← Book details Katanga Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 45 OF 69

Sashe 45

Katanga Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hibba ce take b'allo mata magun gunanta na ulcer tana bata ta sha, don kwana biyu ulcer ince ta takura mata sosai, a had'e ta bata su gaba daya ta korasu da ruwa ba tare da ta duba ko guda nawa bane don da ta lura za taga da karin guda daya wanda Hidayace ta jefa mata shi a ciki don ta sha su samu plane insu ya tafi dai dai, sun samu Daddy yayi tafiya, sai da Hibba ta bar d'akin sannan Momy ta shigo.
" Ki had'a komai naki driver yana jiranki zai mayar da ke gida."
Shine abinda tace mata ta juya ta bar d'akin, jiki a sanyaye take had'a dukkan wani abu da ta san nata ne cikin wata k'atuwar akwati da Rj ya bata, tana hadawa kirjinta na dukan tara tara, ko da ta gama had'a kayan nata sai ta nemi wayoyinta babba da karamar ta rasa, har Momy ta dawo tana neman wayar.
"Naga dai ba da ita kika zo cikin gidan nan ba, don haka kizo ki shige driver yana jira."

Ba tace komai ba ta janyo akwatinta ta shige, amman ta so ko da sim inta ne ta cire don shi take yiwa tunda dama da abinta tazo ba anan ta same shi ba.

Idanuwanta ta lumshe bayan dai daituwarta cikin motar driver ya ja suka fara tafiya, kafin wasu zafafan hawaye su biyo kuncinta har lokacin kirjinta yana wani irin bugu don ba ta san me suka shirya mata ba .....

Last free page
09037093702
[4/26, 8:46 PM] Rabi: 31

Sun kusan cin rabin tafiya taji mararta tayi wani irin k'ullewa had'e da murd'a mata, rintse idanuwanta tayi tana jin yadda marar tata ke murd'awa da alamu dai period inta ne ke hanya duk da tayi mamakin zuwansa a wannan lokaci don lokacinta bai k'arasa ba ba tafi sati biyu da gama wancan ba sai dai kawai tayi la'akari da wani zubin yakan canja lokacin zuwansa, fatanta dai har su isa gida bai zo ba gudun kar ta b'aci saboda ba shirin zuwansa tayi ba, sai dai fatanta nata bai ciyu ba suna karya kwanar layinsu taji yayi wani ambaliya ya fito saboda sama da kasa da motar tayi saboda jakin baban gida da suka tsallaka, innalillahi take ambata a cikin ranta tana adduar Allah yasa ba ta bata motar ba don in ta jikinta ne da sauk'i saboda dogon hijabine har k'asa a jikinta kuma copee ne kalar baza ta fito ba sai dai danshi, kuma ba matsala tunda har k'ofar gida za ta sauka.

Ko da yayi parking a k'ofar gidan nasu ji tayi tana jin nauyin mik'ewa don yanzu ta riga ta tabbatar tayi rushing sosai, inda Allah ya taimaketa sai ya fita daga cikin motar don fito mata da akwatinta da ke cikin boot, idonta ne ya sauka akan dostar motar tayi saurin janyota kafin ta zira k'afafuwanta waje a hankula ra fita daga cikin motar kana ta d'an durk'uso tana goge gurin da dostar, kana ta saka ruwa ta kuma gogewa sai ta rik'e dostar a hannunta don ba za ta iya ajiye mishi ita a haka ba kuma ba za ta iya wullar da jininta ba har sai ta wanke.

Daga nan suka yi sallama da driver ya juya saboda babu yunwa a tattare da shi ko kishirwa duk da abinsa ya taho saboda Momy tace yana ajiyeta ya juyo ko gidan ba ta yadda ya shiga ba.
Jan akwatinta tayi ta nufi cikin gidan nasu da duk wani taku da za tayi da bugawar kirjinta yake tafiya wanda ba tasan dalilin hakan ba, da sallama a bakinta ta shiga inda ta tarar da IYa da Baffa Shamsu da Umma a tsaye a babban tsakar gidan sun zubo mata idanuwa wanda hakan yasa zuciyarta wani irin harbawa, kafin sautin maganar Baffa Shamsu ya sauka cikin kwanyarta.

"Me kika zo yi mana? tunda abinda kika zab'awa rayuwarki kenan ai sai kiyi gaba don baza kizo ki bata mana sunan gida ba."
Yayin da Iya tace.
"Banda abinka zuwa tayi ta shafa mana bak'in fentin da ta shafowa kanta, don sunan zuriarmu ya b'aci, inama Malam zai dawo yazo yaga wacce yake kira 'yar baiwa yau ga baiwarnan mun gani a k'asa, baiwar karuwanci ba."

Saurin rintse ido Nusrat tayi tana jin saukar kalmarta ta k'arshe tare da sarawar b'arin kanta, kafin Umma tace.

"To ai dama ai ba abanza taki yin aure ba, dama jira take ta samu guri ta fito da zallar ainihin abinda take aikatawa, gashinan kuwa mun gani anyi walk'iya ta haska mana, ku kalli k'afarta ga jini nan yana d'igowa da alama cikinne ya fara fita."

Wani ululun bakin ciki ne ya kama Baffa Shamsu, yana jin takaici da tsanar abinda Nusrat in ta aikata, banda daga bakin Aunty Maryam yaji to tabbas bazai yarda ba a yadda yasan tsananin tarbiya a gurin Nusrat in da kamun kai, yayin da Iya kuma ke ta rafka salati tana bin jinin da ke diga a kasa da kallo.

"Tun kan hannuna ya sauka a jikinki ki kama hanya ki bar gidan nan, duk randa zuciyarki ta tsarkaka zaki iya dawowa amma da sharadin sai na aurar da yata don bazanyi saken da zata kasa auruwa kamar ki ba, wannan shine hukuncin kawai da zan iya yi miki."
Cewar Baffa Shamsu

Wasu zafafan hawaye ne suka ziraro ta kuncinta tana jin yadda zuciya da ruhinta ke wani irin radadi, radadi mai zafi me huyar fassarawa, karuwanci shine abinda ke yawo cikin kanta kuma ta kasa bashi maauni wanda zai auna ya bata me kalmar ke nufi.

"Nifa ban fahimci me kuke magana akai ba, bansan me na aikata ba kumin bayani don Allah yadda zan fahimta."

"Mu zaki mayar 'yan iska kidahumai, to anki a miki bayanin, ki bace mini da gani na daina ganin bakar fuskar nan taki me kama da ta 'yan ruwa."
Cewar IYa
Ido ta k'urawa Iyan kamar a fuskarta za ta karanci amsoshin da take son ji yayin da Iyan ta fara rarumar wani ice da ke gefenta had'e da cewa.
"Zaki fice daga cikin gidannan ko sai na karya kasusuwanki, don naga alamun don baa taba fatar jikinki ba ne kika tsaya kina mana taurin kai."

"Zan fita, amman don Allah ki barni na fara gyara jikina."

"Alqur'an kinyi kad'an, cikin gidan malaman zan bari a wanke jinin shege, sakamakon da za kiyiwa soyayyar da Mallam da Audu suka nuna miki kenan, to ba da Zainabu ba wallahi."

"Ki barta ta fara gyara jikin nata mana."
Cewar Baffa Shanmsu.

"Alqur'an baza ta wanke mana d'an shege ba a gidan nan, idan ta k'ara can gaba koma dandalin karuwanne ta wanke."

Meye laifinta ne, me ta aikata musu suka tsaneta?Idan dan son da Rj yake mata ne itace tace ya sota, ko kwa ita ta dauki sonta ta d'ora masa, yanzu wannan laifin har ya kai su tsaneta ya kuma kai matakin da zasu yiwa rayuwarta wannan qullin, qullin da Allah ne kad'ai zai iya fidda ita?

Tafiya take tana jan akwatunta zuciyarta bak'ikirin, duk wani bayani tayi musu na cewar ba ta san maganar da suke ba sunk'i fahimta kuma ba ta san da wani yare za tayi musu bayanin da zasu fahimta ba, ba ta da wani zab'i da ya wuce na ficewa daga gidan don Iya ta tsaya kai da fata ko gyara jikin nata ba za ta bari ta shiga tayi ba.

Tafiya take ba ta san inda zata dosa ba, ba ta da kowa su d'innan dai sune nata, kuma ga abinda suka yi mata, duk maraici shine ginshik'in da ya kawo rayuwarta a haka ta tabbata da yanzu tana jikin Mamanta wacce ta katangesu daga dukkanin wasu matsaloli, amman gashi k'addara ta kawota bigiren da gidan mahaifinta ma ya gagare ta zama bayan k'azamar kalmar da suke kiranta da shi.

Idan tace gidan Auncle Iliya za taje, wani nauyin za taje ta kuma d'ora musu, idan kuma tace cikin gidane to tabbas babu wanda zai iya rikonta a ciki sai dai wuk'a da ta d'auko ta kuma dabawa cikinta, don zasu tambayi dalilin korarta idan ya fasu kuwa sunanta ya riga ya gama b'aci wanda babu me wanketa sai Allahn da ya halicceta, don haka kawai ta mik'i titi tana tafiya ba tare da tasan inda take jefa k'afafuwanta ba, da kuma inda ta dosa ba, ina kuma rayuwa za ta d'auketa ta kaita?
[4/26, 8:46 PM] Rabi: 32
A gajiye ya shigo cikin gidan lik'is, tun safe da ya fita sai yanzu da ake magana da sallar isha ya samu kansa sakamakon wani aiki da ya tattare masa guri aya, bashi da wata bukatada ya huce na yin wanka tare da sauke sallar ishar da ta rage masa ya nemi makwanci kuma don wuce gajiyar gaba d'aya, amman kuma sam zuciya da idaniyansa sun kasa hak'uri Nusrat kawai suke da burin fara gani, tun bayan fitarsa da sukayi waya ba su sake yi ba saboda bai samu kansa gaba daya ba a wunin yau din.

Kansa tsaye cikin gidan ya nufa yana fatan ya sameta a falo ko daga nesa ne ya kalleta zuciyarsa ta samu nutsuwa ya juyo ba tare da magana ta shiga tsakaninsu ba, sai dai kuma Hibba kawai ya tadda a falon tana mutumin nata, sannu da zuwa tayi masa da ka ya amsa mata kafin yace tayi masa magana da Nusrat sai cewa tayi.

"Wallahi Yaa tun dawowata daga islamiya nake mata nocking don na kuma duba jikin nata amman shiru ba ta bud'e ba, to nayi tunanin ko bacci take shine na rabu da ita, to yanzu zamana kenan na gama nocking in shiru, naiwa Aunty Hidaya don naji ko lafiya sai tace mini tana toilet Momy kuma da naje sallah take, shine nake jiran idarwarta naji ko lafiya"
Chapter 45 · 0% Book details