Sashe 41
Katanga Complete Hausa Novel · about 8 min read
Rungume juna suka yi da Daddy, yana jin soyayyar d'an d'an uwan nasa na kuma huda ko wata k'ofa ta zuciyarsa, yana jinsa sosai cikin ransa kamar shine ya haifesa, yayin da shima Rj in soyayyar Daddyn nasa ke kuma ninkaya cikin zuciyarsa, shi maraya ne amman baisan wani abu maraici ba, duk wata k'ofa da zata sakashi tuna shi maraya ne Daddy ya toshe masa ita, Daddyn yakewa kallon mahaifinsa tunda da shi ya tashi ya bud'i ido mahaifinsa ya rasu ba tare da ya mallaki hankalinsa ba sai Allah ya bashi wani mahaifin wanda suka shak'u da juna yake kuma share masa hawayensa a duk sanda sukai kokarin zuba.
Kallonsa Hidaya take kamar ta lashe shi, ya k'ara kyau ya k'ara girma fatarsa ta goge ya zama ingarmar namiji, wani sonsa da k'aunarsa take ji yana kuma shiga ruhi da zuciyarta, ashe hotunan da ya turo mata b'oye wani kaso daga kyahunsa sukayi.
"Hidaya na canja miki ne?"
Rj ya jefo mata wannan tambayar ganin irin kallon da take masa, wata kunya ce ta kamata ta rufe fuskarta da hannuwanta tana dariya kafin tace."Allah Yaa Rj ka canja sosai, kamar ba kai ba."
"Ke ba kiga canjawar da kikayi ba kenan sai tawa?"
Wani dad'i ne ya ziyarci ruhinta cike da jin dad'i tace.
"Dan Allah Yaa Rj na canja?"
"Kin canja mana, tunda ba haka na tafi na barki ba."
"To wata iriyar canjawa nayi."
Tana so taji yace ta k'ara kyau ne, kamar yadda ta gani a tare da shi, muryar Daddy ce ta katsesu da cewa.
"Ku muje gida mana, in munje kwayi hirar."
A ransa yana adduar Allah ya cika masa burinsa ya had'a zuciyoyin Hidaya da Rj in guri guda.
Sai da ya fara shiga suka gaisa da Mommy, Abbas da Hibba sukai masa barka da dawowa kana ya fito ya nufi phart insa da ke gefen gidan zuciyarsa cike da murad'in ganin Nusrat, yana mamakin rashin ganinta da baiyi ba kuma ba ya son tambayar Hidaya don ya fuskanci ba ta so, tunda babu yadda baiyi da ita akan ta had'ashi da Nusrat in a waya tak'i ba, kullum da k'aryar da zata shafto masa, haka da yace ta d'au hotonta ta turo masa ta shiriritar da zancen, ya rasa inda Hidayan ta saka gaba, shi dai a iya saninsa bai taba nuna mata wata alama ta yana sonta ba don shi zuciyarsa Nusrat kawai take so da ita kad'ai yake jin zai iya rayuwa, kwana yake yana mik'awa Allah kukansa akan yabar masa Nusrat insa ba tare da wani ya aureta ba har ya dawo, sai gashi Allah ya amshi adduarsa, Nusrat ta rik'e alkawari da yardar ubangiji.
Wanka yayi da ruwa mai zafi yadda zai huce gajiya, ya d'auro alwala ya fita masallaci bayan ya shirya cikin black in jus da red in t shirt a gaggauce kar ya rasa jam'i, a masallacin ya zauna har sai da yayi sallar isha kana suka shigo cikin gidan tare da Daddy suna tab'a hira a tsakaninsu duk akan aikinsa da cigaban da ya samu, shekararsa biyu da gama karatunsa suka rik'esa a can yayi musu aiki saboda kaifin basira da k'wak'walwar da Allah ya bashi, yanzu ma sun so cigaba da rik'e shin yak'i yarda gaba d'aya hankalinsa yayo gida, shekara uku sukayi da Nusrat sai gashi ya d'ebi shekaru har biyar, inda Allah ya taimakeshi ma ta rik'e masa alk'awarinsa wanda bai tsanmata ba ganin ya sab'a k'aida.
A dining sukayi masauki, Hidayace yau tayi serving in kowa da k'ayataccen girkin da Nusrat in tayi saboda RJ inta.
"Yau ina Nusrat in?"
Daddy ya fad'a yana kallon Hidaya, wanda ya nuna ita yakewa tambayar, d'an sosa kanta tayi kafin tace.
"Cewa tayi kanta na ciwo ba za ta iya fitowa ba."
Mayar da kallonsa yayi kan Hibba kafin yace.
"Maza jeki ki kirahomin ita."
Rj ji yayi kamar Daddy ya tsunduma shi a aljanna da ya tura a kiraho hasken idaniyarsa.
Ina fama da rashin chargi shiyasa kuke jina shiru, ni kaina na k'agu naga munyi nisa cikin labarin amman ko tsakiya ba muzo ba, idan komai ya daidaita zakuna jina sosai da sosai na gode.
[4/26, 8:44 PM] Rabi: BEBE'ARTH
KTG27
Waya suka gama da Yusra, sai ta fara yin game a k'aramar wayarta, saboda ji tayi sam ba ta buk'atar fita cin abincin ba ta san ya gamuwarsu da Rj zata kaya ba, jin za'a murd'a handle in k'ofar yasata d'aga kanta don ganin me shigowar, Hibba ce ta shigo da sallama a bakinta, Nusrat ta amsa mata tana mayar da kanta kan wayarta.
"Aunty Hidaya ce tacewa Daddy wai kanki na ciwo, shine yace nazo na kiraki."
Hmmmm Hidaya me take nufi da ni ne, don kawai ba ta son na fita mu had'u da Rj har sai tayi mini k'aryar ciwo?
Shine tambayar da Nusrat kewa kanta, kafin tacewa Hibban.
"Kicewa Daddy na samu bacci kawai."
"Toh" Ta amsa mata da shi ta fita.
"Ta samu bacci."
Shine abinda ta cewa Daddy, kai kawai ya d'aga mata saboda ya fara cin abinci, yayin da Rj bai yadda da zancen Hibban ba, to tunda tak'i fitowa shi zaije har d'akin ya same ta, bayan Daddy ya kammala cin abincin ya kalli Hidaya da ke ta cin abincin cikin yanga saboda do take kowa ya fashe a barta daga ita sai Rj intadon shima ta fuskanci cin yangar yakewa abincin,yace.
"In kin gama ki iba mata abincin, ga awararta nan, ki tabbata kin tasheta taci tasha magani."
Da "Toh" Ta amsawa Daddyn da ya tashi ya bar dining in Mommy ta mara masa baya saboda ta gama itama, Hibba da Abbas suka tashi kowa ya nufi d'akinsa ya zamto sai su biyu kad'ai akan dininin in, a hankali ya mik'e don dama ya k'oshi da abincin jira yake a bashi guri, plate ya d'auka ya zuba abinci d'an dai dai kana ya d'auki awarar da Daddy yace ta Nusrat ce ya haye sama, baki sake Hidaya ta saki tana kallonsa har ya gama haye matattakalar.
Gajiya tayi da game in don haka ta kashe ta gyara kwanciyarta sosai akan gadon ta ja duvet ta rufe rabin jikinta, a hankula ta lumshe idanuwanta ta luntsuma cikin kogin tunanin nemo mafitar zuciyarta akan soyayyar Rj don yadda taga take taken Hidaya yafi kawai ta sanyawa kanta ruwan sanyi ta hak'ura da shi, tun da dama ba wai cewa yayi yana sonta ba itace take haukanta.
knocking yayi murya can k'asa tace.
"Shigo."
Tana tunanin Mommy ce don itace me yi musu knocking kafin ta shigo, a hankula ya turo k'ofar ya shigo idanuwansa gaba d'aya suka sauka cikin nata, a lokaci d'aya bugun zuciyoyinsu suka sauya, kallon cikin idonta yake sosai wanda ta kasa jurewa hakan ta kautar da kanta gefe, wani d'an k'aramin center table ya janyo ya d'ora plate in da ledar awarar, sai da yayi gyaran murya kafin yace.
"Ni gani nazo tunda guduna ake, saboda ni anki saukowa cin abinci to gashinan abincin ya biyo ki sai ki d'auka ki ci."
Bagarar da zancen nashi tayi da cewa.
"Ina wuni, an dawo lafiya.?"
"Tambayeni kiji."
"To ai tambayar taka nayi."
Baice mata komai ba ya hau dube dube d'aga can duba can kallonshi tayi da mamaki had'e da fad'in.
"Wai me kake nema?"
"Murmushinki nake nema, so nake na lalibo shi a duk inda kika b'oyeshi saboda nayi kewarsa mara misali."
Wani bazataccen murmushi ne ya sub'uce mata had'e da wata siririyar dariya, dariyar shima yake ya tsaya yana mata wani narkakken kallo kafin cikin wata murya mai shauk'i ya kira sunanta.
"Nusrat."
A hankali ta d'ago kanta idanuwansu suka gauraya guri guda, wani maganad'iso ne yake janshi daga cikin idanuwanta ji yake idan bai furta abinda ke k'irjinsa shekaru masu yawa ba yana k'ara yin nauyin da ke k'ok'arin yi masa illa gaba d'aya ba kamar numfashinsa zai rabu da gangar jikinsa ne, cikin wata shauk'ak'k'iyar murya tace.
"Ilove you Nusrat, ban san da wani baki zan gode miki ba, kinyi namijin k'ok'arin da ba ko wacce mace ce zata yishi ba, kin toshe kunnuwanki daga jin gori da habaicin rashin aure saboda cika alk'awarin da kika d'aukar mini duk da ni na sab'a k'aidar k'ara shekaru biyu kan ukun da na ibar miki wanda nima ba a son raina hakan ya faru ba, ban tab'a tunanin zan dawo na tarar kina jiranaba sai gashi kin bani mamaki, tabbas na jinjina miki jinjina ta ban girma sarauniyata, ina so a bani damar da zan shayar da ke ruwan soyayyata mai gard'i wacce na dad'e ina tanadinta da b'oyeta duk saboda ke Nusrat."
Zuciyarta wani irin bugawa take da sauri, tana jin yadda take bud'ewa da karb'ar sak'on soyayyar Rj in me girma, ashe da ba jin sonsa take ba,yanzu ne take jin aininhin soyayyarsa cikin zuciyarta wanda ba ta shiryawa hakan ba saboda hango tari matsalar da ke gabansu amman da dukkan alamu zuciyarta ta shiryawa hakan ba tare da tabi shawararta ba, wani irin yanayi take ji a cikinta mara misaltuwa."
"Kinyi shiru Nusrat, kice wani abu mana pls."
Ya fad'a da karyayyar muryarsa yana kallonta.
Momy ce ta sauko daga benen Daddy ta tarar da Hidaya ita kad'ai a zaune akan dininng tayi zurfi cikin tunani, ranta gaba d'aya a dagule, d'an zungurunta Momy tayi had'e da fad'in.
"Ke kuma lafiya kowa ya tashi ya bar ki a zaune, me kike zaman jira ina Rj in?"
D'an sosa kanta tayi tana b'oye yanayin da zuciyarta ke ciki tace.
" Shine yace na jirashi yaje ya dawo."
"Ok"
Mommyn tace tana hayewa samansu, ajiyar zuciya Hidaya ta sauke tana jin yadda zuciyar tata tayi mata nauyi, number Ishaq ta lalibo ta danna masa kira ta sanya ta free kana ta haye saman ta murd'a handle in k'ofar a dai dai sanda Rj in ya kuma fad'in.
"Pls Nusrat, say something mana"
Yakai k'arshen maganar yana dak'una fuska, kafin gaba d'aya su zubawa k'ofar ido don ganin me shigowar, zuciyar Nusrat na bugawa da tsoron ko Momy ce, ganin Hidaya ce yasata sakin b'oyayyar ajiyar zuciya, mik'o mata wayar Hidaya tayi had'e da fad'in.
"Ishaq ke magana."
Don a lokacin muryarsa ta bayyana tarwai yana.
"Hello."
Kallonsa Hidaya take kamar ta lashe shi, ya k'ara kyau ya k'ara girma fatarsa ta goge ya zama ingarmar namiji, wani sonsa da k'aunarsa take ji yana kuma shiga ruhi da zuciyarta, ashe hotunan da ya turo mata b'oye wani kaso daga kyahunsa sukayi.
"Hidaya na canja miki ne?"
Rj ya jefo mata wannan tambayar ganin irin kallon da take masa, wata kunya ce ta kamata ta rufe fuskarta da hannuwanta tana dariya kafin tace."Allah Yaa Rj ka canja sosai, kamar ba kai ba."
"Ke ba kiga canjawar da kikayi ba kenan sai tawa?"
Wani dad'i ne ya ziyarci ruhinta cike da jin dad'i tace.
"Dan Allah Yaa Rj na canja?"
"Kin canja mana, tunda ba haka na tafi na barki ba."
"To wata iriyar canjawa nayi."
Tana so taji yace ta k'ara kyau ne, kamar yadda ta gani a tare da shi, muryar Daddy ce ta katsesu da cewa.
"Ku muje gida mana, in munje kwayi hirar."
A ransa yana adduar Allah ya cika masa burinsa ya had'a zuciyoyin Hidaya da Rj in guri guda.
Sai da ya fara shiga suka gaisa da Mommy, Abbas da Hibba sukai masa barka da dawowa kana ya fito ya nufi phart insa da ke gefen gidan zuciyarsa cike da murad'in ganin Nusrat, yana mamakin rashin ganinta da baiyi ba kuma ba ya son tambayar Hidaya don ya fuskanci ba ta so, tunda babu yadda baiyi da ita akan ta had'ashi da Nusrat in a waya tak'i ba, kullum da k'aryar da zata shafto masa, haka da yace ta d'au hotonta ta turo masa ta shiriritar da zancen, ya rasa inda Hidayan ta saka gaba, shi dai a iya saninsa bai taba nuna mata wata alama ta yana sonta ba don shi zuciyarsa Nusrat kawai take so da ita kad'ai yake jin zai iya rayuwa, kwana yake yana mik'awa Allah kukansa akan yabar masa Nusrat insa ba tare da wani ya aureta ba har ya dawo, sai gashi Allah ya amshi adduarsa, Nusrat ta rik'e alkawari da yardar ubangiji.
Wanka yayi da ruwa mai zafi yadda zai huce gajiya, ya d'auro alwala ya fita masallaci bayan ya shirya cikin black in jus da red in t shirt a gaggauce kar ya rasa jam'i, a masallacin ya zauna har sai da yayi sallar isha kana suka shigo cikin gidan tare da Daddy suna tab'a hira a tsakaninsu duk akan aikinsa da cigaban da ya samu, shekararsa biyu da gama karatunsa suka rik'esa a can yayi musu aiki saboda kaifin basira da k'wak'walwar da Allah ya bashi, yanzu ma sun so cigaba da rik'e shin yak'i yarda gaba d'aya hankalinsa yayo gida, shekara uku sukayi da Nusrat sai gashi ya d'ebi shekaru har biyar, inda Allah ya taimakeshi ma ta rik'e masa alk'awarinsa wanda bai tsanmata ba ganin ya sab'a k'aida.
A dining sukayi masauki, Hidayace yau tayi serving in kowa da k'ayataccen girkin da Nusrat in tayi saboda RJ inta.
"Yau ina Nusrat in?"
Daddy ya fad'a yana kallon Hidaya, wanda ya nuna ita yakewa tambayar, d'an sosa kanta tayi kafin tace.
"Cewa tayi kanta na ciwo ba za ta iya fitowa ba."
Mayar da kallonsa yayi kan Hibba kafin yace.
"Maza jeki ki kirahomin ita."
Rj ji yayi kamar Daddy ya tsunduma shi a aljanna da ya tura a kiraho hasken idaniyarsa.
Ina fama da rashin chargi shiyasa kuke jina shiru, ni kaina na k'agu naga munyi nisa cikin labarin amman ko tsakiya ba muzo ba, idan komai ya daidaita zakuna jina sosai da sosai na gode.
[4/26, 8:44 PM] Rabi: BEBE'ARTH
KTG27
Waya suka gama da Yusra, sai ta fara yin game a k'aramar wayarta, saboda ji tayi sam ba ta buk'atar fita cin abincin ba ta san ya gamuwarsu da Rj zata kaya ba, jin za'a murd'a handle in k'ofar yasata d'aga kanta don ganin me shigowar, Hibba ce ta shigo da sallama a bakinta, Nusrat ta amsa mata tana mayar da kanta kan wayarta.
"Aunty Hidaya ce tacewa Daddy wai kanki na ciwo, shine yace nazo na kiraki."
Hmmmm Hidaya me take nufi da ni ne, don kawai ba ta son na fita mu had'u da Rj har sai tayi mini k'aryar ciwo?
Shine tambayar da Nusrat kewa kanta, kafin tacewa Hibban.
"Kicewa Daddy na samu bacci kawai."
"Toh" Ta amsa mata da shi ta fita.
"Ta samu bacci."
Shine abinda ta cewa Daddy, kai kawai ya d'aga mata saboda ya fara cin abinci, yayin da Rj bai yadda da zancen Hibban ba, to tunda tak'i fitowa shi zaije har d'akin ya same ta, bayan Daddy ya kammala cin abincin ya kalli Hidaya da ke ta cin abincin cikin yanga saboda do take kowa ya fashe a barta daga ita sai Rj intadon shima ta fuskanci cin yangar yakewa abincin,yace.
"In kin gama ki iba mata abincin, ga awararta nan, ki tabbata kin tasheta taci tasha magani."
Da "Toh" Ta amsawa Daddyn da ya tashi ya bar dining in Mommy ta mara masa baya saboda ta gama itama, Hibba da Abbas suka tashi kowa ya nufi d'akinsa ya zamto sai su biyu kad'ai akan dininin in, a hankali ya mik'e don dama ya k'oshi da abincin jira yake a bashi guri, plate ya d'auka ya zuba abinci d'an dai dai kana ya d'auki awarar da Daddy yace ta Nusrat ce ya haye sama, baki sake Hidaya ta saki tana kallonsa har ya gama haye matattakalar.
Gajiya tayi da game in don haka ta kashe ta gyara kwanciyarta sosai akan gadon ta ja duvet ta rufe rabin jikinta, a hankula ta lumshe idanuwanta ta luntsuma cikin kogin tunanin nemo mafitar zuciyarta akan soyayyar Rj don yadda taga take taken Hidaya yafi kawai ta sanyawa kanta ruwan sanyi ta hak'ura da shi, tun da dama ba wai cewa yayi yana sonta ba itace take haukanta.
knocking yayi murya can k'asa tace.
"Shigo."
Tana tunanin Mommy ce don itace me yi musu knocking kafin ta shigo, a hankula ya turo k'ofar ya shigo idanuwansa gaba d'aya suka sauka cikin nata, a lokaci d'aya bugun zuciyoyinsu suka sauya, kallon cikin idonta yake sosai wanda ta kasa jurewa hakan ta kautar da kanta gefe, wani d'an k'aramin center table ya janyo ya d'ora plate in da ledar awarar, sai da yayi gyaran murya kafin yace.
"Ni gani nazo tunda guduna ake, saboda ni anki saukowa cin abinci to gashinan abincin ya biyo ki sai ki d'auka ki ci."
Bagarar da zancen nashi tayi da cewa.
"Ina wuni, an dawo lafiya.?"
"Tambayeni kiji."
"To ai tambayar taka nayi."
Baice mata komai ba ya hau dube dube d'aga can duba can kallonshi tayi da mamaki had'e da fad'in.
"Wai me kake nema?"
"Murmushinki nake nema, so nake na lalibo shi a duk inda kika b'oyeshi saboda nayi kewarsa mara misali."
Wani bazataccen murmushi ne ya sub'uce mata had'e da wata siririyar dariya, dariyar shima yake ya tsaya yana mata wani narkakken kallo kafin cikin wata murya mai shauk'i ya kira sunanta.
"Nusrat."
A hankali ta d'ago kanta idanuwansu suka gauraya guri guda, wani maganad'iso ne yake janshi daga cikin idanuwanta ji yake idan bai furta abinda ke k'irjinsa shekaru masu yawa ba yana k'ara yin nauyin da ke k'ok'arin yi masa illa gaba d'aya ba kamar numfashinsa zai rabu da gangar jikinsa ne, cikin wata shauk'ak'k'iyar murya tace.
"Ilove you Nusrat, ban san da wani baki zan gode miki ba, kinyi namijin k'ok'arin da ba ko wacce mace ce zata yishi ba, kin toshe kunnuwanki daga jin gori da habaicin rashin aure saboda cika alk'awarin da kika d'aukar mini duk da ni na sab'a k'aidar k'ara shekaru biyu kan ukun da na ibar miki wanda nima ba a son raina hakan ya faru ba, ban tab'a tunanin zan dawo na tarar kina jiranaba sai gashi kin bani mamaki, tabbas na jinjina miki jinjina ta ban girma sarauniyata, ina so a bani damar da zan shayar da ke ruwan soyayyata mai gard'i wacce na dad'e ina tanadinta da b'oyeta duk saboda ke Nusrat."
Zuciyarta wani irin bugawa take da sauri, tana jin yadda take bud'ewa da karb'ar sak'on soyayyar Rj in me girma, ashe da ba jin sonsa take ba,yanzu ne take jin aininhin soyayyarsa cikin zuciyarta wanda ba ta shiryawa hakan ba saboda hango tari matsalar da ke gabansu amman da dukkan alamu zuciyarta ta shiryawa hakan ba tare da tabi shawararta ba, wani irin yanayi take ji a cikinta mara misaltuwa."
"Kinyi shiru Nusrat, kice wani abu mana pls."
Ya fad'a da karyayyar muryarsa yana kallonta.
Momy ce ta sauko daga benen Daddy ta tarar da Hidaya ita kad'ai a zaune akan dininng tayi zurfi cikin tunani, ranta gaba d'aya a dagule, d'an zungurunta Momy tayi had'e da fad'in.
"Ke kuma lafiya kowa ya tashi ya bar ki a zaune, me kike zaman jira ina Rj in?"
D'an sosa kanta tayi tana b'oye yanayin da zuciyarta ke ciki tace.
" Shine yace na jirashi yaje ya dawo."
"Ok"
Mommyn tace tana hayewa samansu, ajiyar zuciya Hidaya ta sauke tana jin yadda zuciyar tata tayi mata nauyi, number Ishaq ta lalibo ta danna masa kira ta sanya ta free kana ta haye saman ta murd'a handle in k'ofar a dai dai sanda Rj in ya kuma fad'in.
"Pls Nusrat, say something mana"
Yakai k'arshen maganar yana dak'una fuska, kafin gaba d'aya su zubawa k'ofar ido don ganin me shigowar, zuciyar Nusrat na bugawa da tsoron ko Momy ce, ganin Hidaya ce yasata sakin b'oyayyar ajiyar zuciya, mik'o mata wayar Hidaya tayi had'e da fad'in.
"Ishaq ke magana."
Don a lokacin muryarsa ta bayyana tarwai yana.
"Hello."