Sashe 44
Katanga Complete Hausa Novel · about 8 min read
Idanuwanta sun kuma kad'awa sunyi jazur sun tara ruwa ruwan da ta kasa rik'eshi har sai da suka zubo ta gefen idanuwanta cikin murya cike da son yin kuka tace.
"Wallahi Momy ban son da maganar aure tsakanin Hidaya da Rj ba da bazan bashi damar da ya nema a gareni ba, ba nice na cusa kaina gareshi ba shine ya cuso kansa gaba d'aya cikin rayuwata kuma ba tun yau ba tun ban fahimci mece soyayya ba, da na san da maganarsa da Hidaya da bazan bud'e zuciyata gareshi ba, amman yanzu tabbas lokacin rufeta yayi rufewa ta har abada, amman ina buk'atar komawa gida hakan zaifi shafawa rayuwata lafiya ."
"Ni kuma bazai shafa mini lafiya ba, kiyi aure kawai shine kwanciyar hankalina."
Cewar Hidaya yayin da Momy tace.
"K'warai kuwa Nusrat auranki shi zai tabbatar mana da samuwar Rj a hannun Hidaya, don haka ina me sanar da ke gobe manema auranki zasu zo daga gidan su Ishaq samun nutsuwarki ki mik'a wuya zuwa ga wannan aure idan kuwa kika k'i to tabbas zan wulakanta rayuwarki fiye da yadda kike zato don zan iya sauka akan ko wani mataki don ganin yarinyata ta samu farin ciki da nutsuwa."
Wayarta ce tayi k'ara wacce kirane daga Daddy akan suzo ita da Nusrat da Hidaya, gasunan kawai tace tana kashe wayar ta ajiye gami da sauke idonta kan Nusrat wacce kawai ga tanan a zaune ne ta kasa sarrafa k'wak'walwarta hade da zuciyarta.
"Ki musa maganar auranki na tabbatar miki da abinda nake nufi, muje falon Daddy yana son ganinmu."
Tana fadin haka suka mik'e tare da Hidaya suka nufi k'ofa wanda ya bawa Hibba damar dai daita nutsuwarta a bakin k'ofar kamar a lokacin za ta shigo, a tare suka murd'a kofar suna budewa babu wanda yace da ita komai kallo daya suka yiyyi mata suka huce.
A hankali take mik'ewa daga zaunen da take tana jin yadda k'afafuwanta suka yi sanyi, sanyin da ba tayi tunanin zasu dauki nauyin gangar jikinta ba, wani irin kunci da zafi zuciyarta take mata, Tabbas iyaye wata babbar katanga ce ga 'yayansu ta tabbata da ace daya daga cikin mahaifanta na raye da bda irin wannan zancen ake a yanzu ba da babu abinda zai kawota zama cikin gidannan bare har hakan ta faru,da ace tasan irin wannan k'addarar na zaman jiranta to tabbas da ba ta yadda zama ya kawota cikin gidannan ba, sai dai kuma ba ka tara sani ga Ubangiji.
Cikin matukar sanyin jiki ta nufi k'ofa za ta fita daga d'akin Hibba na biye da ita da kallon tausayi har za ta fice Hibban tayi saurin fadin.
"Yayarmu, kada ki aikata abinda zuciya da ruhinki ba zasu taba samun nutsuwa da shi ba, ki cire tsoro a ranki babu wani abu da zai faru da rayuwarki face abinda alkalamin kaddararki ya rubuta, an dauke alkaluma kuma takaddun sun bushe."
Juyowa tayi tana kallon Hibban cike da kwarin guiwar da ta samu, murmushi ta sakar mata hade da fadin.
"Thanks"
Tana jin Hibban cikin tamkar yadda take jin Yusranta, murmushi itama Hibban ta sakar mata tana jinta tamkar ciki daya suka fito don har ga Allah ta fi jin shakuwa da ita fiye da Hidayan da suka fito ciki daya.
RJ ne ya sameshi da maganar yana son Nusrat kuma sunma dai daita junansu, duk da yaji wani iri cikin ransa don har ga Allah yaso hada auransa da Hidaya kuma a yadda yake ganinsu yayi tunanin sun dade da dai daita kansu har yake ta tsimayin Rj in yazo ya sameshi da kanshi, a yanzunma da yazo yayi tunanin akan Hidaya ne ashe akan Nusrat ne sai yanzu yakewa maganarsa ta rannan fashin baki da suna dinner yake cewa tabbas zaiyi kewar girkin Nusrat idan tayi aure, yana jin anya kullum ba gidanta zai dinga zuwa dinner ba, sai Rj in yayi dariya yace watakila ma ta wutashsheka zuwa idan ya kasance a kusa kuke kullum da kai za ta saka sanwa.
To maganarsa tana nufin idan shi ya auri Nusrat in kenan, bazai ce bai ji dadin soyayyar Rj da Nusrat inba don itama yana jinta tamkar Hidaya da ya haifa, kuma ya san sun dace da aamun kamilar surika to sai dai kuma kansa ya daure da maganar da suka gama yi da Hidaya yanzu, ga kuma Rj in yace da sanin Nusrat in yazo gurinsa don yanzun nan ma suka rabu wannan dalilin ne yasa ya kira Mommy yace tazo da su gaba d'aya.
Daga Mommy har Hidaya sun firgita da jin Rj inne ya samu Daddy da maganar auren Nusrat, amman kuma sai Hidayan ta kafe akan Nusrat ince ta aikota gurin Daddy akan maganar Ishaq don ba ta son Rj ya riga zuwa saboda ba shi zuciyarta take ainihin so ba, a tare RJ da Nusrat suka daga kai suna kallonta wanda taki yadda ta kalli daya daga cikinsu.
"Nusrat"
Daddy ya kira sunanta ta amsa cikin rawar murya. "Na am"
"Mene ne ainihin gaskiya."
Kuka kawai ta fashe da shi, wanda yazo mata da karfinsa na gaske kuma ba ya bukatar a tsai da shi a yanzu.
"Ga ainihin gaskiya nan, tunda ba'a karya da maganar aure, shi Rj in tun da ba ta sonshi ba sai ya hakura ba, dama aishi Hidaya ce matarsa banda abinka."
Cewar momy kenan, yayin da zuciyar Rj take ta mugun tafarfasa jijiyoyin kansa sun fito rada rada, Daddy kuwa yayi shiru cikin nazari yayin da Nusrat kukanta yake kara karfi.
"Daddy zan gaya maka ainihin gaskiya"
Cewar Hibba da ta d'auke ganinta ga kowa illa Daddy da ta fuskanta, duk da ta tsorata da tsawar da Mommy ta daka mata hade da cewa ta fice ba da ita ake magana ba amman Daddy ya dakatar da ita da fadin yana jinta, tabbas za ta fadi gaskiya ko da kwa Momy za tayi gunduwa da naman jikinta.
"Yayarmu ba ta san maganar Ishaq ba Aunty Hidaya ce ta tsara komai, kuma Momy tayi mata gargadi akan ta amshi maganar auran Ishaq in don Aunty Hidaya ta samu Yaa Rj a hannu."
"Jeki abinki Hibba, Allah ya yi miki albarka."
"Amin Daddy."
Ta tashi ta fita tana kuma tsoron haduwarta da Mommy don sai huci take ta Hidaya kuwa me sauki ce.
"Tabbas Ridwan na so had'a auranka da Hidaya, don duk a tunanina kun jima da hada kanku ashe ba haka abun yake ba, da Hidaya da Nusrat duk daya na daukesu a gurina, idan naki Nusrat tamkar naki Hidaya ne, don haka zanje na nema maka auran Nusrat insha Allah, kuma ba zaa ja lokaci ba kamar yadda kake so."
"Amman banji dadi ba, meyasa Daddy tun tuni ba ka sanar da ni wannan kudirin naka ba?"
"Saboda ba na son ku tirsasa zuciyoyinku yin abinda bashi take so ba, don haka kada kasa komai a ranka, duk sona duk kaunata na ganinku inuwa daya da Hidaya idan Allah bai so ba hakan bazai taba faruwa ba."
Yana kawowa nan ya kalli Hidaya yace .
"Sai ki warware auren da kika so kullawa, don wallahi muddun suka zo gobe to ke zan basu, kuma daga yau kisa a ranki ita soyayya ba'a kwacenta ta dole Allah ne yake dasawa bayinsa ba tare da saninsu ba, da kin mikawa Allah lamuranki kina iya samunsa ta cikin sanyi ba tare da kinsha wahala ba idan har mijinki ne a rubuce bazai taba gogewa ba."
Yana kawowa nan ya tashi zai shige bedroom don wani irin zafin Momy yake ji, saboda irin turbar da ta dora 'yarsa akai, Nusrar da kukanta ya fara yin k'asa ta kirashi.
"Daddy"
Tsayawa yayi yana jiran jin abinda za tace.
"Daddy na hak'ura da Yaa Rj na barwa Hidaya, wallahi ban san da maganar aure tsakaninsu ba, kuma ban san tana sonshi ba duk da ban bude zuciyata gareshi ba, Daddy ni me iya sadaukar da komai ce ga Hidaya muddun hakan zai sama mata kwanciyar hankali."
Gaba daya ya juyo ta zubawa fuskarta idanu, yana kuma jinta cikin ransa, kafin yace.
"Ke da ake so, kinji zaki iya sadaukar mata da shi, amman ita da ita take so ta kasa sadaukar miki sai ma k'okarin cusaki wani guri da take, Hidaya wannan nuni ne gareki, yadda Nusrat ta daukeki ba haka kika dauketa ba, Allah yayi miki albarka Nusrat, tabbas kin samu kyakkyawar tarbiya, amman ina so ki sani aure da ke da Ridwan sai dai in babu shi a rubuce."
Yana kawowa nan yayi shigewarsa d'aki.
。。。。。。
Daddy yaje ya nemawa RJ auran Nusrat gurin Baffa Shamsu, ya kuma bashi babu jaa don duk abin na gida ne, a take ya bada kud'in aure suka tsayar da rana bayan sallah babba.
Rj gaba d'aya ya kasa gane kan Nusrat don duk ta sauya, kullum cikin kunci da damuwa zaka sameta da yayi magana za tace ita wallahi ta hakura ta barwa Hidaya shi, shi kuma ransa yakan baci da jin kalaminta sai yaga kamar dama can ba son nashi take ba, ita kuwa tsoron abinda zai biyo baya take yi, don yanzu Mommy ko gaisuwarta ba ta amsa haka Hidaya ko kallon inda take ba tayi, duk da nasihar da Daddy ya zaunar da ita yayi mata duk a banza, tana tsoron yadda wannan aure zai tafi ya raba zumunci tun kan a daura shi.
Tsakanin Momy da Daddy kuwa babu wani shiri, don tayi mugun shaka da yace Nusrat ta samu tarbiya yana nufin ita ba ta bawa nata yayan tarbiya ba kenan, shiyasa da ya watsar da ita itma ta watsar da shi don tana shirin yadda za ta watsa rayuwar Nusrat ne kawai don diyarta ta samu abinda ta ke so don har ciwo Hidayan ta kwanta bayan ankai kudin Nusrat in.
"Wallahi Momy ban son da maganar aure tsakanin Hidaya da Rj ba da bazan bashi damar da ya nema a gareni ba, ba nice na cusa kaina gareshi ba shine ya cuso kansa gaba d'aya cikin rayuwata kuma ba tun yau ba tun ban fahimci mece soyayya ba, da na san da maganarsa da Hidaya da bazan bud'e zuciyata gareshi ba, amman yanzu tabbas lokacin rufeta yayi rufewa ta har abada, amman ina buk'atar komawa gida hakan zaifi shafawa rayuwata lafiya ."
"Ni kuma bazai shafa mini lafiya ba, kiyi aure kawai shine kwanciyar hankalina."
Cewar Hidaya yayin da Momy tace.
"K'warai kuwa Nusrat auranki shi zai tabbatar mana da samuwar Rj a hannun Hidaya, don haka ina me sanar da ke gobe manema auranki zasu zo daga gidan su Ishaq samun nutsuwarki ki mik'a wuya zuwa ga wannan aure idan kuwa kika k'i to tabbas zan wulakanta rayuwarki fiye da yadda kike zato don zan iya sauka akan ko wani mataki don ganin yarinyata ta samu farin ciki da nutsuwa."
Wayarta ce tayi k'ara wacce kirane daga Daddy akan suzo ita da Nusrat da Hidaya, gasunan kawai tace tana kashe wayar ta ajiye gami da sauke idonta kan Nusrat wacce kawai ga tanan a zaune ne ta kasa sarrafa k'wak'walwarta hade da zuciyarta.
"Ki musa maganar auranki na tabbatar miki da abinda nake nufi, muje falon Daddy yana son ganinmu."
Tana fadin haka suka mik'e tare da Hidaya suka nufi k'ofa wanda ya bawa Hibba damar dai daita nutsuwarta a bakin k'ofar kamar a lokacin za ta shigo, a tare suka murd'a kofar suna budewa babu wanda yace da ita komai kallo daya suka yiyyi mata suka huce.
A hankali take mik'ewa daga zaunen da take tana jin yadda k'afafuwanta suka yi sanyi, sanyin da ba tayi tunanin zasu dauki nauyin gangar jikinta ba, wani irin kunci da zafi zuciyarta take mata, Tabbas iyaye wata babbar katanga ce ga 'yayansu ta tabbata da ace daya daga cikin mahaifanta na raye da bda irin wannan zancen ake a yanzu ba da babu abinda zai kawota zama cikin gidannan bare har hakan ta faru,da ace tasan irin wannan k'addarar na zaman jiranta to tabbas da ba ta yadda zama ya kawota cikin gidannan ba, sai dai kuma ba ka tara sani ga Ubangiji.
Cikin matukar sanyin jiki ta nufi k'ofa za ta fita daga d'akin Hibba na biye da ita da kallon tausayi har za ta fice Hibban tayi saurin fadin.
"Yayarmu, kada ki aikata abinda zuciya da ruhinki ba zasu taba samun nutsuwa da shi ba, ki cire tsoro a ranki babu wani abu da zai faru da rayuwarki face abinda alkalamin kaddararki ya rubuta, an dauke alkaluma kuma takaddun sun bushe."
Juyowa tayi tana kallon Hibban cike da kwarin guiwar da ta samu, murmushi ta sakar mata hade da fadin.
"Thanks"
Tana jin Hibban cikin tamkar yadda take jin Yusranta, murmushi itama Hibban ta sakar mata tana jinta tamkar ciki daya suka fito don har ga Allah ta fi jin shakuwa da ita fiye da Hidayan da suka fito ciki daya.
RJ ne ya sameshi da maganar yana son Nusrat kuma sunma dai daita junansu, duk da yaji wani iri cikin ransa don har ga Allah yaso hada auransa da Hidaya kuma a yadda yake ganinsu yayi tunanin sun dade da dai daita kansu har yake ta tsimayin Rj in yazo ya sameshi da kanshi, a yanzunma da yazo yayi tunanin akan Hidaya ne ashe akan Nusrat ne sai yanzu yakewa maganarsa ta rannan fashin baki da suna dinner yake cewa tabbas zaiyi kewar girkin Nusrat idan tayi aure, yana jin anya kullum ba gidanta zai dinga zuwa dinner ba, sai Rj in yayi dariya yace watakila ma ta wutashsheka zuwa idan ya kasance a kusa kuke kullum da kai za ta saka sanwa.
To maganarsa tana nufin idan shi ya auri Nusrat in kenan, bazai ce bai ji dadin soyayyar Rj da Nusrat inba don itama yana jinta tamkar Hidaya da ya haifa, kuma ya san sun dace da aamun kamilar surika to sai dai kuma kansa ya daure da maganar da suka gama yi da Hidaya yanzu, ga kuma Rj in yace da sanin Nusrat in yazo gurinsa don yanzun nan ma suka rabu wannan dalilin ne yasa ya kira Mommy yace tazo da su gaba d'aya.
Daga Mommy har Hidaya sun firgita da jin Rj inne ya samu Daddy da maganar auren Nusrat, amman kuma sai Hidayan ta kafe akan Nusrat ince ta aikota gurin Daddy akan maganar Ishaq don ba ta son Rj ya riga zuwa saboda ba shi zuciyarta take ainihin so ba, a tare RJ da Nusrat suka daga kai suna kallonta wanda taki yadda ta kalli daya daga cikinsu.
"Nusrat"
Daddy ya kira sunanta ta amsa cikin rawar murya. "Na am"
"Mene ne ainihin gaskiya."
Kuka kawai ta fashe da shi, wanda yazo mata da karfinsa na gaske kuma ba ya bukatar a tsai da shi a yanzu.
"Ga ainihin gaskiya nan, tunda ba'a karya da maganar aure, shi Rj in tun da ba ta sonshi ba sai ya hakura ba, dama aishi Hidaya ce matarsa banda abinka."
Cewar momy kenan, yayin da zuciyar Rj take ta mugun tafarfasa jijiyoyin kansa sun fito rada rada, Daddy kuwa yayi shiru cikin nazari yayin da Nusrat kukanta yake kara karfi.
"Daddy zan gaya maka ainihin gaskiya"
Cewar Hibba da ta d'auke ganinta ga kowa illa Daddy da ta fuskanta, duk da ta tsorata da tsawar da Mommy ta daka mata hade da cewa ta fice ba da ita ake magana ba amman Daddy ya dakatar da ita da fadin yana jinta, tabbas za ta fadi gaskiya ko da kwa Momy za tayi gunduwa da naman jikinta.
"Yayarmu ba ta san maganar Ishaq ba Aunty Hidaya ce ta tsara komai, kuma Momy tayi mata gargadi akan ta amshi maganar auran Ishaq in don Aunty Hidaya ta samu Yaa Rj a hannu."
"Jeki abinki Hibba, Allah ya yi miki albarka."
"Amin Daddy."
Ta tashi ta fita tana kuma tsoron haduwarta da Mommy don sai huci take ta Hidaya kuwa me sauki ce.
"Tabbas Ridwan na so had'a auranka da Hidaya, don duk a tunanina kun jima da hada kanku ashe ba haka abun yake ba, da Hidaya da Nusrat duk daya na daukesu a gurina, idan naki Nusrat tamkar naki Hidaya ne, don haka zanje na nema maka auran Nusrat insha Allah, kuma ba zaa ja lokaci ba kamar yadda kake so."
"Amman banji dadi ba, meyasa Daddy tun tuni ba ka sanar da ni wannan kudirin naka ba?"
"Saboda ba na son ku tirsasa zuciyoyinku yin abinda bashi take so ba, don haka kada kasa komai a ranka, duk sona duk kaunata na ganinku inuwa daya da Hidaya idan Allah bai so ba hakan bazai taba faruwa ba."
Yana kawowa nan ya kalli Hidaya yace .
"Sai ki warware auren da kika so kullawa, don wallahi muddun suka zo gobe to ke zan basu, kuma daga yau kisa a ranki ita soyayya ba'a kwacenta ta dole Allah ne yake dasawa bayinsa ba tare da saninsu ba, da kin mikawa Allah lamuranki kina iya samunsa ta cikin sanyi ba tare da kinsha wahala ba idan har mijinki ne a rubuce bazai taba gogewa ba."
Yana kawowa nan ya tashi zai shige bedroom don wani irin zafin Momy yake ji, saboda irin turbar da ta dora 'yarsa akai, Nusrar da kukanta ya fara yin k'asa ta kirashi.
"Daddy"
Tsayawa yayi yana jiran jin abinda za tace.
"Daddy na hak'ura da Yaa Rj na barwa Hidaya, wallahi ban san da maganar aure tsakaninsu ba, kuma ban san tana sonshi ba duk da ban bude zuciyata gareshi ba, Daddy ni me iya sadaukar da komai ce ga Hidaya muddun hakan zai sama mata kwanciyar hankali."
Gaba daya ya juyo ta zubawa fuskarta idanu, yana kuma jinta cikin ransa, kafin yace.
"Ke da ake so, kinji zaki iya sadaukar mata da shi, amman ita da ita take so ta kasa sadaukar miki sai ma k'okarin cusaki wani guri da take, Hidaya wannan nuni ne gareki, yadda Nusrat ta daukeki ba haka kika dauketa ba, Allah yayi miki albarka Nusrat, tabbas kin samu kyakkyawar tarbiya, amman ina so ki sani aure da ke da Ridwan sai dai in babu shi a rubuce."
Yana kawowa nan yayi shigewarsa d'aki.
。。。。。。
Daddy yaje ya nemawa RJ auran Nusrat gurin Baffa Shamsu, ya kuma bashi babu jaa don duk abin na gida ne, a take ya bada kud'in aure suka tsayar da rana bayan sallah babba.
Rj gaba d'aya ya kasa gane kan Nusrat don duk ta sauya, kullum cikin kunci da damuwa zaka sameta da yayi magana za tace ita wallahi ta hakura ta barwa Hidaya shi, shi kuma ransa yakan baci da jin kalaminta sai yaga kamar dama can ba son nashi take ba, ita kuwa tsoron abinda zai biyo baya take yi, don yanzu Mommy ko gaisuwarta ba ta amsa haka Hidaya ko kallon inda take ba tayi, duk da nasihar da Daddy ya zaunar da ita yayi mata duk a banza, tana tsoron yadda wannan aure zai tafi ya raba zumunci tun kan a daura shi.
Tsakanin Momy da Daddy kuwa babu wani shiri, don tayi mugun shaka da yace Nusrat ta samu tarbiya yana nufin ita ba ta bawa nata yayan tarbiya ba kenan, shiyasa da ya watsar da ita itma ta watsar da shi don tana shirin yadda za ta watsa rayuwar Nusrat ne kawai don diyarta ta samu abinda ta ke so don har ciwo Hidayan ta kwanta bayan ankai kudin Nusrat in.