← Book details Katanga Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 17 OF 69

Sashe 17

Katanga Complete Hausa Novel · about 7 min read

Sai da Iya ta kinta tanci dawowar Baba ta fito babban tsakar gida ta k'wama kujera ta na jiran dawowarsa, aikwa ta na jin sallamarsa ta saki kuka me k'arfi, a gigice ya nufota ya na tambayarta.
"Lafiya Iya, me ya faru kike kuka haka?"
Face hanci Iya ta yi tace.
"Wai ni yau A'i za ta kalli tsabar idona ta zageni ta uwa ta uba. “
" 'Yar baiwa.“
Baba ya k'wallawa Nusrat kira, Nusrat da ke d'aki tun da ta dawo daga kitso kanta ke ciwo shine ta nemi guri ta kwanta, ta na jiyo abinda Iya ke cewa Baba gabanta ya yanke ya fad'i, da ta ji kwa ya k'wallo mata kira nan da nan idonta ya yi rau-rau zai fidda ruwa, a hankali ta mik'e ta fito ba tare da ta amsa kiran ba, kallonta Shukhura ta yi da ke kwashe tuwo ta cika k'atuwar kula ta kai d'akinsu, tace.
"Kinga dai da abinda ta saka miki ko? kuma wannan ba shi zai hana gobe idan tace yimin kaza kiyi mata ba. “
Ba tace mata komai ba sai juya idonta da tayi da ya fara fitar da ruwa ta nufi tsakar gidan, Shuk'hura kuwa taci gaba da kwashe tuwonta ta na mamakin sanyin hali irin na Nusrat, ta yi k'wafa a hankali, a ranta tace.
'Iya kenan, ai gara ki tab'ani akan ki tab'a Yayarmu wallahi, don ba ki son son da nake mata bane.'

Baba na ganin ta taho a sanyaye ya saki murmushi had'e da fad'in.
"Taho mana 'yar baiwa. “
Ganin murmushi akan fuskar Baban nata yasa ta samu k'arfin guiwar k'arasawa gareshi, bak'ar ledar hannunsa ya mik'a mata, me d'auke da d'ata manya-manya kasancewar yasan ta na matuk'ar son d'ata, kana yace.
"Ga masoyin naki.“
Murmushi me sauti ta saki tace.
"Na gode Babana. “
Baki galala Iya ta saki ta na kallonsu daga bisani ta tafa hannuwa tace.
"Yau naga lalacewa ni Asabe, yanzu ina gaya maka abinda yarinyar nan ta yi mini amma kai d'ata ka d'auka ka bata, gani ni wacce na yi silar zuwanka duniya ka san da cewa ina mutuwar son ka'za amma baka tab'a siyowa ka bani ni kad'ai a gidan nan ba, sai dai ka siyo gaba d'aya aci, amman ita da yake shafi da mai ce ka ware ta cikin 'yan uwanta uku, ture biyunma tunda su cikinsu d'aya ai ko Nimha ka siyowa don gudun fitina.“

"D'atan da na siyo mata na tabbata ba za ta cishi ita kad'ai ba, rabawa zasui gaba d'aya da ita da 'yan uwanta, zancen kuma Nusrat ta zage ki wallahi Iya ko jikina duk kunne ne bazan tab'a yadda za ta iya zaginki ba, ko da kuwa dukan mutuwa kikai mata a cikin gidan nan, bare kuma na san halinta ba sawa ba fitarwa, da dai Shukhura kika ce to tabbas wannan zan yadda amma 'yar baiwa lalala, sai dai kice Shukhura ce ta zageki kikace 'yar baiwa ce saboda.... ”Da sauri Iya ta dakatar da shi da fad'in.
'Ni wallahi bance maka Safiya ba, ko sunanta ban ambata a gurin nan ba in ba yanzu ba, jama'a ko kunji na ambaci Safiya? “
Ta fad'a da k'arfi yadda 'yan ciki zasu jiyo ta, murmushi Baba kawai ya yi ya ja hannun Nusrat sukai ciki.
"Kedai Mero kin haifi jarabar aljanu a gidan nan, yarinya ta bi ta zamar muku masifa duk kunfi k'aunarta cikin 'yan uwanta, su kuma hakan ko kad'an hakan ba ya damunsu, wannan wata iriyar musifa ce?
Kai kuwa Audu k'atuwar asara ce ta hau kanka don zan iya dafa qur'ani kafi son wannan 'yar aljanun ko nace 'yar ruwa akan ni da na diroka duniya, bacin haka har maganata za ka k'aryata ka zab'i d'iyarka, babu komai ai gobe Shamsu zai zo garin, Allah sarki d'an albarka na san gobe miyarmu da ka'ji zan cisu har na ture, don ni ina jin idan yazo ma tattara kayana zan na bisa, don wallahi na gaji da cin shinkafa 'yar hausa da tuwon garin masara kullum suna cushe maka a ciki, don na ji ana rad'e rad'en tuwon masara gini yake a cikin mutum, haka kawai na zauna naje na kashe kaina tun wa'adina bai cika ba. “

Sai misalin k'arfe takwas Mama ta dawo, kallon Nusrat da ke kwance ta yi tace.
"Ina Mamana, Yusra taci abinci da kika barta tai bacci?”
"Cikin gida tace mini za ta shiga tun d'azu, Yusra kuma sai da taci abinci tukunna tai bacci. “
"Lafiyanki kuwa naga kina yatsina fuska? “
Ta tambayeta duk da a ranta mamakin wai Shukhura ce tace ta tafi cikin gida, bayan ba k'aunar zuwa gidan take ba, aike ma da dole take shiga.
"To ki tashi ga fura na taho miki da ita kisha sai ki sha magani.“
Da hanzari ta mik'e don dama yunwa take ji kuma har ga Allah ba ta k'aunar cin tuwon donma ta d'an ci d'atan da Baba ya kawo mata duk da wasu sunce shima ya na faifaye ciki, ita kuwa Mama sanin halin d'iyar ta ta yasa ta yo mata guzurin furar.

Sauke idanuwanta ta yi akan kular tuwon da Shukhura ta ajiye, a fili tace.
"Allah ya shirya mini ke mamana. Maza Nusrat ki gama kije ki kira mini ita. “
Ta na rufe bakinta ta jiyo sallamarta suka amsa mata.
"Laa Mamanmu kin dawo ashe? sannunki da dawowa. “
Fuska a had'e tace.
"Yauwa, me kika je yi cikin gida? “
"Nifa ba cikin gida nace mata zanje ba, gidan su Farha nace mata za ni kallo.“
Takai k'arshen maganar ta na kallon fuskar Nusrat.
"Ban hana ki zuwa kallo ba?to da Babanku kawai zan had'aki na huta, Ke kuma ai ga shinan kin rufa mata asiri ta tonawa kanta. “
Takai k'arshen maganar ta na kallon Nusrat, yayin da ita kuma ta saki murmushi.
"Kiyi hak'uri Mamanmu bazan sake ba. “
"Sau nawa kina fad'in haka? “
"Allah da gaske nake Mamanmu daga wannan bazan sake ba. “
"To wancan uban tuwon da kika ajiye da fatan abincinki ne na sati guda ko?“
"Haba² Mama, sai kace wacce uwarta ta tsine mata duniya ta juya mata baya zan jera sati guda ina cin tuwo, tuwonma ba sabo za'a dinga yi mini ba. “
Mama ta so yin dariya amma ta kanne tace.
"Koma me zaki ce kice, amma wancen tuwon sai kinyi sati kina cinsa a gidan nan tun da ke kunnenki na k'ashi ne ba ya jin magana, bacin sau nawa zance ki daina cika mini kula kina kawo mini d'aki? “
Sai da ta fara turo bakin nan gaba kana tace.
"To kina dai kallo duk ran girkinta sai ta cika kula fam ta kai d'aki, bacin daga ita sai 'yarta d'aya kamar rai, mu kuwa ta milliro mana, ta cikawa Baba da sirikarta kwano, nima kuwa yau na rama na millira musu na millirawa Iya ma, Baba kuwa na cika masa kwano har ya na zuba. “
Salati Mama ta yi ta saki baki ta na kallon Shukhura.
"To don ita ta na cika kula ta kai d'aki ita ta shafa, sune mayunwata ba mu ba, ga shinan yanzu kin sakani a bakin duniya, tijarar Iya ma kad'ai ta isheni, don cewa za tai ina sani na baki girkin shiyasa har ga Allah ban son na bar miki girki na fita. “
"A to don wallahi muddun ni nai girki bazan fasa ciko mana kula na kawo d'aki ba, ko ba za muci ba sai dai mui asararsa. “
"Me kika ce?“
Mama ta tambayeta kasancewar k'asa² tai maganar.
"A'a cewa na yi kiyi hak'uri bazan kuma ba. “
"To zo ki fice mini da kular, kije ki k'ara musu tuwon.“
Ta na jin haka ta saki k'ara.
"Waishhhhhh Mama kashi² ina zuwa ta fice da gudu zuwa ban d'aki, murmushi Mama ta yi a ranta ta na nemawa Shukhura shiriya ta d'auki kular tuwon ta fita, murmushi ma Nusrat keyi tun fara dramar Maman da Shukhura, don dama sun riga da sun saba......

300 za ku biya domin samunsa cikin sauk'i.
0567838462
NABABA FADILA SHU'AIB
GTBANK
In kuma katin waya ne ki turo ta wannan layin, shaidarki ta biyama ki turo cikinta.
09037093702.
In katin wayane 400 Za ku biya.

Garab'asa gareku masoyana duk wacce ta sayi wannan littafin za ta sami wanda zan rubuta gaba kyauta, ban yadda ki sayi littafina ki dinga turawa gruop ba, in hakan za kiyi ki sameni a layina muyi magana.

Allah ka k'arawa mahaifanmu lafiya da nisan kwana, Amin.

#Team KTG
#N.W.A
[10/8, 3:42 PM] Binta Lawan: https://chat.whatsapp.com/L7ZWZtJoVg39WGbG36r78I. Pls share

*BEBE'ARTH*

Wattpad@Rashuna

*KATANGA*

____________
*THREE*
Chapter 17 · 0% Book details