Sashe 12
Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da wani irin hanzarin na waigo ina ƙarewa Amira da ta yi maganar cikin takewa da ƙwarin gwiwa kallo haka nan ma Abba shi ma kallon natan yake yi.
"Ita ba ta da bakin kare kanta sai ke?". Cikin girmamawa Amira ta amsa da faɗin"Abba ba ta san komai ba ne shi yasa ta kasa cewa wani abu. Amma ina mai ƙara ba ka haƙuri na san yadda kake taka tsantsan da tarbiyyan Amatullah. Ka yafe min akan kuskuren da na yi na ba ta sunanta a matsayin nawa".
Sai da ya yi ɗan jim kamar mai tunani ko nazarin wani abun kafin ya ce"ba komai amma dai a dinga kiyayewa. Ke ma bai dace kina tara samari a ƙofan gidanku ba ki nutsu ki fitar da wanda kike so a cikinsu, don haka ne daraja da kimarki a matsayinki ta ɗiya mace".
"In sha Allah Abba kwana nan zan fita da guda daga cikin su. Ku dai ci gaba da yi mana addu'a Allah ya ba mu na gari". Cike da jin daÉ—i Abba ya ce"Amin amin ya hayyu. Kuma in kin je kar ki daÉ—e Amira, ni sai na rasa ma me ye kuke tattaunawa su yi awanni suna zance".
"Ba zan wuce mintin talatin ba ina sha Allah". Kansa kawai Abba ya jinjina ya wuce ciki sai da na tabbatar ya gama wucewa kafin na fizgo hannun Amira.
"Waye kika kika ba shi sunana har yanzu gida nema na?". Ta fizge hannunta"dalla! Ki nutsu mu yi magana. Malama ni babu wanda na ba wa sunanki balle har ya zo gida ne nemanki, na yi haka ne kawai don na ƙwace ki daga tuhumar Abba. Yanzu dai ki zo mu je mu ga ko wane ne kuma da me ye ya zo".
"A'a Amira ni gaskiya babu inda zan je tsoro nake ji". Ta watsa mini harara kafin ta finciko ni muka yi waje muna fitowa muka hango mutum zaune a bisa babur yana latsa wayarsa.
"Amira na shiga uku! Idan Abba ya fito ya kalle ni fa?". Na furta muryata tana rawa.
"Ki nutsu mu yi abin da ya kamata mu koma gida akan lokaci. Ban da abin ki me ye zai fito da Abba yanzu kuma, ke dai kawai ki nutsu". Tana dasa aya anan ta ja hannuna muka ci gaba da tafiya duk ɗaga ƙafar da zan yi sai ƙirjina ya buga har muka isa wajen mutumin.
Sunan da ya ƙira ni da shi ya ƙara jefa ni cikin firgici.
"Tauraruwa Amatullah ba ki tsammanin gani na a ƙofar gidanku ba ko?". Jikina ya soma rawa tamkar wacce ake jonawa wutan lantarki. Da ƙyar na daidai nutsuwata.
"Mai-mai-mai aska kai ne?".
"Ƙwarai kuwa ni ne haka kawai zuciyata ta kasa nutsuwa. Na ji ko runtsawa ba zan iya yi ba idan har ban yi kwalli da kyakykyawar fuskarki ba".
"Amatullah wane shi? A ina kika san shi?". Amira ta yi magana a karo na farko.
"Amira shi ne wanda na ba ki labarin wanda muka haÉ—u a inda na kai talla yau". Ban jira amsarta ba na juya ina fuskantarsa da kyau na ci gaba da maganata.
"Na roƙe ka da girman wanda yake yi mana ruwa da ƙanƙara kar ka ƙara sako ƙafarka cikin layin nan, me ye kake so da ni? Don Allah kar ka ja mini masifa da bala'in da kaina ba zai iya ɗauka ba".
"Amatullah ba na nufin da masifa ko bala'in face alkhairin Allah".
"Wani irin alkhairi?".
"Ƙauna ce tafe da ni kuma ina fatan za ki amshe ƙoƙon barana".
Takaici ya mamaye zuciyata"ba na soyayya kuma ba zan fara akan ba don haka ka yi haƙuri Abbana bai ba ni damar tsayawa da ko wani ɗan namiji ba a hali yanzu". Ina gama faɗin haka na ja hannun Amira muka bar wajen muka shiga zaure ɗalibaina suka zuro mana ido. Nan take na sallame su duk suka watse muka zauna ni da Amira.
"Shi ne za ki tursasa mini fita kuma ki kasa cewa komai a gabansa. Kika bar ni ni kaɗai ina ta magana". Ta ɗan murmusa kafin ta ce"na ga ai ba cutar da ke ya zo yi ba shi yasa na yi shuru. Soyayya ce ta kawo sa kin ga kuma babu yanda za a yi na farraƙa tsakanin masoya".
Babu shiri na kai mata duka ta kauce tana ƙara ƙyalƙyale wa da dariya. Na miƙe tsaye ita ma ta miƙe na naɗe tabarma ina cewa"zan shiga ciki kar Abba ya ce na daɗe. Idan Allah ya kai mu gobe za mu tattaunawa".
"Cab! Ni kuwa kin ga yanzu ma zan je na ƙarbo awarata a fita tuya". Na taɓe baki"Allah ya ganar da ke". Ba ta amsa ba illa dariyar da ta yi muka shigo ciki tare ta yi ɗakinsu na yi namu.
[7/17, 1:21 PM] Maimunatu Iyam: *DAFIN HARSHE*
Â©ï¸ Maimuna Tijjani Iyam
___________________________________
Page 1ï¸âƒ£0ï¸âƒ£
Kamar ƙadangaruwar bayan murhu haka na shigo ciki ina raɓe-raɓe iwa munafuka ko kuma wacce ta yi wa Sarki ƙarya, na nema waje na zauna a falo kasancewar na jiyo Umma da Abba suna tattaunawa a cikin uwar ɗaka. Kamar ko yaushe muryar Umma ya ɗara na Abba sai hayagaga take yi kamar za ta yi aron baki.
"Manniru ni fa ba ƙaramar yarinya ba ce da za ka tisa ni a gaba ka yi min wannan zancen banza da na wofin. Da yake ni ce karkatacciyar bishiyar kuka mai daɗin hawa shi yasa kowa ya ɗebo shararsa sai ya watso min, kai da danginka kun uzura min kun sako ni a gaban akan yarinyar da babu wanda ya taya ni goyan cikinta na tsawon watanni tara balle a kawo min tallafi yayin da nake nishin naƙudanta. Kowa ya ɗebo warin bakinsa zai nufo wai ina ƙoƙarin lalata tarbiyyar yarinyar nan".
"Ni kike kallon tsabar idona ki gaya min wannan zancen?". A kaurare na tsinkayo muryarta tana mayar masa da martani kamar wacce take jira ya ce kule ta ce cas.
"An gaya maka É—in na ce an gaya maka. Manniru ka yi duk abin da ka ga dama ga fili ga mai doki, babu wanda zai dakatar da kai balle ya hana ka wanzar da abin da zuciyarka ta yi niyyar aikatawa, ko ce maka aka yi ina tsoro ko shakkanka ne? Ai wallahi an sha ni na warke kan mage ya daÉ—e da wayewa".
"Ba zan taɓa iya aikata abin da zuciyata ta saƙa min akan ki ba. Allah ya sani kuma shi ne masanin abin da yake taskace a cikin tsokar zuciya kina da girma da matsayi a wajena ta yadda duk abin da kika yi zan jure shi, kuma na yi miki uzuri. Amma kin ga wannan harshen naki Hafsatu ina jiye miki zuwan ranar da zai yi silar fadawarki cikin halaka, DAFIN HARSHE ya fi dafin maciji illa da saurin nakasa sassan jikin ɗan adam".
Gama maganar da fitowarsa sun yi daidai da lokacin da ƙwallan da suka wadaci koramar idanuna samun hanyar kwaranya. Ya kafe ni da ido da hakan ya sani yin ƙasa da idanuna.
Sai da ya zauna kafin ya ba ni umarnin zama, na nema waje na zaune kusa da kujerar da yake zaune.
"Kukan me ye kike yi Amatullah?".
Na yi saurin kawar da hawaye da suka ɓata mini fuska kafin na sama sararin cewa"babu komai". Ya yi ɗan jim kafin can ya ci gaba da magana.
"Har baƙon nakin ya tafi?". Babu shiri na ɗago kaina ina dubansa mamaki da tsoro kwance luf a bisa fuskana ban ƙara shan giyan mamaki ba sai da ya ƙara jefa mini wani tambaya a karo na biyu da ya kusa sanya nokinan kaina suncewa take na soma haɗa gumi duk da sanyi da ni'iman Ubangiji da ya lulluɓe garin.
"Me kuka tattauna da shi?".
Na gyara zamana kafin na iya raba tsakanin haƙwarana da suka manne da junansu kamar mayen ƙarfe aka sanya a tsakanin su.
"Abba ba fa waje na ya zo ba. Baƙon Amira ne....". Kafin na ƙarisa ya ɗaga mini hannu alamar baya buƙatar sauraron jin ragowar bayani.
"Amatullah". Ya ƙira sunana cikin kaushashshen amon da ya ƙara sanya ni na sha jinin jikina ainun. Kamar kazar da aka jefa da ruwan gishiri na amsa da ƙyar.
"Na'am Abba".
"Me yasa kike so ki sauya daga yanda na san ku a baya? Shin zuciyar ba ta tausayina akan irin fafutukan da nake yi wajen ganin na inganta tarbiyan, na tsaya kai da fata don tabbatar da cewa ba ki sauƙa daga kan gwadaben da kika taso a kai ba. Amatullah ina sa burin ganin rayuwarki ta inganta na ƙayatar da ita sa ilmi da tarbiyya daga yanzu har izuwa lokacin da zan miƙa ragamar rayuwarki a hannun mijinki".
Take hawaye suka ɓarke mini ban iya cewa komai ba har ya ɗaura daga inda ya yi birki.
"Ke ce duk wani buri da fatan da nake da muradin wanzuwansa a bayan ƙasa kafin na koma ga mahaliccina. Ba zan hana ki soyyaya ko na katange ki ɗaga kula kowa ba don yanzu kin yi hankalin da za ki iya tantance abun da zai dace da ke ko akasin haka. Amma a duk lokacin da kika ji a ranki kin fi buƙatar aure akan karatun da kike yi, to kar ki ji nauyin sanar da ni haka. Ni kuma na yi miki alƙawarin aurar da ke a lokacin da kika buƙata domin gujewa afkuwar ɓarna da yin dana sani a gaba".
Wani irin gumjin kuka ne ya zo mini mai ƙarfin gaske, gabaɗaya falon ya ɗauki sautin kukan. Na ja jiki na ƙara matsowa dab da shi na riƙe ƙafarsa gam sannan na kwantar da kaina a jiki.
"Abba na tuna na yi nadama, ka ji tausayi na ka yafe miji wallahi ba zan ƙara aikata makamancin irin hakan ba. Na yi alƙawarin ba zan ƙara yin abun da zai ɓata maka rai ba".
Bai ba ni amsa ba har sai da na cire tsammani.
"Ita ba ta da bakin kare kanta sai ke?". Cikin girmamawa Amira ta amsa da faɗin"Abba ba ta san komai ba ne shi yasa ta kasa cewa wani abu. Amma ina mai ƙara ba ka haƙuri na san yadda kake taka tsantsan da tarbiyyan Amatullah. Ka yafe min akan kuskuren da na yi na ba ta sunanta a matsayin nawa".
Sai da ya yi ɗan jim kamar mai tunani ko nazarin wani abun kafin ya ce"ba komai amma dai a dinga kiyayewa. Ke ma bai dace kina tara samari a ƙofan gidanku ba ki nutsu ki fitar da wanda kike so a cikinsu, don haka ne daraja da kimarki a matsayinki ta ɗiya mace".
"In sha Allah Abba kwana nan zan fita da guda daga cikin su. Ku dai ci gaba da yi mana addu'a Allah ya ba mu na gari". Cike da jin daÉ—i Abba ya ce"Amin amin ya hayyu. Kuma in kin je kar ki daÉ—e Amira, ni sai na rasa ma me ye kuke tattaunawa su yi awanni suna zance".
"Ba zan wuce mintin talatin ba ina sha Allah". Kansa kawai Abba ya jinjina ya wuce ciki sai da na tabbatar ya gama wucewa kafin na fizgo hannun Amira.
"Waye kika kika ba shi sunana har yanzu gida nema na?". Ta fizge hannunta"dalla! Ki nutsu mu yi magana. Malama ni babu wanda na ba wa sunanki balle har ya zo gida ne nemanki, na yi haka ne kawai don na ƙwace ki daga tuhumar Abba. Yanzu dai ki zo mu je mu ga ko wane ne kuma da me ye ya zo".
"A'a Amira ni gaskiya babu inda zan je tsoro nake ji". Ta watsa mini harara kafin ta finciko ni muka yi waje muna fitowa muka hango mutum zaune a bisa babur yana latsa wayarsa.
"Amira na shiga uku! Idan Abba ya fito ya kalle ni fa?". Na furta muryata tana rawa.
"Ki nutsu mu yi abin da ya kamata mu koma gida akan lokaci. Ban da abin ki me ye zai fito da Abba yanzu kuma, ke dai kawai ki nutsu". Tana dasa aya anan ta ja hannuna muka ci gaba da tafiya duk ɗaga ƙafar da zan yi sai ƙirjina ya buga har muka isa wajen mutumin.
Sunan da ya ƙira ni da shi ya ƙara jefa ni cikin firgici.
"Tauraruwa Amatullah ba ki tsammanin gani na a ƙofar gidanku ba ko?". Jikina ya soma rawa tamkar wacce ake jonawa wutan lantarki. Da ƙyar na daidai nutsuwata.
"Mai-mai-mai aska kai ne?".
"Ƙwarai kuwa ni ne haka kawai zuciyata ta kasa nutsuwa. Na ji ko runtsawa ba zan iya yi ba idan har ban yi kwalli da kyakykyawar fuskarki ba".
"Amatullah wane shi? A ina kika san shi?". Amira ta yi magana a karo na farko.
"Amira shi ne wanda na ba ki labarin wanda muka haÉ—u a inda na kai talla yau". Ban jira amsarta ba na juya ina fuskantarsa da kyau na ci gaba da maganata.
"Na roƙe ka da girman wanda yake yi mana ruwa da ƙanƙara kar ka ƙara sako ƙafarka cikin layin nan, me ye kake so da ni? Don Allah kar ka ja mini masifa da bala'in da kaina ba zai iya ɗauka ba".
"Amatullah ba na nufin da masifa ko bala'in face alkhairin Allah".
"Wani irin alkhairi?".
"Ƙauna ce tafe da ni kuma ina fatan za ki amshe ƙoƙon barana".
Takaici ya mamaye zuciyata"ba na soyayya kuma ba zan fara akan ba don haka ka yi haƙuri Abbana bai ba ni damar tsayawa da ko wani ɗan namiji ba a hali yanzu". Ina gama faɗin haka na ja hannun Amira muka bar wajen muka shiga zaure ɗalibaina suka zuro mana ido. Nan take na sallame su duk suka watse muka zauna ni da Amira.
"Shi ne za ki tursasa mini fita kuma ki kasa cewa komai a gabansa. Kika bar ni ni kaɗai ina ta magana". Ta ɗan murmusa kafin ta ce"na ga ai ba cutar da ke ya zo yi ba shi yasa na yi shuru. Soyayya ce ta kawo sa kin ga kuma babu yanda za a yi na farraƙa tsakanin masoya".
Babu shiri na kai mata duka ta kauce tana ƙara ƙyalƙyale wa da dariya. Na miƙe tsaye ita ma ta miƙe na naɗe tabarma ina cewa"zan shiga ciki kar Abba ya ce na daɗe. Idan Allah ya kai mu gobe za mu tattaunawa".
"Cab! Ni kuwa kin ga yanzu ma zan je na ƙarbo awarata a fita tuya". Na taɓe baki"Allah ya ganar da ke". Ba ta amsa ba illa dariyar da ta yi muka shigo ciki tare ta yi ɗakinsu na yi namu.
[7/17, 1:21 PM] Maimunatu Iyam: *DAFIN HARSHE*
Â©ï¸ Maimuna Tijjani Iyam
___________________________________
Page 1ï¸âƒ£0ï¸âƒ£
Kamar ƙadangaruwar bayan murhu haka na shigo ciki ina raɓe-raɓe iwa munafuka ko kuma wacce ta yi wa Sarki ƙarya, na nema waje na zauna a falo kasancewar na jiyo Umma da Abba suna tattaunawa a cikin uwar ɗaka. Kamar ko yaushe muryar Umma ya ɗara na Abba sai hayagaga take yi kamar za ta yi aron baki.
"Manniru ni fa ba ƙaramar yarinya ba ce da za ka tisa ni a gaba ka yi min wannan zancen banza da na wofin. Da yake ni ce karkatacciyar bishiyar kuka mai daɗin hawa shi yasa kowa ya ɗebo shararsa sai ya watso min, kai da danginka kun uzura min kun sako ni a gaban akan yarinyar da babu wanda ya taya ni goyan cikinta na tsawon watanni tara balle a kawo min tallafi yayin da nake nishin naƙudanta. Kowa ya ɗebo warin bakinsa zai nufo wai ina ƙoƙarin lalata tarbiyyar yarinyar nan".
"Ni kike kallon tsabar idona ki gaya min wannan zancen?". A kaurare na tsinkayo muryarta tana mayar masa da martani kamar wacce take jira ya ce kule ta ce cas.
"An gaya maka É—in na ce an gaya maka. Manniru ka yi duk abin da ka ga dama ga fili ga mai doki, babu wanda zai dakatar da kai balle ya hana ka wanzar da abin da zuciyarka ta yi niyyar aikatawa, ko ce maka aka yi ina tsoro ko shakkanka ne? Ai wallahi an sha ni na warke kan mage ya daÉ—e da wayewa".
"Ba zan taɓa iya aikata abin da zuciyata ta saƙa min akan ki ba. Allah ya sani kuma shi ne masanin abin da yake taskace a cikin tsokar zuciya kina da girma da matsayi a wajena ta yadda duk abin da kika yi zan jure shi, kuma na yi miki uzuri. Amma kin ga wannan harshen naki Hafsatu ina jiye miki zuwan ranar da zai yi silar fadawarki cikin halaka, DAFIN HARSHE ya fi dafin maciji illa da saurin nakasa sassan jikin ɗan adam".
Gama maganar da fitowarsa sun yi daidai da lokacin da ƙwallan da suka wadaci koramar idanuna samun hanyar kwaranya. Ya kafe ni da ido da hakan ya sani yin ƙasa da idanuna.
Sai da ya zauna kafin ya ba ni umarnin zama, na nema waje na zaune kusa da kujerar da yake zaune.
"Kukan me ye kike yi Amatullah?".
Na yi saurin kawar da hawaye da suka ɓata mini fuska kafin na sama sararin cewa"babu komai". Ya yi ɗan jim kafin can ya ci gaba da magana.
"Har baƙon nakin ya tafi?". Babu shiri na ɗago kaina ina dubansa mamaki da tsoro kwance luf a bisa fuskana ban ƙara shan giyan mamaki ba sai da ya ƙara jefa mini wani tambaya a karo na biyu da ya kusa sanya nokinan kaina suncewa take na soma haɗa gumi duk da sanyi da ni'iman Ubangiji da ya lulluɓe garin.
"Me kuka tattauna da shi?".
Na gyara zamana kafin na iya raba tsakanin haƙwarana da suka manne da junansu kamar mayen ƙarfe aka sanya a tsakanin su.
"Abba ba fa waje na ya zo ba. Baƙon Amira ne....". Kafin na ƙarisa ya ɗaga mini hannu alamar baya buƙatar sauraron jin ragowar bayani.
"Amatullah". Ya ƙira sunana cikin kaushashshen amon da ya ƙara sanya ni na sha jinin jikina ainun. Kamar kazar da aka jefa da ruwan gishiri na amsa da ƙyar.
"Na'am Abba".
"Me yasa kike so ki sauya daga yanda na san ku a baya? Shin zuciyar ba ta tausayina akan irin fafutukan da nake yi wajen ganin na inganta tarbiyan, na tsaya kai da fata don tabbatar da cewa ba ki sauƙa daga kan gwadaben da kika taso a kai ba. Amatullah ina sa burin ganin rayuwarki ta inganta na ƙayatar da ita sa ilmi da tarbiyya daga yanzu har izuwa lokacin da zan miƙa ragamar rayuwarki a hannun mijinki".
Take hawaye suka ɓarke mini ban iya cewa komai ba har ya ɗaura daga inda ya yi birki.
"Ke ce duk wani buri da fatan da nake da muradin wanzuwansa a bayan ƙasa kafin na koma ga mahaliccina. Ba zan hana ki soyyaya ko na katange ki ɗaga kula kowa ba don yanzu kin yi hankalin da za ki iya tantance abun da zai dace da ke ko akasin haka. Amma a duk lokacin da kika ji a ranki kin fi buƙatar aure akan karatun da kike yi, to kar ki ji nauyin sanar da ni haka. Ni kuma na yi miki alƙawarin aurar da ke a lokacin da kika buƙata domin gujewa afkuwar ɓarna da yin dana sani a gaba".
Wani irin gumjin kuka ne ya zo mini mai ƙarfin gaske, gabaɗaya falon ya ɗauki sautin kukan. Na ja jiki na ƙara matsowa dab da shi na riƙe ƙafarsa gam sannan na kwantar da kaina a jiki.
"Abba na tuna na yi nadama, ka ji tausayi na ka yafe miji wallahi ba zan ƙara aikata makamancin irin hakan ba. Na yi alƙawarin ba zan ƙara yin abun da zai ɓata maka rai ba".
Bai ba ni amsa ba har sai da na cire tsammani.