Sashe 57
Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ko a gidan karuwai kike rayuwa Amatullah zan iya aurenki. Balle kuma ke É—in Æ´ar uwata ce ta jini. Sai dai ba zan yi miki dole ba don yanzu farin cikinki shi ne abin da na fi so don haka ki je ki yi tunani da zuciyarki".
Na sunkuyar da kaina ƙasa kafin na ce"Anty Sawwama ta san da wannan zancen?".
"Sai da na fara tinkarar ta da maganar kafin na zo wajen ki". Na sauƙe tagwayen ajiyan zuciya ban iya cewa wani abun har ya tashi ya fita daga cikin ɗakin, ji nake yi kaina yana juya tamkar ba a cikin duniyar nake ba ga wani jirin da yake ɗeba ta don da kasancewar a zaune nake. Na koma na kwanta hawaye suna tsiyaya ta gefe da gefen idona.
Tabbas Yaya Alhassan mutumin kirki ne mai ƙoƙarin kame mutuncin kansa da kuma na ahalinsa a ko da yaushe, mutum ne mai nutsuwa da sanin ya kamata me yasa Anty Sawwama za ta amince masa akan auran watsatstsiyar da ta yi cikin shege ta kunyatar da iyayenta da duk wani wanda ya yarda da ita a idon duniya. Hatta mahaifiyarta ta nuna rashin buƙatata a kusa sai ita ce za ta buƙaci ɗanta ya kasance a tare da ni?.
Na sauƙe tagwayen ajiyan zuciya ina gyara kwanciyata, ba zan zama silar rugujewar rayuwar Yaya Alhassan ba. Don haka na gwammace na tafi can wani wajen da ban san kowa ba ni ma ba sanni ba na je na yi rayuwata. Ko zan sama kwanciyar hankalin da na rasa a yanzu. Gwara na shiga duniya kamar yadda Umma ta yi ikirarin ta sallama ni gare ta.
[10/30, 4:03 PM] Maimunatu Iyam🥰: *DAFIN HARSHE*
Â©ï¸ Maimuna Tijjani Iyam
______________________________________
Page 4ï¸âƒ£0ï¸âƒ£
Haka na kwana ina tunani da saƙa da warwara cikin raina, ganin bacci ya ƙi kawo mini ziyara hakan ya sani tashi na fito na ɗaura alawa na koma ciki na gabatar da salla raka'a biyu. Na ɗaga hannayena dukka biyu sama sai dai na kasa magana rawa kawai jikina yake yi. Na kifa kaina a bisa gwiyoyina ina rero kukan marar sauti. Ban runtsa ba har sai da aka yi ƙiran sallan asubahi Anty Sawwama ta shigo da nufin tashi ta iske ni zaune ta dalle mini idanuna da haske tocila.
"Lafiya na gan ki a zaune kamar ba ki runtsa ba?".
"Na runtsa kawai na tashi ne da na ji ƙiran salla". Ba ta ce da ni komai ba ta juya ta fita na bi bayan ta alwala na yi na zauna na buga tagumi a gaban botan har Yaya Alhassan, Amir da Umar suka fito domin tafiya masallaci.
"Amatullah lafiya kuka zauna kika zagba tagumi?". Na tsinkayo muryar Amir a tsakiyar kaina na yi figigi na dawo cikin hayyacina.
"Lafiya ƙalau ina kwananku". Suka haɗe baki wajen amsawa kana suka fita, na tashi na koma cikin ɗakin na shimfiɗa sallaya a zaune na yi sallan don ji nake yi tamkar ƙafafuna ba za su ɗauke ni ba tun ina raka'an farko nake kuka har na yi sallama na ɗaga hannayena dukka biyu zama ina kirari ga Ubangijina.
"Ya Allah kai mai ikon akan kowa da kuma komai. Ya Allah kai ne masanin sirrin dake taskace cikin tsokar zuciyar dake a ciki ƙirji, Allah ka kawo mini mafitan halin da nake ciki. Zan tafi na je can wani wajen da ba a sanni ba ni ma ban san kowa na je na ci gaba da rayuwa a can, don na fahimci zama a nan shi ma wani matsalan ne. Tun da har Umma ta furta ba ta buƙata ta ta sallamar da ni ga duniya zan tafi can wani wajen na je na yi rayuwata, ba zan zama matsala ga rayuwar wasu ba. Ya Allah ya dubi lamarina ka kawo mini komai da sauƙi ka ba ni ikon cinye wannan jarabawan da ya faɗa mini. Allah kai mai rahama ne Allah ya lulluɓe Abbana da rahamarka, Ya Allah kai mai gafara ne Allah ka gafarta masa".
Na shafa addu'ar cikin sanyi da mutuwar jiki wasu hawayen suna gangarowa daga idanuna, na ji ƙarar buɗe ƙofar hakan ya sa na yi saurin komawa na kwanta ba tare da na cire hijabin da na yi sallan ba. Aka shigo aka zauna kusa da ku dab har ina ji sautin ajiyan zuciya da take sauƙewa akai-akai.
Ta dafa goshina tana shafawa har zuwa kaina"Amatullahi Baiwar Allah ina son rayuwarki ta inganta ina don ganin ki cikin farin ciki. A yanzu ba ni da burin da ya wuce na gan nutsuwarki ya daidaita kin sama kwanciyan hankali da walwala ki yi rayuwa kamar kowa cikin sakewa wannan dalilin ya sa nake son Alhassan ya aure ki. Don hankalina ba zai kwanta ba matuƙar kika yi aure a wani wajen kika shiga cikin wasu dangin da wataƙila su goranta miki akan abin da ya faru da ke ko ma su wulaƙanta ki. Amatullah tun ranar da aka kawo mini gawar Manniru a gaba babu rai a tattare da shi na yi wa kaina alƙawarin ba zan taɓa barin abin da ya haifa ta wulaƙanta ba bayan ransa, zan yi tsayiwan tsayin daka wajen tabbatar da cewar rayuwarki ta inganta. Ina da yaƙinin ko bayan babu raina Alhassan ba zai taɓa bari ki wulaƙanta ba".
Ta ƙare zancen tare da gyara mini Kwanciyata ta ja hijabin ta lulluɓe mini ƙafafuna da shi, ta fita rufe ƙofan da ta yi ya yi daidai da bugawan da zuciyata ta yi tamkar za ta ɓalle allon ƙirjina ta fito waje ta daka rawan disko. Tausayin kaina da na ahalina ya mamaye mini ruhina hawaey suka jiƙa mini fuska lajab kaina ya sara ƙirjina ya ci gaba da tsananta bugu.
A bayyane na furta"Anty ki yafe mini wallahi ba zan iya zama ba. Gwara na fi can inda ba a sannin ba kuma ban san kowa ba sai na fi samun kwanciyar hankali". Na ƙarƙare zancen ina tashi na zauna daɓas na leƙa ta taga na ga har gari ya soma yin haske na buɗe ƙofar ɗakin har na saƙalo ƙafata waje na hango su Yaya Alhassan suna shigowa da alama sai yanzu suka dawowa daga masallaci na yi wuf na shanye ƙafata na tura ƙofar ina leƙan su, zuciyata ta harba ganin Yaya Alhassan ya nufo ɗakin yayin da Amir da Umar suka shige ɗakinsu. Ban san abin da ya tuna ba sai kuma na ga juya ta ya bi bayan su Amir, na sauƙe ɓoyayyan ajiyan zuciya ina dafe ƙirjina da yake bugu.
Sai da na ɓata a ƙalla mintuna biyu ina tsaye kafin na buɗe ƙofan a hankali na fito, filin gidan wayam babu kowa don ranan Anty Zulaihatu a gidanta ta kwana, na riƙe takalmana a hannu kamar ƙadangaruwan bayan tullu haka nake yin tafiya saɗaf-saɗaf na yi sa'a su Yaya Alhassan da suka shigo ba su rufe ƙofar ba. Na ja na fita waje layin babu kowa da alama daga masallacin sallan asubahi kowa gida ya shiga saboda yanayin hunturu da ake yi, sanyi ya lulluɓe ko'ina ga wani iska mai daɗi da yake haɗawa da hakan yake alamta sauƙar ruwan sama a ko wani irin lokacin.
Sai da na ƙarewa ko'ina kallo gabar da yamma kudu da arewa kafin na sauƙe tagwayen ajiyan zuciya mai nauyin kasa na soma lafiya. Sai da na bar cikin layin gabaɗaya kafin hango titi na miƙe, na dinga tafiya har sai da gari ya yi haske sosai mutane suka fara wucewa jifa-jifa domin gudanar da lamuran yau da kullum kamar yadda aka saba. Tun da na soma tafiyar ban tsaya ba sai da na iso babban tasha da ta fi wacce muke kaiwa talla girma da kuma mutane. Na tsaya cak na kasa gaba na kasa baya illa bin mutanen da ido nake yi ina ganin yadda suke ta zirga-zirga.
"Malama ki kauce daga kan hanya kin zo kin tare ma waje".
Na yi an yi zancen a zafafe kafin na matsa aka bangaje ni saura ƙiris na faɗi. Na ja ƙafafuna na je kasan wata itaciya na zauna na zabga uban tagumi.
"Baiwar Allah lafiya kuwa kika zauna kika yi shuru? Ko dai ba lafiya ne?".
A tsorace na ɗago kaina sakamakon furucin da suka yi wa ƙofofin kunnuwana dirar mikiya. Na firgita sosai da ganin yanayin wanda ya yi zancen, matashi saurayi ne da fuskarsa ta sha ɗinki kamar bayan ƙwarya ya shigan da sam babu tsari a cikinta ga jakan kayan da yake rataye a kafaɗunsa. Ban gama dawowa daidai daga giyan mamakin da ya shayar da ni ba na ƙara jin sautinsa a karo na biyu.
"Baiwar Allah ko dai da kurma nake magana ne?". Na girgiza masa kaina alamar a'a.
"To na ce lafiya kuwa na ga kin saɓe daga cikin al'umma kin zo gefe kin raɓe".
"Lafiya ƙalau".
"Wannan kuma zance ne kawai kike yin sa wataƙila don ki ji daɗin bakinki. Amma duk wanda ya gan ki ya san da cewar akwai damuwa a tattare da ke".
"Babu komai".
Ya ɗage kafaɗunsa alamar babu abin da ya sha masa "to shikenan Allah ya raba mu da babu". Ya sa ya yi wucewansa ya bar ni a wajen haka na ci gaba da zama har rana ta ƙwalle ban gusa daga wajen ba, motocin da aka yi wa lodi suka fara tashi.
"Baiwar Allah zai fi kyautuwa ki sauya wajen zama tun da na ga kamar zaman ne yake yi miki daÉ—i. Don rana ya fito kuma ya na gasa ki".
Na saci kallonsa da gefen idona kafin na tashi daga wajen kamar kazar da ƙwai ya fashe mata a ciki na sauya wajen zama ya biyo.
"Motar wani gari za ki shiga ne?".
Na soma zazzare idanu kamar shege a rabon gado, kamar daga sama na ji wani karan mota yana shelan sauran mutum uku motar garin jafari. Da sauri na furta "garin jafari zan je".
"Ai kuwa faÉ—uwa ta zo daidai da zama ni ma garin jafari na nufa sai ka tashi kawai mu shiga mota".
Na sunkuyar da kaina ƙasa kafin na ce"Anty Sawwama ta san da wannan zancen?".
"Sai da na fara tinkarar ta da maganar kafin na zo wajen ki". Na sauƙe tagwayen ajiyan zuciya ban iya cewa wani abun har ya tashi ya fita daga cikin ɗakin, ji nake yi kaina yana juya tamkar ba a cikin duniyar nake ba ga wani jirin da yake ɗeba ta don da kasancewar a zaune nake. Na koma na kwanta hawaye suna tsiyaya ta gefe da gefen idona.
Tabbas Yaya Alhassan mutumin kirki ne mai ƙoƙarin kame mutuncin kansa da kuma na ahalinsa a ko da yaushe, mutum ne mai nutsuwa da sanin ya kamata me yasa Anty Sawwama za ta amince masa akan auran watsatstsiyar da ta yi cikin shege ta kunyatar da iyayenta da duk wani wanda ya yarda da ita a idon duniya. Hatta mahaifiyarta ta nuna rashin buƙatata a kusa sai ita ce za ta buƙaci ɗanta ya kasance a tare da ni?.
Na sauƙe tagwayen ajiyan zuciya ina gyara kwanciyata, ba zan zama silar rugujewar rayuwar Yaya Alhassan ba. Don haka na gwammace na tafi can wani wajen da ban san kowa ba ni ma ba sanni ba na je na yi rayuwata. Ko zan sama kwanciyar hankalin da na rasa a yanzu. Gwara na shiga duniya kamar yadda Umma ta yi ikirarin ta sallama ni gare ta.
[10/30, 4:03 PM] Maimunatu Iyam🥰: *DAFIN HARSHE*
Â©ï¸ Maimuna Tijjani Iyam
______________________________________
Page 4ï¸âƒ£0ï¸âƒ£
Haka na kwana ina tunani da saƙa da warwara cikin raina, ganin bacci ya ƙi kawo mini ziyara hakan ya sani tashi na fito na ɗaura alawa na koma ciki na gabatar da salla raka'a biyu. Na ɗaga hannayena dukka biyu sama sai dai na kasa magana rawa kawai jikina yake yi. Na kifa kaina a bisa gwiyoyina ina rero kukan marar sauti. Ban runtsa ba har sai da aka yi ƙiran sallan asubahi Anty Sawwama ta shigo da nufin tashi ta iske ni zaune ta dalle mini idanuna da haske tocila.
"Lafiya na gan ki a zaune kamar ba ki runtsa ba?".
"Na runtsa kawai na tashi ne da na ji ƙiran salla". Ba ta ce da ni komai ba ta juya ta fita na bi bayan ta alwala na yi na zauna na buga tagumi a gaban botan har Yaya Alhassan, Amir da Umar suka fito domin tafiya masallaci.
"Amatullah lafiya kuka zauna kika zagba tagumi?". Na tsinkayo muryar Amir a tsakiyar kaina na yi figigi na dawo cikin hayyacina.
"Lafiya ƙalau ina kwananku". Suka haɗe baki wajen amsawa kana suka fita, na tashi na koma cikin ɗakin na shimfiɗa sallaya a zaune na yi sallan don ji nake yi tamkar ƙafafuna ba za su ɗauke ni ba tun ina raka'an farko nake kuka har na yi sallama na ɗaga hannayena dukka biyu zama ina kirari ga Ubangijina.
"Ya Allah kai mai ikon akan kowa da kuma komai. Ya Allah kai ne masanin sirrin dake taskace cikin tsokar zuciyar dake a ciki ƙirji, Allah ka kawo mini mafitan halin da nake ciki. Zan tafi na je can wani wajen da ba a sanni ba ni ma ban san kowa na je na ci gaba da rayuwa a can, don na fahimci zama a nan shi ma wani matsalan ne. Tun da har Umma ta furta ba ta buƙata ta ta sallamar da ni ga duniya zan tafi can wani wajen na je na yi rayuwata, ba zan zama matsala ga rayuwar wasu ba. Ya Allah ya dubi lamarina ka kawo mini komai da sauƙi ka ba ni ikon cinye wannan jarabawan da ya faɗa mini. Allah kai mai rahama ne Allah ya lulluɓe Abbana da rahamarka, Ya Allah kai mai gafara ne Allah ka gafarta masa".
Na shafa addu'ar cikin sanyi da mutuwar jiki wasu hawayen suna gangarowa daga idanuna, na ji ƙarar buɗe ƙofar hakan ya sa na yi saurin komawa na kwanta ba tare da na cire hijabin da na yi sallan ba. Aka shigo aka zauna kusa da ku dab har ina ji sautin ajiyan zuciya da take sauƙewa akai-akai.
Ta dafa goshina tana shafawa har zuwa kaina"Amatullahi Baiwar Allah ina son rayuwarki ta inganta ina don ganin ki cikin farin ciki. A yanzu ba ni da burin da ya wuce na gan nutsuwarki ya daidaita kin sama kwanciyan hankali da walwala ki yi rayuwa kamar kowa cikin sakewa wannan dalilin ya sa nake son Alhassan ya aure ki. Don hankalina ba zai kwanta ba matuƙar kika yi aure a wani wajen kika shiga cikin wasu dangin da wataƙila su goranta miki akan abin da ya faru da ke ko ma su wulaƙanta ki. Amatullah tun ranar da aka kawo mini gawar Manniru a gaba babu rai a tattare da shi na yi wa kaina alƙawarin ba zan taɓa barin abin da ya haifa ta wulaƙanta ba bayan ransa, zan yi tsayiwan tsayin daka wajen tabbatar da cewar rayuwarki ta inganta. Ina da yaƙinin ko bayan babu raina Alhassan ba zai taɓa bari ki wulaƙanta ba".
Ta ƙare zancen tare da gyara mini Kwanciyata ta ja hijabin ta lulluɓe mini ƙafafuna da shi, ta fita rufe ƙofan da ta yi ya yi daidai da bugawan da zuciyata ta yi tamkar za ta ɓalle allon ƙirjina ta fito waje ta daka rawan disko. Tausayin kaina da na ahalina ya mamaye mini ruhina hawaey suka jiƙa mini fuska lajab kaina ya sara ƙirjina ya ci gaba da tsananta bugu.
A bayyane na furta"Anty ki yafe mini wallahi ba zan iya zama ba. Gwara na fi can inda ba a sannin ba kuma ban san kowa ba sai na fi samun kwanciyar hankali". Na ƙarƙare zancen ina tashi na zauna daɓas na leƙa ta taga na ga har gari ya soma yin haske na buɗe ƙofar ɗakin har na saƙalo ƙafata waje na hango su Yaya Alhassan suna shigowa da alama sai yanzu suka dawowa daga masallaci na yi wuf na shanye ƙafata na tura ƙofar ina leƙan su, zuciyata ta harba ganin Yaya Alhassan ya nufo ɗakin yayin da Amir da Umar suka shige ɗakinsu. Ban san abin da ya tuna ba sai kuma na ga juya ta ya bi bayan su Amir, na sauƙe ɓoyayyan ajiyan zuciya ina dafe ƙirjina da yake bugu.
Sai da na ɓata a ƙalla mintuna biyu ina tsaye kafin na buɗe ƙofan a hankali na fito, filin gidan wayam babu kowa don ranan Anty Zulaihatu a gidanta ta kwana, na riƙe takalmana a hannu kamar ƙadangaruwan bayan tullu haka nake yin tafiya saɗaf-saɗaf na yi sa'a su Yaya Alhassan da suka shigo ba su rufe ƙofar ba. Na ja na fita waje layin babu kowa da alama daga masallacin sallan asubahi kowa gida ya shiga saboda yanayin hunturu da ake yi, sanyi ya lulluɓe ko'ina ga wani iska mai daɗi da yake haɗawa da hakan yake alamta sauƙar ruwan sama a ko wani irin lokacin.
Sai da na ƙarewa ko'ina kallo gabar da yamma kudu da arewa kafin na sauƙe tagwayen ajiyan zuciya mai nauyin kasa na soma lafiya. Sai da na bar cikin layin gabaɗaya kafin hango titi na miƙe, na dinga tafiya har sai da gari ya yi haske sosai mutane suka fara wucewa jifa-jifa domin gudanar da lamuran yau da kullum kamar yadda aka saba. Tun da na soma tafiyar ban tsaya ba sai da na iso babban tasha da ta fi wacce muke kaiwa talla girma da kuma mutane. Na tsaya cak na kasa gaba na kasa baya illa bin mutanen da ido nake yi ina ganin yadda suke ta zirga-zirga.
"Malama ki kauce daga kan hanya kin zo kin tare ma waje".
Na yi an yi zancen a zafafe kafin na matsa aka bangaje ni saura ƙiris na faɗi. Na ja ƙafafuna na je kasan wata itaciya na zauna na zabga uban tagumi.
"Baiwar Allah lafiya kuwa kika zauna kika yi shuru? Ko dai ba lafiya ne?".
A tsorace na ɗago kaina sakamakon furucin da suka yi wa ƙofofin kunnuwana dirar mikiya. Na firgita sosai da ganin yanayin wanda ya yi zancen, matashi saurayi ne da fuskarsa ta sha ɗinki kamar bayan ƙwarya ya shigan da sam babu tsari a cikinta ga jakan kayan da yake rataye a kafaɗunsa. Ban gama dawowa daidai daga giyan mamakin da ya shayar da ni ba na ƙara jin sautinsa a karo na biyu.
"Baiwar Allah ko dai da kurma nake magana ne?". Na girgiza masa kaina alamar a'a.
"To na ce lafiya kuwa na ga kin saɓe daga cikin al'umma kin zo gefe kin raɓe".
"Lafiya ƙalau".
"Wannan kuma zance ne kawai kike yin sa wataƙila don ki ji daɗin bakinki. Amma duk wanda ya gan ki ya san da cewar akwai damuwa a tattare da ke".
"Babu komai".
Ya ɗage kafaɗunsa alamar babu abin da ya sha masa "to shikenan Allah ya raba mu da babu". Ya sa ya yi wucewansa ya bar ni a wajen haka na ci gaba da zama har rana ta ƙwalle ban gusa daga wajen ba, motocin da aka yi wa lodi suka fara tashi.
"Baiwar Allah zai fi kyautuwa ki sauya wajen zama tun da na ga kamar zaman ne yake yi miki daÉ—i. Don rana ya fito kuma ya na gasa ki".
Na saci kallonsa da gefen idona kafin na tashi daga wajen kamar kazar da ƙwai ya fashe mata a ciki na sauya wajen zama ya biyo.
"Motar wani gari za ki shiga ne?".
Na soma zazzare idanu kamar shege a rabon gado, kamar daga sama na ji wani karan mota yana shelan sauran mutum uku motar garin jafari. Da sauri na furta "garin jafari zan je".
"Ai kuwa faÉ—uwa ta zo daidai da zama ni ma garin jafari na nufa sai ka tashi kawai mu shiga mota".