← Book details Katanga Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 40 OF 69

Sashe 40

Katanga Complete Hausa Novel · about 8 min read

Itace da kanta taje ta taho da Nusrat in, daga bakin k'ofa ta tsaya tayi mata nuni da ta shiga ita kuma ta juya.
Ta d'an jima sosai a bakin k'ofar kamar ta shiga kamar ba ta shiga ba, ta b'angaran Ishaq kuwa yaji tsaiwar mutum a bakin k'ofa da sabon k'amshin turaran da ya ziyarci hancinsa amman shiru yaji ba'a shigo ba, a hankali ya mik'e ya nufi bakin k'ofar, yana d'aga labulen itama ta d'aga kenan za ta shigo idanuwansu ya sark'e guri d'aya, d'an ja baya tayi a ranta tana yaba tsarin kyahunsa duk da bai kai Yaa Rj ba da wannan me kyahun da sukai karo har sau biyu a asibiti ba, mtsss taja tsaki a ranta ko meye na tuno shi kuma?

Ja da baya yayi har lokacin idonsa bai bar kanta ba, yana jin yadda k'auna da soyayyarta ke karya kuzarinsa.

"Bismillah zo ki shige."
Ya fad'a yana me nuna mata hanyar da hannunsa, babu musu ta shige a sanyaye don idanuwansa sun fara kashe k'arfinta da ta fito da shi, bayan sun zauna gaba d'aya k'asa tayi da kanta tana mai gaisheshi cikin muryarta da ta k'ara yin sanyi wacce shi kuma ta k'ara sanyashi mutuwa sosai cikin k'aunarta, bayan sun gaisa babu kwane kwane ya zayyana mata abinda ke tafe da shi wanda itama ba tayi nauyin bakin sanar da shi akwai alkawarin wani a kanta ba inda shi kuma ya nuna mata buk'atarsa ta yin abotaka tunda ba ta amshi soyayyarsa ba, ita kwa tace sam babu abotaka tsakanin mace da namiji baza ta amsa ba, da k'yar dai ya shawo kanta akan in ya kira waya zata amsa ko ba ko yaushe ba, kuma in ya bukaci ganinta za ta amince ko da a wata sau d'aya ne ba ta amince masa ba sai da sukai alk'awarin bazai dinga kashe mata kud'i ba kafin daga bisani sukai sallama ya bata rafar 'yan dubu akan ta baiwa Hidaya, taso k'in amasa ta kuma nuna mishi zai fara karya alkawarinsu tun yanzu yace ai ba ita ya bawa ba Hidaya ya bawa.

A haka rayuwa take juyawa tana tafiya, shekara ta zama tamkar wata, wata tamkar sati, sati tamkar kwana aya, kwana aya, kwana aya tamkar huni, anyi azumin watan ramadana cikin hukuncin Ubangiji, wanda suka dinga iban garar girkuna kala kala gurin Nusrat, don har searching in girkuna ta dunga yowa a wayar Hidaya,don ita kanta girkinma yana sanyata nishad'i kuma tasan kanta take taimaka don ta tabbata duk mijin da ya aureta to tabbas sai yayi alfahari da ita indai a b'angaran girki ne.
Sam ba tayi wasa gurin ibada ba, ta mayar da hankali sosai tana rok'awa iyayanta rahama gurin Ubangiji, su kuma da kyakkyawar rayuwa a garesu tare da miji na gari, da kuma dawo da KATANGAR kaunar dake tsakaninsu da Shukhura.

Har yanzu bata da waya babba, Daddy ne yaso siya mata amman Momy tace masa Nusrat in ba ta da ra'ayin rik'e babar waya gara ya siya mata k'arama, don ta sanshi mak'udan kudi zai saka ya siya mata wayar musamman yadda yake kwasar girkunanta masu dad'i, to shine ya siya mata waya 'yar k'arama me kyau me kuma tsada, dama tana da sim inta a ajiye ta d'auko ta d'orashi akai.
Kud'in kayan sallah ma da ya tashi bayarwa kai d'aya duk ya bayar har Nusrat don sosai yake jinta a ransa kamar 'yar da ya haifa, amman Momy sai da ta zaftare rabi a na Nusrat in, amman duk da haka Nusrat in ba iya kanta tayiwa siyayyar sallar ba har da Yusra, ta kuma siyawa yarinyar da Aunty Hafsa ta haifa me suna Nuru kaya set biyar masu matuk'ar kyau da tsada duk a cikin kud'in nata amman Hidaya ce ta k'ara mata kud'in wanda itama Ishaq ne ya bata yace ta san yadda za tayi ta bawa Nusrat in ba tare da ta san shine ya bata ba.

Uku ga sallah suka d'unguma sukai zariya, farin ciki duk ya cika zuciyar Nusrat burinta kawai ta isa mahaifarta ta ganta gata ga Yusranta, cikin Umma da Iya babu wanda yake ta ita, ko kuma ya nuna murnar canjawarta, don ba k'arya ta goge ta k'ara kyau musamman da take amfani da mayuka da aabulu da shower gel in da Hidaya ta siyo mata, sosai fatarta ta kuma gogewa kyahunta ya kuma baytana a fili, to duk bak'inci suka nuna mata a fili da habaicin da suka saba suna fad'in duk kwad'ayinta dai baza ta samu miji tamkar ya na Shukhura ba, babu wanda ta tankawa kamar ko yaushe ta janye jikinta ta nufi d'akinsu ta bud'e ta shiga da kayanta da na su Yusra da ta siyo musu.

D'akin ta gyara komai yayi nead, kana ta nemi guri ta zauna, tana jin b'acin ran da su Iya suka sanyata yana damunta duk kwa k'ok'arinta na ganin ta kawar da shi ta yakice shi daga ranta, kallon d'akin nasu take sosai tana tuna rayuwarsu a ciki kamar yanzu komai yake faruwa cikin kwanyarta, rayuwa kenan, number Yusra ta lalibo ta danna mata kira saboda in ba haka ba kuka za tayi wanda kuma kukan bazai shafa mata lafiya ba.

Wani wawan ihu Yusra ta saki yayin da Nusrat ta sanar mata tana cikin garin zariya.
"Gani nan gani nan Yayarmu"
Shine abinda take fad'i cikin zallar d'auki da farin ciki, katseta Nusrat in tayi akan ta bari gobe za tazo, k'in yadda tayi da k'yar ta lallasheta kana ta hak'ura, suna gama wayar, wayar Ishaq ta shigo mata don yaji ya suka isa zariyar.

Washe gari tun da safe ta shirya ta yiwa Momy sallama akan ta tafi unguwar fulani, acan Uncle Iliyan yake a zaune, Hidaya taso yi mata rakiya amman ciwon kai take fama da shi don haka kawai tace ta gaishesu, yayin da suka tafi da Hibba da tace zata bita don itama tana son ganin Yusran.

Tunda Nusrat ta sanar da Yusran suna hanya Yusra ta kasa tsaye ta kasa zaune, tana jin sallamarsu da gudu taje ta d'afe Nusrat in suka ruk'un kume juna cikin murna da farin ciki, yayin da Hibba ta tsaya tana ganin ikon Allah tana jin a ranta inama suma irin hakanne ke wakana tsakaninsu da Hidaya, duk laifin Momynsu ne da ta gina musu irin Katangar da Mamansu Yusran ta gina musu da yanzu hakan bazai bata sha'awa ba.

A yau dai farin cikin Yusra da Nusrat bazai rubutu ba masu karatu ku hasasho kawai, musamman da taga irin siyayyar da Yayar tasun ta jibgo mata, duk da yanzu Alhmdlillh duk wani abin buk'ata Auncle Iliya yana iya bakin k'ok'arinsa ba k'aramar murna tayi ba ta dinga jero mata addua tare da iyayansu da suka rasa.
Aunty Hafsa ma tayi murna ga kuma kayan da ta bayar a sakawa Nuru, godiya ta dungai mata, tana k'ara ganin girma da kimar Nusrat in tare da jinjinawa mahaifiyarsu da yi mata adduar dacewa.

Ko da suka tashi tafiya Yusra had'o kayanta tayi akan za ta bisu, in yaso in suka tafi ta dawo, amman Nusrat ta hanata, duk da k'asan ranta tana son kasancewa da k'anwar tata, kuka sosai Yusran ta samu guri tana yi kamar k'aramar yarinya,ganin haka yasa Aunty Hafsa ta d'au waya ta kira Auncle Iliya ta sanar masa abinda ke faruwa kawai yace suje din in sun tafi ta dawo.

Tsalle da murna Yusran ta hau yi yayin da Aunty Hafsan ta gaya musu abinda Auncle Iliyan yace.

Satinsu d'aya da zuwa zariya Shukhura ma suka zo, tazo gidan da sha tara ta arzik'inta wanda Umma ta dinga yadarwa da su Nusrat in magana, Yusra taso tankawa Nusrat in ta hanata, huni ranar Shukhura tayi a gidan amman ba ta neme su ba suma basu nuna sun san da zuwanta ba, Nimha kuwa da tazo har d'akin da suke ta shigo suka gaisa, don haka suma suka saka rana suka je gidanta har da su Hidaya suka huni sur a can, don su Nimha anyi kud'i ana ta fantamawa.

Satinsu biyu cur a zariya suka tarkata nasu ya nasu suka tafi, Yusra da Nusrat suna ta kewar juna, don sati biyunnan da sukayi tare ya tayar musu da tsimin abubuwa masu yawa, har ba taso tafiyarsu ba tayi tunanin wata guda zasui, duk da yanzunma Momy tace Daddy ne yace su dawo saboda Rj jibi zai dawo kar ya dawo gidan ba kowa, duk da tasan Daddynma a matse yake da su dawo don ya gaji da kame kamen abinda yake ci·....

Juma'a asabar lahadi zaku jini shiru·
[4/26, 8:44 PM] Rabi: BEBE'ARTH

KTG 26

Ana ya gobe Rj zai dawo Hidaya ta tsame jikinta ta tafi saloon akai mata gyaran jiki da na kai, Nusrat kallonta kawai take yadda take ta rawar kan dawowar Rj in, hatta kayan da zata saka sababbi ne ta siyo su, zuciyarta ta fara zargin anya Hidaya da Rj in ba soyayya suke ba ya ninketa a bai bai yasa ta mishi alk'awari amman ko ma dai meye za ta zuba ido taga dawowarsa da wani taku zaiyi, idan kwa ya tabbata Hidaya son RJ take to tabbas zata haramtawa kanta shi tun kafin a haramta mata zuciyarta ta samu matsala.

Biyar da rabi na yamma Hidaya da Daddy suka tafi filin jirgi taro Rj saboda yace shida dai dai jirginsu zai sauka, shidan kwa a filin jirgin tayi musu hakan yayi dai dai da isowar jirgin nasu, idanuwa waje Hidaya ta zuba tana jiran saukowar annurin zuciyarta.

Murmushi kwance akan kamilalliyar fuskarsa ya fara saukowa daga jirgin yana wurga idanuwansa ra inda zai hango Daddy, idanuwansa akan Hidaya suka sauka wanda itama nata idanuwan akansa suke zuciyarta tana wani irin bugawa had'e da yamutsawa da zallar soyayyar yayan nata, murmushi ya sakar mata wanda ya kuma matar da ita a zallar k'aunarsa kafin ta sakar masa nata murmushin shi kuma a lokacin ya d'auke idonsa daga kanta ya mayar kan Daddy da ke gefenta suka sakarwa juna murmushi kafin ya nufo gurin da suke a tsaye.
Chapter 40 · 0% Book details