Sashe 79
Matar Damisa Part 2 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Akwana a tashi Uncle Artaff shima yana shirin barin Nigeria, zai koma can masarautar california da iyalansa, sunyi bankwana da kowa, anan ma Ayush ba ƙaramin shiga damuwa tayi ba ganin yanda kowa yaketa tafiya,
Bayan tafiyar Uncle Artaff da wata guda shima Junaid ya tada nashi tafiyan zai koma california shima tareda su Ayushert, a hutun da aka bashi ma har ya ƙara kwanaki, Ayush ba ƙaramin farin ciki tayi ba jin wannan Albishir daga bakin mijinta, ga murnar zata je ta tarar da mommy tayi missing ɗinta sosai, amma abun mamaki duk yaran babu mai son tafiyar, saboda basa so subar school ɗinsu, ga waɗanda suka shaƙu sosai especially matan sunfi ƙawaye amma shi Areeph daman bashida wanda zaiyi missing ɗinsa sai iya Rapeekh domin shine kawai abokinsa, shima Rapeekh bason tafiyar Areeph yake yi ba, harda kukansa cewar Areeph zai bar Nigeria, sunyi shirinsu tsab, akan washe gari da sassafe zasu tafi airport domin har sun yanki Viza,
Washe gari sun fito zasu shiga motar da zai kaisu airport kwatsam wani irin murɗa ya damƙi cikin Ayushert, bata san lokacin data fara jero addu'o'i ba, nan danan zazzaɓi mai zafin gaske ya rufe ta, ga hajijiya haka ta tafi luu zata faɗi Ogah Junaid yayi saurin tarota tareda faɗin "lafiya kuwa? meyake faruwa dake?..." kafin ta bashi amsa dasauri ta zame daga jikinsa ta nufi wajen fanfo anan ta tsuguna tana kwarara amai ba ƙaƙƙautawa, zuwa gabanta yayi ya tsaya yana kallonta yace "kodai mu fasa tafiyar nan yau naga bakida lafiya koh?..."
girgiza kai tayi tace "ba komai zamu iya tafiya..." matsowa dab da ita yayi ya soma taɓa jikinta ji yayi kamar garwashi tsabar zafin da jikinta ya ɗau, lokaci guda ta fita hayyacinta ido sunyi zuru-zuru, shima girgiza kai yayi yace "gaskiya mu haƙura da tafiyar nan, idan kin samu sauƙi inyaso sai mu tafi koh?...". Nan danan saiga hawaye kwance a fuskarta ita sam bataso a haƙura da tafiyar tasa ranta sosai a tafiyar, tace "ina zumuɗi naje naga mommy dan Allah My kar kace bazamu tafi ba a yau, wallahi bana jin ciwon jikina..."
yace "shikenam toh tinda kince haka, saiki wanke bakinki kizo mu tafi kar jirgin mu ya tashi .." a hanzarce ta wanke bakinta suka koma wajen mota, yaran kuma suna ciki sai wasan su suke ta sha yayin da shi kuma Areeph yake riƙe da wayarsa sai game yaketa yi,
Ogah Junaid ko kaɗan bai kawo komai a ransa ba na dalilin aman Ayush, ya ɗauka cewa rashin lafiya ne na halin rayuwa yau da kullum, baiyi tunanin akwai ciki a jikinta ba saboda a yanda ta sanar masa shine tace "bata son haihuwa yanzu saita huta, kuma wai taje tayi Allurar planning na tsawon shekara huɗu..." Kuma tayi lissafi ne da cewar a yanzu yaranta sunada shekara huɗu a duniya idan ta ƙara shekara huɗu kuma sunada shekara takwas alokacin ne zatayi ƙoƙarin yi musu ƙani ko ƙanwa, saidai kuma data je yin Allurar planning sai akayi mistake maimakon ayi na yanda takeso 4 years sai akayi rashin sa'a sukayi mata na Three months kuma tin kafin Ogah Junaid ya dawo taje akayi mata, saidai kuma shi ba'a son ransa tayi planning ba, kawai ya ƙyaleta ne a haka....
A yanzu ko ita kanta bata san tanada cikin ba, saboda yana yin planning saida ya ɗauke mata jini kwatata daga baya ta dawo tana gani, kumadu ya ƙara ɗage mata haka yake mata shiyasa bazata san tanada pregnant ba, gashi har na tsawon wata biyu.....
Haka suka shige mota sai airport anan suka shiga jirginsu,
Haka su Areeph da Angel da Amrish suka rinƙa tsalle suna murna cewar yau zasu shiga jirgi wai basu taɓa shiga ba,
Ogah Junaid sam baiji daɗin hakan ba, yaso ace yanda suke da kuɗin nan ace yaransa sun saba shiga jirgi, gashi yanzu yanda suketa tsalle kamar wasu baƙauyawa, son samu ace duk ƙarshen wata ana fita dasu yawon buɗe ido ƙasashe daban daban, amma laifin kansa yake gani da baiyi ƙoƙarin yin haka ba, ko ita Ayush ya kamata ace ta saba shiga jirgi amma itama yanzu ne karo na farko....
Bayan tafiyar Uncle Artaff da wata guda shima Junaid ya tada nashi tafiyan zai koma california shima tareda su Ayushert, a hutun da aka bashi ma har ya ƙara kwanaki, Ayush ba ƙaramin farin ciki tayi ba jin wannan Albishir daga bakin mijinta, ga murnar zata je ta tarar da mommy tayi missing ɗinta sosai, amma abun mamaki duk yaran babu mai son tafiyar, saboda basa so subar school ɗinsu, ga waɗanda suka shaƙu sosai especially matan sunfi ƙawaye amma shi Areeph daman bashida wanda zaiyi missing ɗinsa sai iya Rapeekh domin shine kawai abokinsa, shima Rapeekh bason tafiyar Areeph yake yi ba, harda kukansa cewar Areeph zai bar Nigeria, sunyi shirinsu tsab, akan washe gari da sassafe zasu tafi airport domin har sun yanki Viza,
Washe gari sun fito zasu shiga motar da zai kaisu airport kwatsam wani irin murɗa ya damƙi cikin Ayushert, bata san lokacin data fara jero addu'o'i ba, nan danan zazzaɓi mai zafin gaske ya rufe ta, ga hajijiya haka ta tafi luu zata faɗi Ogah Junaid yayi saurin tarota tareda faɗin "lafiya kuwa? meyake faruwa dake?..." kafin ta bashi amsa dasauri ta zame daga jikinsa ta nufi wajen fanfo anan ta tsuguna tana kwarara amai ba ƙaƙƙautawa, zuwa gabanta yayi ya tsaya yana kallonta yace "kodai mu fasa tafiyar nan yau naga bakida lafiya koh?..."
girgiza kai tayi tace "ba komai zamu iya tafiya..." matsowa dab da ita yayi ya soma taɓa jikinta ji yayi kamar garwashi tsabar zafin da jikinta ya ɗau, lokaci guda ta fita hayyacinta ido sunyi zuru-zuru, shima girgiza kai yayi yace "gaskiya mu haƙura da tafiyar nan, idan kin samu sauƙi inyaso sai mu tafi koh?...". Nan danan saiga hawaye kwance a fuskarta ita sam bataso a haƙura da tafiyar tasa ranta sosai a tafiyar, tace "ina zumuɗi naje naga mommy dan Allah My kar kace bazamu tafi ba a yau, wallahi bana jin ciwon jikina..."
yace "shikenam toh tinda kince haka, saiki wanke bakinki kizo mu tafi kar jirgin mu ya tashi .." a hanzarce ta wanke bakinta suka koma wajen mota, yaran kuma suna ciki sai wasan su suke ta sha yayin da shi kuma Areeph yake riƙe da wayarsa sai game yaketa yi,
Ogah Junaid ko kaɗan bai kawo komai a ransa ba na dalilin aman Ayush, ya ɗauka cewa rashin lafiya ne na halin rayuwa yau da kullum, baiyi tunanin akwai ciki a jikinta ba saboda a yanda ta sanar masa shine tace "bata son haihuwa yanzu saita huta, kuma wai taje tayi Allurar planning na tsawon shekara huɗu..." Kuma tayi lissafi ne da cewar a yanzu yaranta sunada shekara huɗu a duniya idan ta ƙara shekara huɗu kuma sunada shekara takwas alokacin ne zatayi ƙoƙarin yi musu ƙani ko ƙanwa, saidai kuma data je yin Allurar planning sai akayi mistake maimakon ayi na yanda takeso 4 years sai akayi rashin sa'a sukayi mata na Three months kuma tin kafin Ogah Junaid ya dawo taje akayi mata, saidai kuma shi ba'a son ransa tayi planning ba, kawai ya ƙyaleta ne a haka....
A yanzu ko ita kanta bata san tanada cikin ba, saboda yana yin planning saida ya ɗauke mata jini kwatata daga baya ta dawo tana gani, kumadu ya ƙara ɗage mata haka yake mata shiyasa bazata san tanada pregnant ba, gashi har na tsawon wata biyu.....
Haka suka shige mota sai airport anan suka shiga jirginsu,
Haka su Areeph da Angel da Amrish suka rinƙa tsalle suna murna cewar yau zasu shiga jirgi wai basu taɓa shiga ba,
Ogah Junaid sam baiji daɗin hakan ba, yaso ace yanda suke da kuɗin nan ace yaransa sun saba shiga jirgi, gashi yanzu yanda suketa tsalle kamar wasu baƙauyawa, son samu ace duk ƙarshen wata ana fita dasu yawon buɗe ido ƙasashe daban daban, amma laifin kansa yake gani da baiyi ƙoƙarin yin haka ba, ko ita Ayush ya kamata ace ta saba shiga jirgi amma itama yanzu ne karo na farko....