Sashe 42
Katanga Complete Hausa Novel · about 8 min read
K'irjinta yana wani irin bugawa ta karb'i wayar cikin sanyin muryarta tace.
"Salamu Alaikum"
Jin muryar Nusrat ya sanya Ishaq cikin wani matsanancin dad'i, yau shi Nusrat ta kira akan k'ashin kanta, tabbas dole yau yayiwa Allah godiya da yasa ya fara samun matsayi gurin Nusrat in,muryarsa cike da zallar farin ciki yace.
"Wa'alaiki salamu da My Nuss, da fatan dai kina cikin k'oshin lafiya?"
Wayar ta ciro daga kunnenta ta kalla kafin ta d'aga kai ta kalli Rj da ya mik'e tsaye cikin matsanancin b'acin ran da ya kasa b'oyuwa akan kamilalliyar fuskarsa, zuciyarsa wani irin tuk'uk'i take masa mai zafi ya bud'e k'ofar ya fice, Hidaya ta bi bayansa d'auke da b'oyayyen murmushi....
[4/26, 8:45 PM] Rabi: BEBE'ARTH
KTG28
Da sassarfa ta had'a ta taddashi a farfajiyar tsakar gidan yana dosar inda sashensa yake saboda tsabar saurin da yake zubawa.
"Ai Yaa Rj Nusrat da Ishaq suna matuk'ar son junansu, kuma wallahi mutumin kirki ne sosai, yanzu haka ma maganar kawo kud..."
Ba ta k'arasa ba sakamakon wata muguwar tsawa da ya daka mata wacce ita tayi sanadiyar had'iye sauran maganar tata, da hannu ya nuna mata hanya yana jifanta da wani mugun kallo na tambayarki nayi, ko ni sa'anki ne, ina wasa da ke?
Sim sim ta shige idonta yana cikowa da k'walla yayin da shi kuma yaja tsuka yayi gaba zuciyarsa tayi bak'ik'k'irin, rigin gine ya kwanta a kan gado ya zubawa pop ido kamar yana karantar yadda aka zana shi yayi masifar kyau amman ba haka zancen yake ba, tunaninsa gaba d'aya yana kan Nusrat, bai jin zai iya jure rad'ad'in rasata ko kad'an, bai san so ko k'auna ba sai a kanta,a kanta zuciyarsa ta fara bud'ewa kuma yana jin akanta za ta rufe har abada, a komai nasa ita yake gani cikin idanuwansa kamanninta kuwa sun dad'e da mannewa cikin idanuwansa, yana mugun sonta, idan yace so yana nufin so na hak'ik'a wanda babu d'igon algus a ciki.
Bazan iya jure rashinki ba NUSRAT ki taimakeni ki gaya mini ba ki bud'ewa kowa zuciyarki ba sai ni don Allah na rok'eki ba don ni ba kar ki karya alk'awarin da nake murnar kin rik 'e mini shi.
Abinda yake sak'awa daga can k'asan zuciyarsa kenan yayin da wani b'ari na zuciyarsa yake jin kamar gaske ne maganar da Hidaya ta gaya mishi, tun da lokacin da yake saurarar jin ta bakinta shiru tayi masa alamu kenan na ta riga ta bud'ewa wani zuciyarta, kai ina ba haka bane tana dai da wani dalili nata.
Bayan fitarsa zubawa wayar ido tayi da Ishaq yake ta faman hello hello da ya gaji ya kashe wayar, rintse idanuwanta tayi tana jin yadda jijiyoyin kanta suke mik'ewa.
Innalillahi wa inna ilaihir rajiun shine abinda take ambata cikin ranta ko za ta ji zafi da rad'ad'in da zuciyarta take zai ragu, sai yanzu ta fuskanci dalilin da yasa Hidayan ta mik'o mata wayar saboda ta gane itace ta kira Ishaq d'in ba shi ya kirata ba, tayi hakanne don ta b'ata tsakaninta da Rj yayi mata kallon me karya alk'awari tun da ta gaya mata shine wanda ta yiwa alkawari, sam ba ta d'au Ishaq a matsayin saurayi ba sai dai tana bashi girma saboda yadda yake hak'uri da ita da bata kulawa duk da shi yaga zai iya hakan, to hakanne yasata karb'ar wayar tunda ba ta san me zaice mata ba may be kuma ya kira wayarta yaji ta a kashe don da ta gama game in kasheta tayi gaba d'aya, ba tayi tunanin wayar a speaker take ba da kuma Rj in bai san tsakaninta da Ishaq ba, amman za tayi k'ok'arin fahimtar da shi kada yayi mata kallon me karya alk'awari.
Da wannan abin da Hidaya take gara tazo ta tareta suyi me yuyuwa yafi, amman tunda haka ta zab'a to itama za ta zuba mata idanuwa taga inda wasan nata zai tsaya, ita dai baza taki amsar soyayyar Rj ba saboda dama ita take jira don ta tura shirmen mafarkinta gefe, sai dai tana tsoron inda makomarsu za ta tsaya saboda ga Momy ga Hidaya a gefe, don ta tabbata Momy ba za ta bar 'yarta ta zab'eta ba amman ko ma dai meye Allah ba ya bacci, idan har Rj mijinta ne zai kawo musu hanya mafi sauk'i.
Washe gari ko break bai tsaya yayi ba ya d'auki hanyar kaduna dama al raedy Daddy da Mommy sun san da tafiyar tasa, Hajiya, (Haka suke kiran mahaifiyar tasu da k'annensa mata guda biyu da ta haifa a kadunan, suma dukkaninsu sunyi aure ko wacce tana da yara bibbiyu) tayi matuk'ar farin cikin ganin d'an nata, hakama k'annen nasa Safiya da Hafsa ko wacce tazo don ganin d'an uwan nasu don sun san halinsa na son girma da manyance sai yace bazai je musu ba duk da zolayar da suke masa yanzu na sun girmeshi dole ya basu girman saboda sun rigashi dire 'ya'ya.
Bai baro kaduna ba sai cike da tarin k'aunar mahifiyarsa da 'yan uwansa sai dai zuciyarsa cike take da tashin hankalin abinda yaji daga bakin Hajiyarsu wanda ko da wai bai tab'a hasasho hakan ba, ta sanar mishi ne akan maganar Aurensa shi da Hidaya nan da shekara d'aya idan Hidayan ta kammala karatunta, duk da ita Hajiyan ta so yana dawowa yayi aure sai dai sunyi maganar da Daddy inda yake ce mata so yake Hidayan ta kammala karatunta shekara me zuwa ya had'asu aure don yaga alamun ma sun dai daita kansu, farin ciki sosai Hajiyan ta shiga don Daddy mutum ne ba abun yadarwa ba, had'a zuri'a da shi kuwa babban rabo ne, kasa rik'e farin cikin nata tayi shiyasa da Rj in yazo tayi masa zancen, ganin tarin farin cikin da mahaifiyar tasa take ciki ne yaga bazai iya katse mata shi ba kawai yabita akan hakane, amman fa zuciyarsa gaba d'aya a cunkushe take tunaninsa ya katse ya rasa wani irin tunani zaiyi.
Yana doso hancin motarsa harabar gidan idonsa ya sauka akan Nusrat da Ishaq suna tsaye da alamu sallama suke zai tafi don a jikin motarsa suke a tsayen, hankalinsa ne ya kasa kwanciya da yai ta kiran wayar ba'a peking, Hidaya da ta shigo taga tarin miss call insa sai tayi masa tex akan yazo gobe tana son ganinsa a zuwan Nusrat ce ta tura masa shi kuwa Ishaq ganin wannan tex in sai ya kwantar masa da hankali ya kuma tsundumashi cikin farin ciki don ya fara ganin alamun nasara daga Nusrat in, kuma dama yana son zuwa ya ganta don ya kwana biyu bai zo ba gashi zaiyi tafiyar da bai san kwanaki nawa za ta ibeshi ba.
Nusrat kuwa tana tsaka da had'a dinner ya kirata gashi ya k'araso, ta shiga d'inbin mamaki don ba suyi da shi zaizo d'in ba to amman sai taji ba za ta iya wulakanta shi ba tun da har ya riga yazo, Allah ya taimaketa ta kusa gamawa sai ta k'arasa a gaggauce ta bar Hibba da jerawa akan dinning, dama a shiryanta take cikin bak'ar doguwar riga da ta kuma fito da hasken fatarta, turare kawai ta kuma fesawa ta d'auki siririn jan mayafi ta yafa ta fita fuskarta na bada wani annurin kyahu.
Sun d'an tab'a hira ba laifi aka fara kiran sallar magariba ya tashi zai tafi shine ta yo mishi rakiya bakin motarsa.
Wani irin duhu Rj ya fara gani cikin idanuwansa yana jin wata sabuwar damuwar na kuma ninkaya cikin zuciyarsa, ko parking bai dai daita sosai ba ya fito yana rik'e kansa da ke mugun sara masa a hankali yake tafiya ya nufi sashensa, Nusrat kuwa hankalinta gaba d'aya yana kansa har Ishaq ya shiga motarsa ya ja ya tafi da sassarfa tabi bayansa tana kiran sunansa amman ko nuna alamun yaji bai yi ba da gudu ta had'a tasha gabansa tana d'an haki na gudun da tayi, d'ago da rinannun idanuwansa yayi ya aza a kan kyakkyawar fuskarta, kallon cikin ido sukewa juna, a hankula yaji zuciyarsa tana sanyi duk wata damuwa tana kwaranyewa saboda abinda yake karanta cikin idanuwanta, zare idonta tayi daga cikin nasa saboda yadda taji kuzarinta yana karkaryewa had'e da karsashinta, zoben da ya saka mata ta murza ta d'ago da hannun ta nuna masa had'e da fad'in.
"Ka saka nayi maka alk'awari ba tare da ina da tabbacin sona kake ba, haka nayi k'ok'arin cika maka shi tare da jure dukkan wani k'unci, saboda rashin cika alk'awari alamace ta munafiki, amman sai gashi da rashin fahimta za ka saka mini, Ishaq ba saurayina bane, ya dai nuna yana sona ban amince masa ba na gaya mishi da alkawarin wani a kaina, sai ya buk'aci yin abota da ni naso k'in amincewa amman ya kafa mini naci na barshi a zuwan idan ka dawo mayi rabuwar mutumci da shi saboda ba ka san halin mutum ba.
Akan ka zuciyata ta bud'e, kaine ka fara shiga cikinta ka samu babban masauki ina fatan kuma akanka za ta rufe idan ka bata damar hakan."
Tana kawowa nan ta juya za ta tafi.
"Nusrat"
Ya kira sunanta, d'an dakatawa tayi ba tare da ta juyo ba.
"Kiyi hak'uri don Allah."
"Laifi indai naka ne ba ya zama a zuciyar Nusrat, musamman wannan da rashin fahimta ne kawai, har an tayar da sallah bara na k'arasa ciki."
Wani kyakkyawan murmushi ya saki yana bin bayanta da kallo da ta wuce ba ta jirayi me zaice ba, ina sonki Nusrat yaji zuciyarsa ta ambaci hakan kafin ya shafa kansa ya nufi sashensa cike da karsashi da sabon kuzari, don duk sai yaji wata damuwa tasa ta yaye kawai zai tunkari Daddy da maganar yana son Nusrat tun kafin ya tunkareshi da maganar Hidaya don bazai iya kaucewa hakan ba saboda matsayi da kimar Daddyn a gurinsa, ita kuma Hajiya ya san ta yadda zai b'illo mata.....
[4/26, 8:45 PM] Rabi: BEBE'ARTH
KTG29
"Salamu Alaikum"
Jin muryar Nusrat ya sanya Ishaq cikin wani matsanancin dad'i, yau shi Nusrat ta kira akan k'ashin kanta, tabbas dole yau yayiwa Allah godiya da yasa ya fara samun matsayi gurin Nusrat in,muryarsa cike da zallar farin ciki yace.
"Wa'alaiki salamu da My Nuss, da fatan dai kina cikin k'oshin lafiya?"
Wayar ta ciro daga kunnenta ta kalla kafin ta d'aga kai ta kalli Rj da ya mik'e tsaye cikin matsanancin b'acin ran da ya kasa b'oyuwa akan kamilalliyar fuskarsa, zuciyarsa wani irin tuk'uk'i take masa mai zafi ya bud'e k'ofar ya fice, Hidaya ta bi bayansa d'auke da b'oyayyen murmushi....
[4/26, 8:45 PM] Rabi: BEBE'ARTH
KTG28
Da sassarfa ta had'a ta taddashi a farfajiyar tsakar gidan yana dosar inda sashensa yake saboda tsabar saurin da yake zubawa.
"Ai Yaa Rj Nusrat da Ishaq suna matuk'ar son junansu, kuma wallahi mutumin kirki ne sosai, yanzu haka ma maganar kawo kud..."
Ba ta k'arasa ba sakamakon wata muguwar tsawa da ya daka mata wacce ita tayi sanadiyar had'iye sauran maganar tata, da hannu ya nuna mata hanya yana jifanta da wani mugun kallo na tambayarki nayi, ko ni sa'anki ne, ina wasa da ke?
Sim sim ta shige idonta yana cikowa da k'walla yayin da shi kuma yaja tsuka yayi gaba zuciyarsa tayi bak'ik'k'irin, rigin gine ya kwanta a kan gado ya zubawa pop ido kamar yana karantar yadda aka zana shi yayi masifar kyau amman ba haka zancen yake ba, tunaninsa gaba d'aya yana kan Nusrat, bai jin zai iya jure rad'ad'in rasata ko kad'an, bai san so ko k'auna ba sai a kanta,a kanta zuciyarsa ta fara bud'ewa kuma yana jin akanta za ta rufe har abada, a komai nasa ita yake gani cikin idanuwansa kamanninta kuwa sun dad'e da mannewa cikin idanuwansa, yana mugun sonta, idan yace so yana nufin so na hak'ik'a wanda babu d'igon algus a ciki.
Bazan iya jure rashinki ba NUSRAT ki taimakeni ki gaya mini ba ki bud'ewa kowa zuciyarki ba sai ni don Allah na rok'eki ba don ni ba kar ki karya alk'awarin da nake murnar kin rik 'e mini shi.
Abinda yake sak'awa daga can k'asan zuciyarsa kenan yayin da wani b'ari na zuciyarsa yake jin kamar gaske ne maganar da Hidaya ta gaya mishi, tun da lokacin da yake saurarar jin ta bakinta shiru tayi masa alamu kenan na ta riga ta bud'ewa wani zuciyarta, kai ina ba haka bane tana dai da wani dalili nata.
Bayan fitarsa zubawa wayar ido tayi da Ishaq yake ta faman hello hello da ya gaji ya kashe wayar, rintse idanuwanta tayi tana jin yadda jijiyoyin kanta suke mik'ewa.
Innalillahi wa inna ilaihir rajiun shine abinda take ambata cikin ranta ko za ta ji zafi da rad'ad'in da zuciyarta take zai ragu, sai yanzu ta fuskanci dalilin da yasa Hidayan ta mik'o mata wayar saboda ta gane itace ta kira Ishaq d'in ba shi ya kirata ba, tayi hakanne don ta b'ata tsakaninta da Rj yayi mata kallon me karya alk'awari tun da ta gaya mata shine wanda ta yiwa alkawari, sam ba ta d'au Ishaq a matsayin saurayi ba sai dai tana bashi girma saboda yadda yake hak'uri da ita da bata kulawa duk da shi yaga zai iya hakan, to hakanne yasata karb'ar wayar tunda ba ta san me zaice mata ba may be kuma ya kira wayarta yaji ta a kashe don da ta gama game in kasheta tayi gaba d'aya, ba tayi tunanin wayar a speaker take ba da kuma Rj in bai san tsakaninta da Ishaq ba, amman za tayi k'ok'arin fahimtar da shi kada yayi mata kallon me karya alk'awari.
Da wannan abin da Hidaya take gara tazo ta tareta suyi me yuyuwa yafi, amman tunda haka ta zab'a to itama za ta zuba mata idanuwa taga inda wasan nata zai tsaya, ita dai baza taki amsar soyayyar Rj ba saboda dama ita take jira don ta tura shirmen mafarkinta gefe, sai dai tana tsoron inda makomarsu za ta tsaya saboda ga Momy ga Hidaya a gefe, don ta tabbata Momy ba za ta bar 'yarta ta zab'eta ba amman ko ma dai meye Allah ba ya bacci, idan har Rj mijinta ne zai kawo musu hanya mafi sauk'i.
Washe gari ko break bai tsaya yayi ba ya d'auki hanyar kaduna dama al raedy Daddy da Mommy sun san da tafiyar tasa, Hajiya, (Haka suke kiran mahaifiyar tasu da k'annensa mata guda biyu da ta haifa a kadunan, suma dukkaninsu sunyi aure ko wacce tana da yara bibbiyu) tayi matuk'ar farin cikin ganin d'an nata, hakama k'annen nasa Safiya da Hafsa ko wacce tazo don ganin d'an uwan nasu don sun san halinsa na son girma da manyance sai yace bazai je musu ba duk da zolayar da suke masa yanzu na sun girmeshi dole ya basu girman saboda sun rigashi dire 'ya'ya.
Bai baro kaduna ba sai cike da tarin k'aunar mahifiyarsa da 'yan uwansa sai dai zuciyarsa cike take da tashin hankalin abinda yaji daga bakin Hajiyarsu wanda ko da wai bai tab'a hasasho hakan ba, ta sanar mishi ne akan maganar Aurensa shi da Hidaya nan da shekara d'aya idan Hidayan ta kammala karatunta, duk da ita Hajiyan ta so yana dawowa yayi aure sai dai sunyi maganar da Daddy inda yake ce mata so yake Hidayan ta kammala karatunta shekara me zuwa ya had'asu aure don yaga alamun ma sun dai daita kansu, farin ciki sosai Hajiyan ta shiga don Daddy mutum ne ba abun yadarwa ba, had'a zuri'a da shi kuwa babban rabo ne, kasa rik'e farin cikin nata tayi shiyasa da Rj in yazo tayi masa zancen, ganin tarin farin cikin da mahaifiyar tasa take ciki ne yaga bazai iya katse mata shi ba kawai yabita akan hakane, amman fa zuciyarsa gaba d'aya a cunkushe take tunaninsa ya katse ya rasa wani irin tunani zaiyi.
Yana doso hancin motarsa harabar gidan idonsa ya sauka akan Nusrat da Ishaq suna tsaye da alamu sallama suke zai tafi don a jikin motarsa suke a tsayen, hankalinsa ne ya kasa kwanciya da yai ta kiran wayar ba'a peking, Hidaya da ta shigo taga tarin miss call insa sai tayi masa tex akan yazo gobe tana son ganinsa a zuwan Nusrat ce ta tura masa shi kuwa Ishaq ganin wannan tex in sai ya kwantar masa da hankali ya kuma tsundumashi cikin farin ciki don ya fara ganin alamun nasara daga Nusrat in, kuma dama yana son zuwa ya ganta don ya kwana biyu bai zo ba gashi zaiyi tafiyar da bai san kwanaki nawa za ta ibeshi ba.
Nusrat kuwa tana tsaka da had'a dinner ya kirata gashi ya k'araso, ta shiga d'inbin mamaki don ba suyi da shi zaizo d'in ba to amman sai taji ba za ta iya wulakanta shi ba tun da har ya riga yazo, Allah ya taimaketa ta kusa gamawa sai ta k'arasa a gaggauce ta bar Hibba da jerawa akan dinning, dama a shiryanta take cikin bak'ar doguwar riga da ta kuma fito da hasken fatarta, turare kawai ta kuma fesawa ta d'auki siririn jan mayafi ta yafa ta fita fuskarta na bada wani annurin kyahu.
Sun d'an tab'a hira ba laifi aka fara kiran sallar magariba ya tashi zai tafi shine ta yo mishi rakiya bakin motarsa.
Wani irin duhu Rj ya fara gani cikin idanuwansa yana jin wata sabuwar damuwar na kuma ninkaya cikin zuciyarsa, ko parking bai dai daita sosai ba ya fito yana rik'e kansa da ke mugun sara masa a hankali yake tafiya ya nufi sashensa, Nusrat kuwa hankalinta gaba d'aya yana kansa har Ishaq ya shiga motarsa ya ja ya tafi da sassarfa tabi bayansa tana kiran sunansa amman ko nuna alamun yaji bai yi ba da gudu ta had'a tasha gabansa tana d'an haki na gudun da tayi, d'ago da rinannun idanuwansa yayi ya aza a kan kyakkyawar fuskarta, kallon cikin ido sukewa juna, a hankula yaji zuciyarsa tana sanyi duk wata damuwa tana kwaranyewa saboda abinda yake karanta cikin idanuwanta, zare idonta tayi daga cikin nasa saboda yadda taji kuzarinta yana karkaryewa had'e da karsashinta, zoben da ya saka mata ta murza ta d'ago da hannun ta nuna masa had'e da fad'in.
"Ka saka nayi maka alk'awari ba tare da ina da tabbacin sona kake ba, haka nayi k'ok'arin cika maka shi tare da jure dukkan wani k'unci, saboda rashin cika alk'awari alamace ta munafiki, amman sai gashi da rashin fahimta za ka saka mini, Ishaq ba saurayina bane, ya dai nuna yana sona ban amince masa ba na gaya mishi da alkawarin wani a kaina, sai ya buk'aci yin abota da ni naso k'in amincewa amman ya kafa mini naci na barshi a zuwan idan ka dawo mayi rabuwar mutumci da shi saboda ba ka san halin mutum ba.
Akan ka zuciyata ta bud'e, kaine ka fara shiga cikinta ka samu babban masauki ina fatan kuma akanka za ta rufe idan ka bata damar hakan."
Tana kawowa nan ta juya za ta tafi.
"Nusrat"
Ya kira sunanta, d'an dakatawa tayi ba tare da ta juyo ba.
"Kiyi hak'uri don Allah."
"Laifi indai naka ne ba ya zama a zuciyar Nusrat, musamman wannan da rashin fahimta ne kawai, har an tayar da sallah bara na k'arasa ciki."
Wani kyakkyawan murmushi ya saki yana bin bayanta da kallo da ta wuce ba ta jirayi me zaice ba, ina sonki Nusrat yaji zuciyarsa ta ambaci hakan kafin ya shafa kansa ya nufi sashensa cike da karsashi da sabon kuzari, don duk sai yaji wata damuwa tasa ta yaye kawai zai tunkari Daddy da maganar yana son Nusrat tun kafin ya tunkareshi da maganar Hidaya don bazai iya kaucewa hakan ba saboda matsayi da kimar Daddyn a gurinsa, ita kuma Hajiya ya san ta yadda zai b'illo mata.....
[4/26, 8:45 PM] Rabi: BEBE'ARTH
KTG29