Sashe 35
Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tsaye a ƙofar fita na hango Al'amin yana tsaye muka sakarwa juna murmushi yayin da muka haɗa ido, na riƙo hannun Ammi ina cewa"raka ni na je na yi wa Bawan Allahn can godiya".
"In kuka daɗe ni kam tafiyata zan yi don yunwa nake ji". Rauda ta yi zancen tana neman waje ta zauna tana jiran mu, ba mu amsa mata ba illa darawa da muka yi dukkanmu. Da sallama muka isa wajen Al'amin ya amsa mana yana ƙara yalwata annurin fuskarsa.
"Na yi tunanin ai ɓacewa kuka yi a cikin makarantar".
Na murmusa tare da cewa"mun tsaya yi karatu ne".
"Na dai lura ajin matan nan kun dade sosai".
Na ƙara murmusawa a karo na biyu kana na ce"daman na zo na yi maka godiya ne. Tabbas ka cece ni daga tuhumar Malam Aminu".
"Ya zama dole ne hakan Amatullah babu wanda bai san tambayoyin titsiye irin na Malam Aminu ba".
"To ni dai ina godiya matuƙa".
Har yanzu fuskarsa É—auke take da murmushi ya ce"to yanzu dai mu je na raka ku ko?".
Ammi ta amshe zancen"mu muka ce maka muna buƙata".
Ya harare ta"yau dai ba zan kula ki don masifarki sai dai ki ci kanki". Ban tsoma musu baki ba illa murmushin da na yi muka soma tafiya muka isa wajen Rauda sai dariya muke yi mata don duk ta sauya Ammi sai tsiya take ya mata wai kamar ba ta yin azumi yunwar lokaci guda ta jigata ta har haka. Har muka rabu da Ammi da Rauda, Al'amin bai daina ja na da hira ba har farkon layinmu ya raka ni, muka rabu cikin girmamawa da mutunta juna.
Ina doso ƙofar gidanmu na ji gabaɗaya raina yana ɓaci zuciyata tana tafasa sosai. Haka kawai na nema dukkan nutsuwata na rasa ƙirjina ya tsananta bugu. Sai da na tsaya a zaure na ja dogon numfashi na fesar kafin na ƙarisa cikin gidan, har yanzun Umma ba ta dawo ba don haka wanka na yi na sauya kayana na tattare wasu abubuwan kana na ɗaura mama girki tuwo na yi da miyar bushashshen kuɓuewa na juye a kula, na je wajen Amira don ba na son zama shirun.
Babban dalilin ma shi ne ina son jin haƙiƙanin abin da ya faru tsakanin Asabe da Malam Vector da ya kai su ga raunana juna, kiciɓus na yi da Ummanta za ta fito na matsa na mata hanya ina yi mata addu'ar a dawo lafiya bayan ta shaida mini za ta je wajen Sa'ade uwar adashe ta kai zubinta.
A falo na tarar da Amira tana kallo a wayanta na zauna kusa da ita tare da fizge wayar, ta bi ni da kallo"har kin dawo?".
"Har ne ma? Watau don ba ke kike zuwa ba dole ki faɗi haka. Amira na yi na yi dake mu shiga islamiyyar nan amma kin ƙi, ina guje miki ranar da wannan damar za ta kuɓuce miki".
Ta gyara zamanta tare da cewa"tun da dai na sama na salla ya ishe ni". Kaina kawai na jijjina na kawar da maganar ta hanyar cewa"wai ni kuwa me ye faru tsakanin Asabe da Maman Vector, Umma ba ta nan balle na tambaye ta".
"Kin san Baban Vector ya dawo daga Benue shi ne Maman Vector ta kama shi da Asabe a cikin É—akinta suna hira, kin sa ta da shegen kishin tsiya tana ganin haka ba ta wata-wata ba ta É—auko tafasasshen ruwan zafi ta shiga ta juyewa Asabe a jikinta".
Na dafe ƙirji"na shiga uku. Amma kuwa Maman Vector ba ta kyauta ba ai kamata ya yi ta fara jin dalilin shigarsa ɗakin Asabe".
"Ko ni ce fa zan yi fiye da abin da Maman Vector ta yi, wani dalilin ne zai sanya su keɓe da juna bayan su ɗin ba muharraman juna ba ne".
"Amira kenan. To ai in haka ne ma laifin Baban Vector ne tun da shi ya je har cikin ɗakinta". Ta taɓe baki"koma dai mene ne ni kam Maman Vector ta yi min daidai". Ta gyara zamana ina fuskantan da kyau kana na soma cewa"ni zuwa na yi ma na tambaye ki, ko akwai in da za ki je ne yanzu ko zuwa bayan sallan isha'i?".
Ta yi mini wani kallo kana ta ce"yau ko toyar awara ba zan fita ba amma lafiya kike tambaya?". Na yi ɗan jim kafin na ce"wallahi ba za ki gane ba ne ba na son zaman cikin gidan ne, ko Bashir za ki ƙira mini a waya to mu gaisa?". Tun kafin na rufe bakina na ga ta tsare ni da wani irin kallon mamaki da al'ajabi.
[10/4, 12:16 PM] Maimunatu Iyam🥰: *DAFIN HARSHE*
©ï¸Maimuna Tijjani Iyam
__________________________________
Page 2ï¸âƒ£7ï¸âƒ£
Sake da baki da hanci take kallona tamkar wacce ta ga wani sabon halitta, mamakinta ya kasa ɓoyiwa har sai ta furzo shi waje.
"Bashir kuma? Yau da bakinki kike cewa na ƙira miki Bashir?". Na sauƙe sakakken ajiyar zuciya mai nauyin gaske kafin na sama zarafin faɗin"Amira ke fa ko yaushe kike nusar da ni cewar wanda ya nuna yana sonka a rayuwar nan ya gama maka komai, to yanzu laifi ne don na buƙaci ki ƙira mini shi kawai mu gaisa". Ta jinjina kanta"ba laifi ba ne kawai ban yi tunanin za ki buƙaci hakan da wuri ba ne, bari na ƙira miki shi". Murmushi kawai na sakar mata ina miƙa mata wayarta da yake hannuna ta karɓa ta soma lalumo lambarsa, haka kawai na tsinci kaina cikin wani irin yanayi wanda ni kaina ba zan iya fasalts ainihin takamammen abin da nake ji ba, na dai don kawai na sauya daga Amatullah ɗin da nake a can baya.
Manna mini wayar da ta yi a kunne da sauƙar sallamar Bashir a cikin kunnuwana su suka yi nasarar dawo da ni izuwa duniyar zahiri daga na tunanin da na afka.
Na sauƙe ɓoyayyar ajiyar zuciya kafin na amsa sallamar, jin muryata ya sanya sa sakin wani nishaɗantaccen murmushin da har sai da na ji ilahirin gaɓoɓin jikin sun amsa.
"Tabbas na cika cikakken mai sa'a tun da har Sarauniya da kanta ta ƙira ni yau. Da ina da ikon buɗe ƙirjina da na yi hakan don na gwada miki irin farin cikin da nake ciki a yanzu".
"Uhmm! Daman na ƙira ne don mu gaisa. Kuma na ba ka haƙuri akan abin da ya faru ɗazu".
Tun kafin na rufe bakina ya katse ni"babu abin da za ki yi min a cikin duniyar wanda yake buƙatar sai kin ba ni haƙuri Amatullah, ni ɗin bawanki ne mai hidimta miki kuma zan yi alfahari da hakan a ko'ina kuma a gaba ko waye. Ina da tabbacin ba zan taɓa yin dana sanin sonki ba har abada ki ba ni dama don na gwada miki ƙarfin son da nake yi miki".
Gabaɗaya na ji jikina ya mutu murus na gyara zamana kafin na ce"na ba ka dama". Ina faɗin haka na miƙawa Amira wayar ina rufe fuskata da tafukan hannayena saboda kunyar da yi wa raina mamaya.
Babu abin da Amira take yi face dariya a haka dai suka yi sallama da Bashir bayan na ji da kunnena ya na faɗin ya damƙa amanata a hannunta.
"Lalle ikon Allah! Ashe akwai ranar da za ki ba da kai bori ya hau Amatullah?. Haƙiƙa Bashir ya cika mai sa'a kamar yadda yake faɗa".
"Ban san me yasa ba ban san dalilin da ya sa har na ba shi dama ba Amira. Na dai fahimta kawai ina buƙatar wanda zai dinga kwantar mini da hankali ne wanda zai dinga saurara damuwa da matsalolin rayuwarta, wanda a duk lokacin da nake cikin damuwa zan tsaya a tare da ni. Tun da kin ga Umma ko yaushe ba ta zama a gida babu shaƙuwa a tsakaninmu ba ta da lokacin sauraran damuwata". A raunane na ƙare zancen ƙwalla yana ciko mini kurmin idanuna.
Cike da kula ta Amirka take furta" ko ba ki da wata matsala ma yanzu kin kai muzalin da za ki buƙaci wani a kusa da ke, rayuwar nan sai da farin ciki. Farin ciki kuma ba ya samuwa daga wajen masoyi na haƙiƙa". Na furzar da zazzafan iska mai ɗumi daga bakina kafin na sama sararin cewa"indai har na fahimci yana da ɗabi'un ƙwarai zan buƙaci ya gabatar da kansa a wajen Abba, don ni ba zan tsaya yin dogon soyayya da mutum ba".
"Ina da tabbaci akan son da Bashir yake yi miki gangariya ce".
Ban ce da ita komai illa gyaɗa mata kai da na yi alamar na gamsu da abin da ta furta, na jingina bayana cikin kujerar da nake zaune tare lumshe idanuna ina jin kaina kamar ba ni ba don ban taɓa tsammanin a nan kusa ko nisa zan iya amincewa wani saurayi ba. Shuru ya ratsa wajen kafin na kawar da shi ta hanyar cewa"wai a gida za ki zauna ne yau ba inda za ki je?". Na yi zancen har yanzu ban buɗe lumshashshun idanuna ba.
"Wai lafiyarki kuwa Amatullah? Sai ka ce wacce take zaune akan wuta a cikin gidan".
"Ba za ki gane ba ne Amira wallahi har raina yanzu ba na ƙaunar zaman cikin gidan nan, indai ba ya zama dole ba". Ta yi ɗan jim kafin ta ce"to ki dai yi a hankali". Na zabura tamkar wacce aka tsigarawa matsilli na buɗe idona tare da cewa"to ko dai gidan Ta salla za mu je?".
"Wai ke lafiyarki kuwa?".
Ta yi saurin katse mini hanzari kallon da ta tsare ni da shi ya tursasa mini yin ƙasa da kaina ina jin wani iri a rai da ruhina. Tashi ta yi ta shiga ciki ta ɗauko hijabinta ta dawo.
"Tashi mu je don na fahimci in dai ba fita muka yi hankalinki ba zai kwanta ba".
"In kuka daɗe ni kam tafiyata zan yi don yunwa nake ji". Rauda ta yi zancen tana neman waje ta zauna tana jiran mu, ba mu amsa mata ba illa darawa da muka yi dukkanmu. Da sallama muka isa wajen Al'amin ya amsa mana yana ƙara yalwata annurin fuskarsa.
"Na yi tunanin ai ɓacewa kuka yi a cikin makarantar".
Na murmusa tare da cewa"mun tsaya yi karatu ne".
"Na dai lura ajin matan nan kun dade sosai".
Na ƙara murmusawa a karo na biyu kana na ce"daman na zo na yi maka godiya ne. Tabbas ka cece ni daga tuhumar Malam Aminu".
"Ya zama dole ne hakan Amatullah babu wanda bai san tambayoyin titsiye irin na Malam Aminu ba".
"To ni dai ina godiya matuƙa".
Har yanzu fuskarsa É—auke take da murmushi ya ce"to yanzu dai mu je na raka ku ko?".
Ammi ta amshe zancen"mu muka ce maka muna buƙata".
Ya harare ta"yau dai ba zan kula ki don masifarki sai dai ki ci kanki". Ban tsoma musu baki ba illa murmushin da na yi muka soma tafiya muka isa wajen Rauda sai dariya muke yi mata don duk ta sauya Ammi sai tsiya take ya mata wai kamar ba ta yin azumi yunwar lokaci guda ta jigata ta har haka. Har muka rabu da Ammi da Rauda, Al'amin bai daina ja na da hira ba har farkon layinmu ya raka ni, muka rabu cikin girmamawa da mutunta juna.
Ina doso ƙofar gidanmu na ji gabaɗaya raina yana ɓaci zuciyata tana tafasa sosai. Haka kawai na nema dukkan nutsuwata na rasa ƙirjina ya tsananta bugu. Sai da na tsaya a zaure na ja dogon numfashi na fesar kafin na ƙarisa cikin gidan, har yanzun Umma ba ta dawo ba don haka wanka na yi na sauya kayana na tattare wasu abubuwan kana na ɗaura mama girki tuwo na yi da miyar bushashshen kuɓuewa na juye a kula, na je wajen Amira don ba na son zama shirun.
Babban dalilin ma shi ne ina son jin haƙiƙanin abin da ya faru tsakanin Asabe da Malam Vector da ya kai su ga raunana juna, kiciɓus na yi da Ummanta za ta fito na matsa na mata hanya ina yi mata addu'ar a dawo lafiya bayan ta shaida mini za ta je wajen Sa'ade uwar adashe ta kai zubinta.
A falo na tarar da Amira tana kallo a wayanta na zauna kusa da ita tare da fizge wayar, ta bi ni da kallo"har kin dawo?".
"Har ne ma? Watau don ba ke kike zuwa ba dole ki faɗi haka. Amira na yi na yi dake mu shiga islamiyyar nan amma kin ƙi, ina guje miki ranar da wannan damar za ta kuɓuce miki".
Ta gyara zamanta tare da cewa"tun da dai na sama na salla ya ishe ni". Kaina kawai na jijjina na kawar da maganar ta hanyar cewa"wai ni kuwa me ye faru tsakanin Asabe da Maman Vector, Umma ba ta nan balle na tambaye ta".
"Kin san Baban Vector ya dawo daga Benue shi ne Maman Vector ta kama shi da Asabe a cikin É—akinta suna hira, kin sa ta da shegen kishin tsiya tana ganin haka ba ta wata-wata ba ta É—auko tafasasshen ruwan zafi ta shiga ta juyewa Asabe a jikinta".
Na dafe ƙirji"na shiga uku. Amma kuwa Maman Vector ba ta kyauta ba ai kamata ya yi ta fara jin dalilin shigarsa ɗakin Asabe".
"Ko ni ce fa zan yi fiye da abin da Maman Vector ta yi, wani dalilin ne zai sanya su keɓe da juna bayan su ɗin ba muharraman juna ba ne".
"Amira kenan. To ai in haka ne ma laifin Baban Vector ne tun da shi ya je har cikin ɗakinta". Ta taɓe baki"koma dai mene ne ni kam Maman Vector ta yi min daidai". Ta gyara zamana ina fuskantan da kyau kana na soma cewa"ni zuwa na yi ma na tambaye ki, ko akwai in da za ki je ne yanzu ko zuwa bayan sallan isha'i?".
Ta yi mini wani kallo kana ta ce"yau ko toyar awara ba zan fita ba amma lafiya kike tambaya?". Na yi ɗan jim kafin na ce"wallahi ba za ki gane ba ne ba na son zaman cikin gidan ne, ko Bashir za ki ƙira mini a waya to mu gaisa?". Tun kafin na rufe bakina na ga ta tsare ni da wani irin kallon mamaki da al'ajabi.
[10/4, 12:16 PM] Maimunatu Iyam🥰: *DAFIN HARSHE*
©ï¸Maimuna Tijjani Iyam
__________________________________
Page 2ï¸âƒ£7ï¸âƒ£
Sake da baki da hanci take kallona tamkar wacce ta ga wani sabon halitta, mamakinta ya kasa ɓoyiwa har sai ta furzo shi waje.
"Bashir kuma? Yau da bakinki kike cewa na ƙira miki Bashir?". Na sauƙe sakakken ajiyar zuciya mai nauyin gaske kafin na sama zarafin faɗin"Amira ke fa ko yaushe kike nusar da ni cewar wanda ya nuna yana sonka a rayuwar nan ya gama maka komai, to yanzu laifi ne don na buƙaci ki ƙira mini shi kawai mu gaisa". Ta jinjina kanta"ba laifi ba ne kawai ban yi tunanin za ki buƙaci hakan da wuri ba ne, bari na ƙira miki shi". Murmushi kawai na sakar mata ina miƙa mata wayarta da yake hannuna ta karɓa ta soma lalumo lambarsa, haka kawai na tsinci kaina cikin wani irin yanayi wanda ni kaina ba zan iya fasalts ainihin takamammen abin da nake ji ba, na dai don kawai na sauya daga Amatullah ɗin da nake a can baya.
Manna mini wayar da ta yi a kunne da sauƙar sallamar Bashir a cikin kunnuwana su suka yi nasarar dawo da ni izuwa duniyar zahiri daga na tunanin da na afka.
Na sauƙe ɓoyayyar ajiyar zuciya kafin na amsa sallamar, jin muryata ya sanya sa sakin wani nishaɗantaccen murmushin da har sai da na ji ilahirin gaɓoɓin jikin sun amsa.
"Tabbas na cika cikakken mai sa'a tun da har Sarauniya da kanta ta ƙira ni yau. Da ina da ikon buɗe ƙirjina da na yi hakan don na gwada miki irin farin cikin da nake ciki a yanzu".
"Uhmm! Daman na ƙira ne don mu gaisa. Kuma na ba ka haƙuri akan abin da ya faru ɗazu".
Tun kafin na rufe bakina ya katse ni"babu abin da za ki yi min a cikin duniyar wanda yake buƙatar sai kin ba ni haƙuri Amatullah, ni ɗin bawanki ne mai hidimta miki kuma zan yi alfahari da hakan a ko'ina kuma a gaba ko waye. Ina da tabbacin ba zan taɓa yin dana sanin sonki ba har abada ki ba ni dama don na gwada miki ƙarfin son da nake yi miki".
Gabaɗaya na ji jikina ya mutu murus na gyara zamana kafin na ce"na ba ka dama". Ina faɗin haka na miƙawa Amira wayar ina rufe fuskata da tafukan hannayena saboda kunyar da yi wa raina mamaya.
Babu abin da Amira take yi face dariya a haka dai suka yi sallama da Bashir bayan na ji da kunnena ya na faɗin ya damƙa amanata a hannunta.
"Lalle ikon Allah! Ashe akwai ranar da za ki ba da kai bori ya hau Amatullah?. Haƙiƙa Bashir ya cika mai sa'a kamar yadda yake faɗa".
"Ban san me yasa ba ban san dalilin da ya sa har na ba shi dama ba Amira. Na dai fahimta kawai ina buƙatar wanda zai dinga kwantar mini da hankali ne wanda zai dinga saurara damuwa da matsalolin rayuwarta, wanda a duk lokacin da nake cikin damuwa zan tsaya a tare da ni. Tun da kin ga Umma ko yaushe ba ta zama a gida babu shaƙuwa a tsakaninmu ba ta da lokacin sauraran damuwata". A raunane na ƙare zancen ƙwalla yana ciko mini kurmin idanuna.
Cike da kula ta Amirka take furta" ko ba ki da wata matsala ma yanzu kin kai muzalin da za ki buƙaci wani a kusa da ke, rayuwar nan sai da farin ciki. Farin ciki kuma ba ya samuwa daga wajen masoyi na haƙiƙa". Na furzar da zazzafan iska mai ɗumi daga bakina kafin na sama sararin cewa"indai har na fahimci yana da ɗabi'un ƙwarai zan buƙaci ya gabatar da kansa a wajen Abba, don ni ba zan tsaya yin dogon soyayya da mutum ba".
"Ina da tabbaci akan son da Bashir yake yi miki gangariya ce".
Ban ce da ita komai illa gyaɗa mata kai da na yi alamar na gamsu da abin da ta furta, na jingina bayana cikin kujerar da nake zaune tare lumshe idanuna ina jin kaina kamar ba ni ba don ban taɓa tsammanin a nan kusa ko nisa zan iya amincewa wani saurayi ba. Shuru ya ratsa wajen kafin na kawar da shi ta hanyar cewa"wai a gida za ki zauna ne yau ba inda za ki je?". Na yi zancen har yanzu ban buɗe lumshashshun idanuna ba.
"Wai lafiyarki kuwa Amatullah? Sai ka ce wacce take zaune akan wuta a cikin gidan".
"Ba za ki gane ba ne Amira wallahi har raina yanzu ba na ƙaunar zaman cikin gidan nan, indai ba ya zama dole ba". Ta yi ɗan jim kafin ta ce"to ki dai yi a hankali". Na zabura tamkar wacce aka tsigarawa matsilli na buɗe idona tare da cewa"to ko dai gidan Ta salla za mu je?".
"Wai ke lafiyarki kuwa?".
Ta yi saurin katse mini hanzari kallon da ta tsare ni da shi ya tursasa mini yin ƙasa da kaina ina jin wani iri a rai da ruhina. Tashi ta yi ta shiga ciki ta ɗauko hijabinta ta dawo.
"Tashi mu je don na fahimci in dai ba fita muka yi hankalinki ba zai kwanta ba".