode!"

Dakin ta kalla ta ce,
"Yaushe kazo ne?"

Ya ce,
"Tin karfe biyu."

"Kaci abinci.?"
Ta tambaye shi.

"Kema kinsan Mami baza ta bar 'dan ta da yunwa ba."
"Uhmm ina Mamin take ne?"

"Tana dakin ta. Dauko mana ice cream din musha kar ya narke."

Mikewa tayi ta kawo suka fara sha yana bata a baki har suka shanye.

Hira suke abinsu kamar me, in ka kalle su sai sun baka sha'awa dan sun dace da juna.

Sosai take bashi labarin ckul din ta shima yana bata labarin yanayin wajen aikin su. Har akai magariba ya tafi yayi sallah ita ma tayi sama. sannan suka dawo falo.

Mikewa yayi zai fita ta ce,
"Ina zaka?"

"Ina zamu dai?"
Ya fada yana nuna mata waje.

Mikewa tayi tabi bayan sa. Garden din gidan suka nufa suka zauna a kujera suna facing junan su.

Indai Yaa Aslam yazo kano nan ne wajen zaman su,

" *Husnah* ina son ki ina kaunar ki kece farin ciki na kece rayuwa ta."

Murmushi tayi. tayi kasa da kan ta
Kallon ta yayi ya ce,
"Duk adadin zancen da zan miki *Husunah* bazan yi san rai na ba. sako na zuciyata bakina ya furta ido ba bazai boye ba. kinyi kyau ke mai kyau ce, abu da zan sa ai mana. Zan sa ai mana sahamaki, abadan bazamu rabu ba."

"Sha makin me?"
Asma'u ta tambaya.

"Aure man! Asma'u aure shine shamakin da bazai taba raba mu ba."

Murmushi tayi ta ce,
"Ka iya Sassauta harshe ka wajen fada min abinda zai min dadi. Ya Aslam Wani lokacin ina tsoran kar ka guje min dan duniyar ga da fadi. Dare da rana ban da burin da ya wuce muyi tadi."

Murmushi yayi ya ce,
"Asma'u kenan Kimin hukunci yadda ya dace a sanda nai.miki laifi. Amman sai ki min adalci a sanda bani da laifi. In kuma naki na baki kulawa ki hada rami me xurfi. a sanda na canja wani hali kimin nasiha baki guje ni ba. Ki fahimce ni aduk abinda zan miki ki auna kiga a wane hali zan miki abin. Ni dai nasan a cikin hayacina bazan taba miki abinda bakya so ba."

Asma'u ta ce,
"Yaya Aslam kamar yadda Kayi dakon soyayya ta a ko ina ka bayyana ta a fili ina gudun masu yin kwace su san ina da dalilin son da nake maka kar su kwacen ka. Tarrayar mu dakai bata da karshe dan zuciya ta da son ka ta girma ta rayu kuma da son ka zata mutu."

Murmushi yayi ya ce,
"Asma'u kenan ba wacce zata kwace miki ni. Ni naki ne ke tawa ce."

Shiru tayi sannan ta dago idon ta har ya sauya kala. A kidime ya sauko daga kujerar da yake, yana tambayar ta
"Menene? Me nayi miki?"

Kuka ta fashe dashi. Jikin sa ya janyo ta yana lalashin ta har ta samu tayi shiru sai ajiyar zuciya da take sauke da karfi

Bayan ta yake shafawa a hankali har ta koma sauke ta a hhankali. Dago ta yayi ya ce,
"Me nayi miki?"

Kai ta girgiza. Ya kalle ta ya ce,
"Dan Allah ki fadan me yake damun ki zan fiki shiga damuwa in baki fada min ba."

Kuka ta kuma fashe da shi ta ce,
"Wallahi Yaa Aslam ina jin tsoro! Ina jin tsoron kar na rasa ka."

Sai ga wani kukan nan. Rumgume ta yayi tsam yana jin wani son ta na kara ratsa shi.

A hankali ya fara magana. Ya ce,
"Asma'u kinsan wani abu kuwa. Nasha yin istihara akan al amarin mu amman a ko da yaushe kara jin son ki da kaunar ki nake. Wannan ya nuna min cewa *ke alheri ce* dan in da ke ba alheri bace da Allah zai na yayen son ki na. Asma'u tin kina yarinya nake son ki tin baki da abinda za'a so ki dan haka ki daina sawa wani abu zai sa na rabu dake, ki daina tsoron komai ki dauka ni naki ne, ke kadai. Kamar yadda kema zaki zama tawa ni kadai. Haba ni dai nasan *Husnah* *tawa ce* "

Ya dago da kanta yana goge mata hawaye. Mikewa suka yi. Ya ce,
"Smile!"

ai kuwa sai ga shi nan ta saki murmushi, ya kai hannu zai taba dimple din ta tai saurin kaucewa.

Zama yayi yana dariya, ya daga hannu ya kira ta. Alamar tazo.

Kai ta make, murmushi yayi ya ce,
"Zo mu zauna dake masoyiya na amince dake a zuciya, aure na dake na shirya amana zan rike ba gajiya. Tinda kin min so na gaskiya, dan haka ban barin ki kisha wuya. Zan kula dake zinariya."

Matsawa tayi gunsa, ta ce,
"Naji dadi wazai min murna, nayi godiya a gareka, tinda kakira ni matar ka, zana baka dukan hakkin ka, ni bazan yadda a kushe ka ba. Tinda na yaba da halin ka saboda iya takun ka natsuwar ka, da tsarin ka ni na so ka.
Na zo mu zauna dakai a rayuwa na amince dake muyi auren sunnah."

Kallon ta yake yana mamakin kalaman ta, dan yasan ba sosai Asma'u ta fiya magana a gaban sa ba saboda kunyar ta. ya ce,
"Ni dake zan daura aure na zamo ango ke amarya, dakina a gidana zaki tare ki rangada kwalliya ki min ado me kyau. Farin cikin zaya daure, hawayen ki ni zani share, dake zan zauna na more. Miyi rayuwa mai inganci bazan taba saki kuka ba."

Ta ce,
"Kai ne zabi Allah yayi mini. Naji dadi kuma kayi mini. Ga hannu na kama ka hayar mini. Gidan aure ka kaini ka ajiye ni. A mata zai zama babu kamar ni. Matsayi mai girma zana baka. In kula dakai muyi soyayya mai tsafta da rikon amana."

Mikewa yayi ya matso gun ta. Kasa tayi da kanta.

"Oh my God! Ji yarinya sai kace bake kika gama magana ba yanzu kuma sai kunya. Wannan kunyar taki."
Ya fada yana nuna ta sai kuma yayi kwafa ya ce,
"Zan cire tane, wata rana sai kin manta da kin taba jin kunya ta kamar haka."

Mikewa yayi ya kalli agogon hannun sa. Ya ce,
"Tashi mu shiga ciki tara saura."

Da sauri ta dago ta ce,
"Dan Allah da gaske?"

"Zo ki gani."
Tayi wajen sa.

Rumgume ta yayi ya nuna mata.
"Uhmm to sake ni, Dady ya dawo tin dazu."

"Muna nan soyayya bamuji shigowar sa ba."
"Kai kayi soyayya ni banyi ba."

Ta fada tana yin gaba. Kamo ta yayi ya ce,
"Au ke bakiyi ba?"

Kai ta girgiza masa ta ce,
"Ni kuwa nayi soyayya."

Sakin ta yayi ta dan matsa ta juyo ta ce,
"Ina ni ina soyayya da yaya nah. Wallahi kunya nake ji."

Ta ruga a kuje. Murmushi yayi yabi bayan ta.

Falo ta shiga tana haki kallon ta Dady yayi ya ce,
"To fah Aslam yazo an manta da Dady ko *Husnah* "

Gun sa tayi ta ce,
"Aah wallahi ban san dare yayi ba muna garden!"

*Husnah-Aslam*
*Husnah-Sabir*

Na sameku lafiya ya al amura. Allah ubangiji ya taimake mu.
Ameen

Nagode masoya masu comment da masu like da kowa ma.

*INDABAWA*
[1/18, 14:16] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR*
*Asma'u Husnah*

Na *Maryam S Indabawa*
*Mans*

🌐 *HAJOW* 🌐
*Hakuri da Juriya Online writers Association *
*Gidan Amanci da albarka*

Dedicated to *My Lovelly Momy*

*Mahaifiya ta abar alafahari na. Allah ya sa ki gama da duniya lafiya*zn

91-95

*Wani mutum yacewa Hasanul Basry:Ya Aba Sa'id ina kawo maka kukana akan 'Ke'kashewar zuciyata saiyace masa:Ka ladabtar da zuciyarka da ambaton Allah*

Aslam ne ya shigo shima gefen Dady yayi shida Asma'u suka sa shi a tsakiya suna masa sannu da zuwa.

Yaya Buhari ya ce,
"Wallahi Mami a gidan nan ba a so na."

Sai a lokacin Aslam ya kula da shi. Dariya yayi ya ce,
"Aah 'kanina ashe ka dawo,"

Kai ya dauke wai yayi zuciya. Dariya sukayi.

Asma'u tayi gefen sa ta ce,
"Sannu bro ya aiki?"

Banza yai mata. Kukan karya ta fashe dashi in kaji yadda ta fashe dashi kayi zaton na gaske ne. Nan da nan Yaya Buhari ya jata yana bata hakuri.

Dariya ta saki ta ce,
"Daman nace sai ka.kula ni."

"Kai amman yarinyar nan kinga lago na."
Ya fada yana daga ta daga jikin sa.

Daga haka suka hau hira. Har karfe goma suna falo sannan Aslam da Asma'u suka tafi gun cin abinci.

A can ma sun jima suna hira sannan suka ci abincin cikin so da kauna.

Aslam ya ce,
" *Husnah* ji nake ina ma anyi abin nan gidan mune mu sha soyayyar mu."

"Lokaci dai. Allah nuna mana."
"Ameen! Allah har na hango yadda zamuyi soyayya nake."

"Kai Yaa Aslam! Kana son soyayya."
"Dole naso ta *Husnah* dan wanda bai soyayya bai son dadin duniya nan ba soyayya tayi. Allah kuma ya bar mu da masoyan mu."
Chapter 17 · 0% Book details