← Book details Katanga Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 2 OF 69

Sashe 2

Katanga Complete Hausa Novel · about 7 min read

300 za ku biya domin samunsa cikin sauk'i.
0567838462
NABABA FADILA SHU'AIB GTBANK
in kuma katin waya ne ki turo ta wannan layin, shaidarki ta biya ma ki turo cikinta.
09037093702
In katin wayane 400 zaku biya.

Garab'asa gareku masoyana, duk wacce ta sayi wannan littafin za ta sami wanda zan rubuta gaba kyauta, ban yadda ki sayi littafina ki dinga turawa gruop ba, in hakan za kiyi ki sameni a layina muyi magana.

Allah ka k'arawa mahaifanmu lafiya da nisan kwana.

#Team KTG
#N.W.A
[10/8, 3:42 PM] Binta Lawan: *BEBE'ARTH*

Wattpad@Rashuna

*KATANGA*

____________
*TWO*
Yau ta kama lahadi, duk da suna cikin hutun makarantar boko, su Nusrat duk sun tsefe kawunansu zasu kitso, sai da Nusrat ta fara wanka ta yiwa Yusra ma ta wanke mata kanta ta taje ta shafe mata shi da mai sannan suka shirya zasu tafi, kallon Shukhura Mama ta yi da ta saka hijabi zasu tafi tace.
"Ke yanzu ba za ki wankan ba haka za ki bisu?“
Sai da ta fara turo baki gaba kana tace.
"To Mama nan da nan d'in sai na yi wanka, abinda yanzun nan za'a mana mu dawo. “
"Allah ya shirya. “
Mama kawai tace ta na mik'awa Nusrat kud'in kitson nasu had'e da fad'in.
"Ta fara yi miki kitson, kuma tai miki manya don kinsan yadda yawan kanki yake, kuma ke zan barwa girkin dare don fita zan yi, saura kuma kice a fara yiwa Yusra don na san hali. “
Murmushi Nusrat ta yi, bayan ta saka hannu biyu ta anshi kud'in kana tace.
"Mun tafi.“
Maman tace.
"Allah ya tsare, ku dai yi addu'a kafin ku fita. “Tace.
"Amin, tom insha Allah.“ Tare da jan hannun Yusra suka bi bayan Shukhura da ta fita tun d'azu.

Har sun d'an gota gurin Iya ta hango giftawarsu da sauri ta k'walowa Nusrat kira.
"Ke ke A'i zo nan. “
Da yake haka take kiranta tun ma Malam na raye, juyowa Nusrat ta yi, Yusra ta turo baki gaba tace.
"Wallahi na san aiki za ta sakaki, kawai kizo mui tafiyarmu mu rabu da ita.“
Murmushi Nusrat ta yi tace.
"Bara dai naje na ji kiran da take mini.“
"Tak'i ta rabu da ni d'in, shegiya ifrituwa me zunb'utun baki. “
Suka jiyo muryar Iya daga ciki, kuma turo baki Yusra ta yi ta na hararar gurin kafin ta fice waje da sauri, Nusrat kuma ta nufi gurin Iyan ta na murmushi.
Gyaran d'aki tace tai mata da wankin band'aki sai 'yan tsunmokaranta ma da tace ta wanke mata.

Kallon Shukhura Nana me kitso ta yi tace.
"Ina su Yayar taku?“
"Ga sunan suna hanya. “
"To shiga ciki, gani nan bari na k'arasa sharar nan. “
Rufe bakinta kenan Yusra ta yi sallama, kallon ta Shukhura ta yi bayan ta amsa sallamar ta ta tace.
"Ina Yayarmun?“
"Ba Iya ce ta kirata ba, har ta na ce mini ifrituwa. “
Wani haushi ne ya kama Shukhura, ta zura takalminta ta fasa shiga d'akin ta fice a fusace Yusra ta biyo bayanta.

Kamar an jefota ta shigo ta na kallon Nusrat da ke zubar da shara.
"Sannu"
Tace mata, kafin ta shige zuwa gurin Iya, iya na ganinta ta d'aure b'arin goron da ta b'antara a gefen zaninta kana tace.
"To rasa kunya b'eran tanka, kinzo kimin rashin kunyar taki ne? “
Kar katar da kai Shukhura ta yi tace.
"Ashe 'Yar aljanu na da rana tun da har an iya sakata aiki, me yasa ba ki kirawo 'yar lelen taki tai miki ba sai ita za ki saka, amma in abu zaki bayar babu wanda ke gabanki sai Nimha, amman in aikine sai wacce kika raina, don kin san Nimha ko tsintsiya ba za ta iya d'aga miki ba.
Bayan kuma kitso zamu je kina gani kuma Mamanmu na zaman jiranmu“

"Tunda dai ba ke na saka ba, ki shige ki bani guri, kiyi can da rashin kunyarki. “
Cewar Iya
"Waa aini kin san abinda bazai tab'a yuyuwa bane, don wallahi bazan bautawa wanda bai san ina yi ba, in cin mutumci ne ya taso azo a tarkace mini, lalalala wallahi, itama ita taga za ta iya.“
"Ni kikewa cin mutumci Safiya, Allah ya dawo da Audu, wallahi za ki gane Ubanki na haifa. “
"Amin, ya dawo d'in ki gaya masa, wallahi duka d'aya yamin kinsan sai na bi ta inda zan rama, Allah ya baki sa'a. “
"Wai da sa'ar ki kikeyi ne Shukhura?“
Cewar Nusrat ta na kallonta, ba ta bata amsa ba ta fice ta na zunb'uro baki, Iya kuwa k'ifi² ta yi da ido tunowa da ta yi sanda ta saka Nusrat a gaba ta na zaginta Shukhura ta amshe ta hayayyak'o kamar za ta daketa har sai da Mama ta fito ta kikkifawa Shukhura mari, shine Baba ya na dawowa Iya ta kwashe ta gaya masa, aikwa ranar Shukhura ta sha duka gurin Baba, ita kuwa ta d'auki aniyar wallahi sai ta rama akan Iya, sai da ta bari duhu ya yi ta kad'a karkashinsu me yauk'i taje ta zuba a band'akin Iya,don ta na da tabbacin yanzu za ta fito ta shiga band'akin ta lab'e a bayan k'ofa, Iya na shiga ta yi sufa ta fad'i Shukhura ta fito ta na ta k'yak'yata mata dariya, tace mata kad'an ta gani muddun ta na sakawa Baba na dukanta, Iya kuwa jiki yai tsami da k'yar ta iya mik'ewa.

"Yanzu Mama kina kallo ga Iya can ta saka Nusrat aiki.“
Shukhura ta fad'a ta na turo baki gaba. “
"To meye, don ta sakata aiki?“
Mama ta fad'a ta na cigaba da tankad'en da take.
"Amma Mama kefa kikace a fara mata kitson saboda za ki bar mata girki.“
"Yanzu kuma na fasa ba, kije ke a fara miki sai ki baro Yusran a can in Yayar taku tazo sa taho tare sai ki karb'i girkin na samu na fita. “
"Amma Mama....“
Dakatar da ita Mama ta yi had'e da fad'in.
"Ban san jin komai ki shige kije kiyi abinda na saki. “
Fita ta yi ta na tutturo baki Mama ta girgiza kai had'e da fad'in.
"Allah ya shirya. “

Sai da Iya ta kinta tanci dawowar Baba ta fito babban tsakar gida ta k'wama kujera ta na jiran dawowarsa, aikwa ta na jin sallamarsa ta saki kuka me k'arfi, a gigice ya nufota ya na tambayarta.
"Lafiya Iya, me ya faru kike kuka haka?"
Face hanci Iya ta yi tace.
"Wai ni yau A'i za ta kalli tsabar idona ta zageni ta uwa ta uba. “
" 'Yar baiwa.“
Baba ya k'wallawa Nusrat kira, Nusrat da ke d'aki tun da ta dawo daga kitso kanta ke ciwo shine ta nemi guri ta kwanta, ta na jiyo abinda Iya ke cewa Baba gabanta ya yanke ya fad'i, da ta ji kwa ya k'wallo mata kira nan da nan idonta ya yi rau-rau zai fidda ruwa, a hankali ta mik'e ta fito ba tare da ta amsa kiran ba, kallonta Shukhura ta yi da ke kwashe tuwo ta cika k'atuwar kula ta kai d'akinsu, tace.
"Kinga dai da abinda ta saka miki ko? kuma wannan ba shi zai hana gobe idan tace yimin kaza kiyi mata ba. “
Ba tace mata komai ba sai juya idonta da tayi da ya fara fitar da ruwa ta nufi tsakar gidan, Shuk'hura kuwa taci gaba da kwashe tuwonta ta na mamakin sanyin hali irin na Nusrat, ta yi k'wafa a hankali, a ranta tace.
'Iya kenan, ai gara ki tab'ani akan ki tab'a Yayarmu wallahi, don ba ki son son da nake mata bane.'

Baba na ganin ta taho a sanyaye ya saki murmushi had'e da fad'in.
"Taho mana 'yar baiwa. “
Ganin murmushi akan fuskar Baban nata yasa ta samu k'arfin guiwar k'arasawa gareshi, bak'ar ledar hannunsa ya mik'a mata, me d'auke da d'ata manya-manya kasancewar yasan ta na matuk'ar son d'ata, kana yace.
"Ga masoyin naki.“
Murmushi me sauti ta saki tace.
"Na gode Babana. “
Baki galala Iya ta saki ta na kallonsu daga bisani ta tafa hannuwa tace.
"Yau naga lalacewa ni Asabe, yanzu ina gaya maka abinda yarinyar nan ta yi mini amma kai d'ata ka d'auka ka bata, gani ni wacce na yi silar zuwanka duniya ka san da cewa ina mutuwar son ka'za amma baka tab'a siyowa ka bani ni kad'ai a gidan nan ba, sai dai ka siyo gaba d'aya aci, amman ita da yake shafi da mai ce ka ware ta cikin 'yan uwanta uku, ture biyunma tunda su cikinsu d'aya ai ko Nimha ka siyowa don gudun fitina.“
Chapter 2 · 0% Book details