Sashe 83
Matar Damisa Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Mommy ɗagowar da zatayi idanuwanta suka sauƙa akan Triplets suna tsaye suna kallon duk abubuwan da ke faruwa, Amrish ganin yanda Daddynsu ya faɗi aka ɗauke shi yasa jikinta ya soma ɓari yana kakkarwa kamar mejin sanyi, ta tsaya cak ta kasa motsawa a yayinda Angel da Areeph suka nufo gurin Mommy suna faɗin "Mamy meya samu Daddyn mu?..." dake sunan da suke ƙiranta dashi kenam,
Mommy tace "babu komai ta ƙarisa maganar tareda goge hawayen fuskarta..."
Areeph yace "Mamy kina kuka kuma kina ce mana babu, shin meya samu Daddyn mu kuma ina Mommyn mu take?..."
Itama Angel tace "wannan Jaririn waye?..."
Mommy tace "Jaririn Mommynku ne ta haihu...". Angel ta kuma cewa "toh tana ina Mommyn namun?..."
Mommy ta kasa basu amsa kwatsam idonta ya sauƙa akan Amrish wacce take tsaye guri ɗaya sai fitar da numfashi take sama-sama, a tsorace mommy ta tashi ta nufi wajenta tareda faɗin "takwara meya faru ne? dan Allah ki temake mu kar ciwonki ya tashi please, ki kwantar da hankalinki kinji koh..."
Haka take rarrashin ta cikin kulawa domin ita daman Amrish batada cikakkiyar lafiya an haifeta da ciwon zuciya amma ba'a ankara ba sai bayan ta soma girma, zuwa yanzu dai sau biyu ciwon yake tashi, shiyasa akafi lallaɓata kuma tanada raunin zuciya bata juran damuwa, fargaban mommy a yanzu shine kar ciwon ya tashi a halinda take ciki yanzu...
Amrish ba abunda take faɗi illa "Mommy! Daddy!! Mommy!!! Daddy!!!!...". Ido yayi zuru-zuru. Mommy tasa hannu ta rungumeta tana rarrashinta ta ɗayan ɓangaren kuma tana riƙe da Jariri,
Can saiga su Uncle Artaff sun sauƙo yace "Suma yayi amma yanzu ya farfaɗo yana buƙatar hutu domin jikinsa yahau temporary...". Sarki Raamud yasa hannu ya ɗauki Amrish zasu tafi da su can part ɗinsu...
Bayan Kwana biyu Ogah Junaid yana nan a cikin Damuwa na rashin matarsa uwar ƴaƴansa kullum sai mommy taje parts ɗinsa tayi masa girki daƙer take rarrashinsa akan yaci amma duk da hakan baifi yaci 2 spoon ba shikenam, gaba ɗaya ya lalace duk ya rame cikin kwana biyu, ba bacci ba cin abinci sosai kullum acikin damuwa, mommy har ta rasa yanda zatayi dashi,
A ranar ciwon zuciyan Amrish ya tashi a part ɗin mommy acikin tana motsawa har ta daina motsi kwata-kwata, numfashi ya ɗage cakk ga jinin dake fita a bakinta gaba ɗaya Mommy ba ƙaramin razana tayi ba, duk sun saddaƙar da cewa Amrish itama ta mutu, domin babu alamar da zai nuna cewa tana a raye, haka sauran ƴan uwan natan suka fara kuka, itakam Angel ihu take tana ambatan sunan Amrish, shi kuwa Areeph shima faɗuwa yayi ganin ƴar uwarsa ta mutu, duk ana cikin wannan halin Amrish ta mutu shima Areeph ya faɗi amma an kasa sanar wa Ogah Junaid dake can part ɗinsa saboda ana gudun tayar masa da hankali, yanzu ma ba'a cikin hayyacinsa yake ba,
Mommy ta kasa aiwatar da komai duk jiki ya mace sai kukan da take tayi, Sarki Raamud ne ya ɗauki wayarsa ya ƙira Uncle Artaff akan yazo, kafin nan kuwa acikin ma'aikatan gidan an samu wacce tayi gudu taje har part ɗin Ogah Junaid tana zuwa ta haura saman Upstairs taje tana bubbuga room ɗinsa,
Junaid yana kan sallayarsa yanda ya idar da Sallah yana kan addu'o'i kunnuwansa suke jiyo masa bugun ƙofa kamar daga sama, kafin ya buɗe baki yayi magana kwatsam yaji an turo ƙofar da ƙarfi wata mata ƴar dattijuwa ta shugo ta durƙusa a gabansa tana haki numfashi sama-sama yanda tasha guda,
Junaid kallonta yake hankali a tashe domin yasan ba lafiya ba, fuskarsa har yayi fiyau, idanuwansa kuma suna nan a dishe basu koma normal ba,
Haka ya jira saida matar da daidaita numfashinta sannan ta soma magana tana faɗin "Yallaɓai Amrisha ciwon zuciyarta ya tashi ta rasu, shima yaron Areeph ya faɗi suna can..."
Ogah Junaid idanuwansa ya zazzaro waje kamar zasu faɗo ƙasi, lokaci guda hawaye suka bayyano masa akan eyes ko ƙibtawa bayayi idonsa akan matar,
tana gama iddasa saƙonta ta tashi ta fice abunta, haka jikinsa yake kakkarwa ya miƙe a razane hajijiya yana ɗibarsa haka ya nufi hanyar fita,
Da gudu yake taka matakalar beni yana saƙƙowa ƙafarsa ta zame haka ya faɗo yana gangarowa daga kan Benin har zuwa ƙasi, nan danan goshinsa ya fashe sai jini, ƙafarsa ta gurɗe Allah ya temaka bai karya wuyansa ba, tsabar yasa yaran acikin ransa haka yayi ƙarfin halin tashi yana jan ƙafa daƙer ya fice daga falon, yana jin jiri amma haka yake daurewa, cikin sa'a ya samu driver part ɗinsa cikin hanzari ya shige mota Driver ya miƙe dashi part ɗin su mommy, yana zuwa ya tarar da mommy zaune ƙasan carpet tana rungume da Amrish sai kuka take tayi shi kuma Sarki Raamud ya ɗauki Areeph a saman kafaɗarsa, ganin Junaid a wani irin yanayi yasa gaban Sarki ya yanke tareda faɗin "subhanallahi Junaid meya sameka haka, dubi fuskarka duk ya wanke da Jini..."
Mommy najin haka ta ɗago dasauri tana kallonsa still yana tafe yana ɗingishi! a ruɗe Junaid yayo gurin mommy tareda durƙusawa yakai hannu ya ɗago da Amrish yana bubbugan fuskarta tareda ambatar sunanta "Mamana! Mamana!! Please wakeup Mamana don't leave your Dad please....". ya rungumeta tareda fashewa da matsanancin kuka, ya miƙe tsaye da ita ya ɗorata saman kafaɗarsa ya nufi gurin Sarki Raamud yaje ya karɓo Areeph wanda shima yana nan a sume ba motsi duk ya ɗaukesu su biyun ya fice waje, yana zuwa ya sakasu a mota shima ya shiga kai tsaye cikin masarautar suka ƙara shigewa suka nufi hospital ɗin Narasimha, daga baya su Mommy suma suka biyo bayansu da nasu motar gaba ɗaya sun mance da hospital ɗin Narasimha tsabar tashin hankali da suka tsinci kansu shiyasa tin da basu kai yaran nan ba...
Suna zuwa Narasimha ya farfaÉ—o da Areeph daman suma yayi, Amrish kuwa saida akayi aiki sosai akanta, domin saida akayiwa heart É—inta aiki sannan akayi nasarar ceton rayuwarta, shima Ogah Junaid anyi masa treat na ciwon da yaji sannan an haÉ—a masa da maganin rage damuwa dana saka bacci domin rabonsa dayin bacci yau kwana uku kenam bai rintsa ba,
Ogah Junaid da yaransa sai da sukayi sati guda a wajen Narasimha domin yaƙi barinsu su tafi har saida Amriish ta fara samun sauƙi, Idan suna tare da Daddynsu hankalinsu yafi kwanciya especially Amrish yanzu da take ganin Daddynta ta daina damuwa sosai, kullum sai mommy ta aiko musu da abinci, yanzu kuwa Ogah Junaid ya daina fita Aiki kwata-kwata tin lokacin da aka sanar masa rasuwar Ayushert ɗinsa,
Bayan an sallame su da wata guda Ogah Junaid yana kwance a saman gadonsa ga yaran suma suna kusa dashi a jere duk suna bacci, yanzu duk tare yake kwana dasu, su huÉ—u akan gado dashi kansa Junaid sai Areeph da Angel da Amrish,
Amriish ko kaɗan bata son motsawa ajikin Daddynta hakan yasa ta fara kwana a room ɗinsa itama Angel ganin haka yasa tace bazata iya kwana ita kaɗai a ɗakinsu ba itama ta fara kwana da Daddynta, shima Areeph ganin duk a ɗakin Daddynsu suke yasa shima ya dawo ɗakin, kullum kuwa sai mommy ta kawo musu ƙaninsu Jariri har ya fara wayo, dake madara mai kyau da tsada ake bashi, yaron ya samu sunan sarki Raamud inkiya kuma (KHUBAYR) wannan inkiyar Ayushert ce tin kafin ta haihu tabar wasiyya akan a sanya masa sunan...
Daga Nigeria sun samu labarin mutuwar Ayush kowa ba ƙaramin girgiza yayi ba dajin labarin, especially Doctor Hasheem yafi kowa shiga damuwa sosai, duk sun shirya akan zasu zo ƙasar california yin ta'aziyya,
Doctor Hasheem da matarsa Maimoon da yaransu biyu sai Lailah da mijinta Doctor Mansur da yarinyar ta mace, da Daddyn Maimoon da mamanta duk sun zo,
Mommy ba ƙaramin farin ciki tayi ba ganin yanda duk suka haɗa kayuwansu suka zo musu ta'aziyya,
Sunyiwa Ogah Junaid shima duk ya canza ya zamo kamar Maraya babu kuzari ajikinsa, saida suka ƙwana kafin suka dawo Nigeria...
Daga baya Hafzat itama da mijinta suka je, tinda hafzat take bata taɓa yin kukan da tasha a lokacinda aka sanar mata rasuwar Ayushert ba, har sukazo kuka takeyi gaba ɗaya ta fita hayyacinta, bata bar masarauta ba sai da tayi wata guda kafin saboda bataso tabar Triplets, ba ƙaramin tausayinsu tayi ba na rashin uwa tin suna yara....
★★★★★★
*AFTER 2 YEARS....*
Har zuwa wannan shekarar Ogah Junaid bai koma Aikin soja ba, a matsayinsa na General duk aikin da zaiyi saidai yayi daga gida, idan ana bukatar yasa hannu a takarda saidai a kawo masa gida yasa hannu duk wasu ayyukansa a gida yake yinsu, yanzu shine yake kula da yaransa, suma yaran sun ƙi school a duk lokacin da aka kaisu makaranta sai sun dawo da jinya a jikinsu tsabar ɗankwara har yanzu basu fitar da wannan damuwar na rashin mahaifiyarsu ba, akoda yaushe suna tsammanin dawowarta, ga khubayr ya girma ba tareda mahaifiyarsa ba yanzu yanada shekara biyu a duniya, yana samun kulawa sosai agurin ƴan uwansa, tsabar shaƙuwar da sukayi baya son yin nisa dasu don ko gurin mommy yanzu baya zuwa..
Mommy tace "babu komai ta ƙarisa maganar tareda goge hawayen fuskarta..."
Areeph yace "Mamy kina kuka kuma kina ce mana babu, shin meya samu Daddyn mu kuma ina Mommyn mu take?..."
Itama Angel tace "wannan Jaririn waye?..."
Mommy tace "Jaririn Mommynku ne ta haihu...". Angel ta kuma cewa "toh tana ina Mommyn namun?..."
Mommy ta kasa basu amsa kwatsam idonta ya sauƙa akan Amrish wacce take tsaye guri ɗaya sai fitar da numfashi take sama-sama, a tsorace mommy ta tashi ta nufi wajenta tareda faɗin "takwara meya faru ne? dan Allah ki temake mu kar ciwonki ya tashi please, ki kwantar da hankalinki kinji koh..."
Haka take rarrashin ta cikin kulawa domin ita daman Amrish batada cikakkiyar lafiya an haifeta da ciwon zuciya amma ba'a ankara ba sai bayan ta soma girma, zuwa yanzu dai sau biyu ciwon yake tashi, shiyasa akafi lallaɓata kuma tanada raunin zuciya bata juran damuwa, fargaban mommy a yanzu shine kar ciwon ya tashi a halinda take ciki yanzu...
Amrish ba abunda take faɗi illa "Mommy! Daddy!! Mommy!!! Daddy!!!!...". Ido yayi zuru-zuru. Mommy tasa hannu ta rungumeta tana rarrashinta ta ɗayan ɓangaren kuma tana riƙe da Jariri,
Can saiga su Uncle Artaff sun sauƙo yace "Suma yayi amma yanzu ya farfaɗo yana buƙatar hutu domin jikinsa yahau temporary...". Sarki Raamud yasa hannu ya ɗauki Amrish zasu tafi da su can part ɗinsu...
Bayan Kwana biyu Ogah Junaid yana nan a cikin Damuwa na rashin matarsa uwar ƴaƴansa kullum sai mommy taje parts ɗinsa tayi masa girki daƙer take rarrashinsa akan yaci amma duk da hakan baifi yaci 2 spoon ba shikenam, gaba ɗaya ya lalace duk ya rame cikin kwana biyu, ba bacci ba cin abinci sosai kullum acikin damuwa, mommy har ta rasa yanda zatayi dashi,
A ranar ciwon zuciyan Amrish ya tashi a part ɗin mommy acikin tana motsawa har ta daina motsi kwata-kwata, numfashi ya ɗage cakk ga jinin dake fita a bakinta gaba ɗaya Mommy ba ƙaramin razana tayi ba, duk sun saddaƙar da cewa Amrish itama ta mutu, domin babu alamar da zai nuna cewa tana a raye, haka sauran ƴan uwan natan suka fara kuka, itakam Angel ihu take tana ambatan sunan Amrish, shi kuwa Areeph shima faɗuwa yayi ganin ƴar uwarsa ta mutu, duk ana cikin wannan halin Amrish ta mutu shima Areeph ya faɗi amma an kasa sanar wa Ogah Junaid dake can part ɗinsa saboda ana gudun tayar masa da hankali, yanzu ma ba'a cikin hayyacinsa yake ba,
Mommy ta kasa aiwatar da komai duk jiki ya mace sai kukan da take tayi, Sarki Raamud ne ya ɗauki wayarsa ya ƙira Uncle Artaff akan yazo, kafin nan kuwa acikin ma'aikatan gidan an samu wacce tayi gudu taje har part ɗin Ogah Junaid tana zuwa ta haura saman Upstairs taje tana bubbuga room ɗinsa,
Junaid yana kan sallayarsa yanda ya idar da Sallah yana kan addu'o'i kunnuwansa suke jiyo masa bugun ƙofa kamar daga sama, kafin ya buɗe baki yayi magana kwatsam yaji an turo ƙofar da ƙarfi wata mata ƴar dattijuwa ta shugo ta durƙusa a gabansa tana haki numfashi sama-sama yanda tasha guda,
Junaid kallonta yake hankali a tashe domin yasan ba lafiya ba, fuskarsa har yayi fiyau, idanuwansa kuma suna nan a dishe basu koma normal ba,
Haka ya jira saida matar da daidaita numfashinta sannan ta soma magana tana faɗin "Yallaɓai Amrisha ciwon zuciyarta ya tashi ta rasu, shima yaron Areeph ya faɗi suna can..."
Ogah Junaid idanuwansa ya zazzaro waje kamar zasu faɗo ƙasi, lokaci guda hawaye suka bayyano masa akan eyes ko ƙibtawa bayayi idonsa akan matar,
tana gama iddasa saƙonta ta tashi ta fice abunta, haka jikinsa yake kakkarwa ya miƙe a razane hajijiya yana ɗibarsa haka ya nufi hanyar fita,
Da gudu yake taka matakalar beni yana saƙƙowa ƙafarsa ta zame haka ya faɗo yana gangarowa daga kan Benin har zuwa ƙasi, nan danan goshinsa ya fashe sai jini, ƙafarsa ta gurɗe Allah ya temaka bai karya wuyansa ba, tsabar yasa yaran acikin ransa haka yayi ƙarfin halin tashi yana jan ƙafa daƙer ya fice daga falon, yana jin jiri amma haka yake daurewa, cikin sa'a ya samu driver part ɗinsa cikin hanzari ya shige mota Driver ya miƙe dashi part ɗin su mommy, yana zuwa ya tarar da mommy zaune ƙasan carpet tana rungume da Amrish sai kuka take tayi shi kuma Sarki Raamud ya ɗauki Areeph a saman kafaɗarsa, ganin Junaid a wani irin yanayi yasa gaban Sarki ya yanke tareda faɗin "subhanallahi Junaid meya sameka haka, dubi fuskarka duk ya wanke da Jini..."
Mommy najin haka ta ɗago dasauri tana kallonsa still yana tafe yana ɗingishi! a ruɗe Junaid yayo gurin mommy tareda durƙusawa yakai hannu ya ɗago da Amrish yana bubbugan fuskarta tareda ambatar sunanta "Mamana! Mamana!! Please wakeup Mamana don't leave your Dad please....". ya rungumeta tareda fashewa da matsanancin kuka, ya miƙe tsaye da ita ya ɗorata saman kafaɗarsa ya nufi gurin Sarki Raamud yaje ya karɓo Areeph wanda shima yana nan a sume ba motsi duk ya ɗaukesu su biyun ya fice waje, yana zuwa ya sakasu a mota shima ya shiga kai tsaye cikin masarautar suka ƙara shigewa suka nufi hospital ɗin Narasimha, daga baya su Mommy suma suka biyo bayansu da nasu motar gaba ɗaya sun mance da hospital ɗin Narasimha tsabar tashin hankali da suka tsinci kansu shiyasa tin da basu kai yaran nan ba...
Suna zuwa Narasimha ya farfaÉ—o da Areeph daman suma yayi, Amrish kuwa saida akayi aiki sosai akanta, domin saida akayiwa heart É—inta aiki sannan akayi nasarar ceton rayuwarta, shima Ogah Junaid anyi masa treat na ciwon da yaji sannan an haÉ—a masa da maganin rage damuwa dana saka bacci domin rabonsa dayin bacci yau kwana uku kenam bai rintsa ba,
Ogah Junaid da yaransa sai da sukayi sati guda a wajen Narasimha domin yaƙi barinsu su tafi har saida Amriish ta fara samun sauƙi, Idan suna tare da Daddynsu hankalinsu yafi kwanciya especially Amrish yanzu da take ganin Daddynta ta daina damuwa sosai, kullum sai mommy ta aiko musu da abinci, yanzu kuwa Ogah Junaid ya daina fita Aiki kwata-kwata tin lokacin da aka sanar masa rasuwar Ayushert ɗinsa,
Bayan an sallame su da wata guda Ogah Junaid yana kwance a saman gadonsa ga yaran suma suna kusa dashi a jere duk suna bacci, yanzu duk tare yake kwana dasu, su huÉ—u akan gado dashi kansa Junaid sai Areeph da Angel da Amrish,
Amriish ko kaɗan bata son motsawa ajikin Daddynta hakan yasa ta fara kwana a room ɗinsa itama Angel ganin haka yasa tace bazata iya kwana ita kaɗai a ɗakinsu ba itama ta fara kwana da Daddynta, shima Areeph ganin duk a ɗakin Daddynsu suke yasa shima ya dawo ɗakin, kullum kuwa sai mommy ta kawo musu ƙaninsu Jariri har ya fara wayo, dake madara mai kyau da tsada ake bashi, yaron ya samu sunan sarki Raamud inkiya kuma (KHUBAYR) wannan inkiyar Ayushert ce tin kafin ta haihu tabar wasiyya akan a sanya masa sunan...
Daga Nigeria sun samu labarin mutuwar Ayush kowa ba ƙaramin girgiza yayi ba dajin labarin, especially Doctor Hasheem yafi kowa shiga damuwa sosai, duk sun shirya akan zasu zo ƙasar california yin ta'aziyya,
Doctor Hasheem da matarsa Maimoon da yaransu biyu sai Lailah da mijinta Doctor Mansur da yarinyar ta mace, da Daddyn Maimoon da mamanta duk sun zo,
Mommy ba ƙaramin farin ciki tayi ba ganin yanda duk suka haɗa kayuwansu suka zo musu ta'aziyya,
Sunyiwa Ogah Junaid shima duk ya canza ya zamo kamar Maraya babu kuzari ajikinsa, saida suka ƙwana kafin suka dawo Nigeria...
Daga baya Hafzat itama da mijinta suka je, tinda hafzat take bata taɓa yin kukan da tasha a lokacinda aka sanar mata rasuwar Ayushert ba, har sukazo kuka takeyi gaba ɗaya ta fita hayyacinta, bata bar masarauta ba sai da tayi wata guda kafin saboda bataso tabar Triplets, ba ƙaramin tausayinsu tayi ba na rashin uwa tin suna yara....
★★★★★★
*AFTER 2 YEARS....*
Har zuwa wannan shekarar Ogah Junaid bai koma Aikin soja ba, a matsayinsa na General duk aikin da zaiyi saidai yayi daga gida, idan ana bukatar yasa hannu a takarda saidai a kawo masa gida yasa hannu duk wasu ayyukansa a gida yake yinsu, yanzu shine yake kula da yaransa, suma yaran sun ƙi school a duk lokacin da aka kaisu makaranta sai sun dawo da jinya a jikinsu tsabar ɗankwara har yanzu basu fitar da wannan damuwar na rashin mahaifiyarsu ba, akoda yaushe suna tsammanin dawowarta, ga khubayr ya girma ba tareda mahaifiyarsa ba yanzu yanada shekara biyu a duniya, yana samun kulawa sosai agurin ƴan uwansa, tsabar shaƙuwar da sukayi baya son yin nisa dasu don ko gurin mommy yanzu baya zuwa..