Sashe 23
Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta zame hannunta daga cikin nawa kafin ta furta"kowa ya san wannan. Don kwanakin baya duk inda kika shiga a garin nan maganarsa ake yi. Mai girma gwamna da kansa ya ba yi masa tayi wani gwagwgwaɓan matsayi a gwamnatance da alƙawarin buɗe jami'a mai zaman kanta a damƙa masa ragamarta kuma a sanya mats sunansa. Ban da alƙawarurrukan zunzurutun kuɗin da abubuwan more rayuwa da ya yi masa, amma duk da haka ya ƙi karɓa".
"Na rantse da girman wanda rayuwata take hannunsa ban san fuskarsa a zahiri ba. Kuma shi ya fara tara ta da maganan banza".
Ta yi hanzarin katse ni"ki rufa mana asiri Amatullah. Ko a mafarki mutumin ba zai taɓa tarar wata mace da maganar banza ba saboda dattakunsa yana ƙoƙarin kiyaye duk wani abun da zai taɓa martaban kimarsa. Ke dai kawai ki tsori ta ne da kalaman Bashir suna yi miki amsa-kuwwa a kunnenki". Na ja dogon numfashi na fesar kafin na ce"wallahi babu kuskure cikin abin da na faɗa miki Amira".
"Ki yi shuru haka ya isa". Tana rufe bakinta ta ja hannuna muka ci gaba da tafiya, har muka isa gida na kasa magana kamar gunki tafiyar kawai nake yi ba tare da na san inda nake ajiya ƙafana ba.
[8/4, 7:11 PM] Maimunatu Iyam: *DAFIN HARSHE*
Â©ï¸ Maimuna Tijjani Iyam
_______________________________________
Page 1ï¸âƒ£8ï¸âƒ£
Muna isa na wuce ɗakinmu na yada zango a falo ina mayar da nurfarfashi kamar wacce ta yi gudun ceton rai. Sai Amira ce ta shigo mini da kayan tallan ta juya ta fita bayan ta gama jeranta mini maganar da ban ba ta amsar ko guda daga ciki ba. Yadda na ji falon ya yi shuru ya tabbatar miji da cewar Umma ba ta cikin gidan amma na fi zargin cewar ba ta yi nisa ba tun da ga shi ba ta rufe ƙofa ba.
Ina zaune a wajen Abba ya fito daga ɗaki yana saka hula akansa, na maza na tashi na gyara zamana ina yi masa sannu da fitowa. Ya amsa mini yana neman waje ya zauna, mamaki ya hana ni yin wani motsin kirki na shiga duniyar tunanin dalili da ya hana Abba fita wajen aiki, a iya sanina da shi baya fashin zuwa wajen aiki in ba tare da wani ƙauƙauran dalili ba.
"Har kun dawo kenan?".
Na gyaÉ—a masa kaina da hakan ya ba shi zarafin ci gaba da maganar da ya sani daskarewa a wajen, na sha jinin jikina ainun.
"Ummanki ce ta fita tun ɗazu ita nake ta jira ni ma shi yasa ban fita ba". Na ɗaga ido ina kallonsa"Abba da ka yi tafiyar ka ai, wataƙila ba nisa ta yi ba".
Ya jijjiga kansa kafin ta ce da ni"A'a Amatullah ko na fita hankalina ba zai kwanta ba. Zan fi samun nutsuwa idan na ga ta dawo cikin ƙoshin lafiya". Na yi shuru na kasa yin magana don na ga lamarin ya fi ƙarfin kwanyata, tausayin Abba ya cika mini sashin ruhina har ƙwalla suka ciko mini kurmin idaniyata.
"Ya islamiyyarta kun kuwa? Ya batun sauƙanku yaushe ne?".
Na musguta kafin na ce"islamiyya alhamdulillah, Abba nan da sati huɗu ne sauƙar in sha Allah". Ya jinjina kansa"Allah ya nuna mana lokacin, za mu yi magana da Ummanki sai mu ga abin da ya dace ayi".
"Ina godiya Allah ya ƙara girma. Bari na sa maka ruwa a buta an yi ƙiran salla". Na ƙare zancen ina miƙewa na fita waje na sa masa ruwan alwala a buta kana ni ma na yi nawa. Na shiga cikin ɗaki bayan na sanar da shi na saka ruwan.
Ko da na iddar da sallan na daɗe a zaune na gaza gane me ye yake yi mini daɗi. Ƙur'anin da na ɗauko zan yi muraja'a ma na gaza karanta ko aya guda, ganin wankin hula yana son kai ni dare ya tursasa mini tashi na fara shirin tafiya islamiyya, sauran kunun da na dawo da shi na sha kafin na fito har lokacin Abba bai dawo ba. Don haka na shiga ɗakin su Amira na sanar da ita idan Abba bai dawo ba ta ja mana ƙofar falon.
Ina fitowa daga cikin gida na hango Abba yana dawowa na tsaya har ya iso wajen.
"Har kin fito za ki tafi?". Na É—aga masa kaina.
"Kin cin abinci ne?".
"Na sha kunu". Cike da kulawa ya ce"kunu ai ba abinci ba ne Uwata, ga wannan naira darin ki sayi ko awara ce ki ci in kin isa". Cikin girmamawa na amsa ina yi masa godiyar da yake amsawa cikin daɗin rai, muna tsaye a wajen muka hango Umma tafe, jikina ya yi matuƙar sanyi ganin yadda Abba gabaɗaya ya gigice daga ganin ta tun kafin ta iso wajen ya ɗauki hanyar zuwa gare ta da rawar jiki ya amshi jakar da yake maƙale a kafadarta.
Yana ta yi masa sannu ta yi biris da shi har suka iso inda nake, na yi mata sannu ta amsa mini a daƙile tamkar an yi mata dole.
"Ai ke na tsaya jira ki dawo kafin na fita".
Ta gantsalo masa harara kamar ta yi arba da kashi"ko yanzu da na dawo ɗin uban me ye zan tsinana maka?. Yanzu kam ga ni ai sai ka dafa ni ka cinye, babu dama na motsa ko wani wajen sai ka titsiye ni da tambayoyin babu gaira babu dalili". Ya yi shuru tare da sadda kansa ƙasa ba tare da ya ce komai ba. Ta kuma jan wani uban tsaki kafin ta zarce da faɗin"wuce mu shiga ciki yanzu ko". Ta yi zancen lokacin da yaran gidan da iyayensu maza da suka je masallaci suka nufo inda muke tsaye.
Tamkar raƙumi da akala haka Abba ya bi bayanta suka shiga cikin gida, na yi maza na goge hawayen da suka zubo mini ba tare da na shirya musu kafin na ɗauki hanyar bari wajen. A hankali nake tafiya tamkar wacce aka zarewa laka na shawo layin da zai sada ni da islamiyyar kenan na ji an danna mini horn ɗin mota har sai da na riɗime na rasa inda zan yi na tsaya kawai cak na ɗaura hannuna aka na lumshe idanuna ina jiran na ji da inda motar za ta buge ni.
"Ƴan matan buɗe idonki mana".
A hankali na soma buɗe idanuna kafin har na buɗe su tar akan sai da gabana ya faɗi, saboda kwarjinin da ya yi mini a ganin farko da na yi masa. Na yi saurin ja da baya ina dafe ƙirjina dole na yi ƙasa da idona.
"Na razana ki ko? Ki yi haƙora tuba nake yi. Ban lura da ke ba sai na zo dab dake". Shuru na yi ban amsa masa ba sai dai hakan bai hana sa ci gaba da furzar da zancen da ke cikinsa ba.
"Ko sai na durƙusa akan gwiwoyina ne sannan za ki haƙura".
"To ai ni babu abin da ka yi mini ba". Na yi maganar ina ƙoƙarin wucewa ya yi saurin shan gabana.
"Na razana ki mana baiwar Allah. Kuma kin san an ce tsorita musulumi haramu ne. Don Allah ki furta ki yafe min raina zai fi samun nutsuwa, don akan hanyar nake zan yi tafiya mai nisa. Ki taimaka min kar na tafi da haƙƙin wani a kaina".
Na cira kai na yi masa kallo guda kafin na janye idanuna"kamar yadda na gaya maka ba ka yi mini komai ba, amma tun da ka matsa na haƙura Allah ya kiyaye hanya ya kai ka lafiya". Ina gama maganar na wuce na soma tafiya cikin sauri saboda lokaci ya riga ya ƙure kafin na iso har Malam Suleiman ya shigo ajinmu ana karɓan hadda na shiga na zauna na buɗe ƙur'anina, duk yadda na so biya karatun lamarin ya gagara wai cire wando ta kai, ji na yi kamar ba a taɓa karanta mini wajen ba a kaf cikin rayuwata. Ina ta ƙoƙari haɗa kalmomin amma ya ci tura har aka iso kaina na tashi na isa gaban Malam Suleiman, sai dai na gaza karanta ko aya guda sai faman kame-kame nake yi.
"Amatullah anya ki biya karatun nan a gida kuwa?".
Na yi ƙasa da kaina don ni kaina na san duk abin da zai fito daga bakina a lokacin ƙarya ne.
"Malam na yi amma......". Kafin na ƙarisa ya dakatar da ni"koma ki zauna idan an fito salla ki zo ki same ni".
"To Malam". Na amsa da shi ina tashi daga wajen na koma mazaunina na zauna, na kwantar da kaina akan desk ban ɗago ba har sai da aka fita sallan asr Rauda ta taɓo ni na tashi muka fito muka yi alwala, muna iddar da sallan na wuce wajen Malam Suleiman.
Yana zaune a cikin staff room na shigo na zauna, sai da ya gama rubutun da yake yi kafin ya gyara zamansa yana fuskanta na da kyau ya soma magana.
"Amatullah mene ne yake damunki? Me ye ya yi miki zafi a cikin rayuwar nan?".
Kalamansa suka daki ƙwaƙwalwata tare da raunana zuciyata, na ɗau tsawon lokacin wani bai yi mini irin wannan tambayar ba.
"Babu abin da yake damuna Malam".
"Kar ki yi ƙarya don fuskarki ta riga da ta bayyanar da labarin zuciyarki. Amatullah dole akwai wani abun, tun da ga shi har ya fara taɓa karatunki, duk wanda ya sanki a makarantar nan ya san ki ne saboda dalilai guda biyu na farko ƙoƙari da mayar da hankalin da kike da shi akan karatu na biyu kuma ladabi da biyayyarki".
"Babu komai akwai dai matsalolin rayuwa ne na yau da kullum, kuma yanzu a rayuwar nan kowa da irin na shi kalan damuwar".
Ya yi ɗan jim kafin can ya yi magana cikin taushin harshe"na fahimta kuma ina fatan haka ɗin ne. Kar ki saka komai a ranki ki miƙa wa Allah dukkan lamuranki don shi kaɗai ne zai iya magance miki matsalolinki, kin ga rayuwar nan kowa da na shi matsalar idan kika ji na wani sai ki ji na ki ko kashi ɗaya bai kai cikin kashi ɗarin nasa ba. Kar ki bari ki ɓata shekarun da kika yi a baya kuma karatu mussamman yanzu da aski ya zo gaban goshi".
"Na rantse da girman wanda rayuwata take hannunsa ban san fuskarsa a zahiri ba. Kuma shi ya fara tara ta da maganan banza".
Ta yi hanzarin katse ni"ki rufa mana asiri Amatullah. Ko a mafarki mutumin ba zai taɓa tarar wata mace da maganar banza ba saboda dattakunsa yana ƙoƙarin kiyaye duk wani abun da zai taɓa martaban kimarsa. Ke dai kawai ki tsori ta ne da kalaman Bashir suna yi miki amsa-kuwwa a kunnenki". Na ja dogon numfashi na fesar kafin na ce"wallahi babu kuskure cikin abin da na faɗa miki Amira".
"Ki yi shuru haka ya isa". Tana rufe bakinta ta ja hannuna muka ci gaba da tafiya, har muka isa gida na kasa magana kamar gunki tafiyar kawai nake yi ba tare da na san inda nake ajiya ƙafana ba.
[8/4, 7:11 PM] Maimunatu Iyam: *DAFIN HARSHE*
Â©ï¸ Maimuna Tijjani Iyam
_______________________________________
Page 1ï¸âƒ£8ï¸âƒ£
Muna isa na wuce ɗakinmu na yada zango a falo ina mayar da nurfarfashi kamar wacce ta yi gudun ceton rai. Sai Amira ce ta shigo mini da kayan tallan ta juya ta fita bayan ta gama jeranta mini maganar da ban ba ta amsar ko guda daga ciki ba. Yadda na ji falon ya yi shuru ya tabbatar miji da cewar Umma ba ta cikin gidan amma na fi zargin cewar ba ta yi nisa ba tun da ga shi ba ta rufe ƙofa ba.
Ina zaune a wajen Abba ya fito daga ɗaki yana saka hula akansa, na maza na tashi na gyara zamana ina yi masa sannu da fitowa. Ya amsa mini yana neman waje ya zauna, mamaki ya hana ni yin wani motsin kirki na shiga duniyar tunanin dalili da ya hana Abba fita wajen aiki, a iya sanina da shi baya fashin zuwa wajen aiki in ba tare da wani ƙauƙauran dalili ba.
"Har kun dawo kenan?".
Na gyaÉ—a masa kaina da hakan ya ba shi zarafin ci gaba da maganar da ya sani daskarewa a wajen, na sha jinin jikina ainun.
"Ummanki ce ta fita tun ɗazu ita nake ta jira ni ma shi yasa ban fita ba". Na ɗaga ido ina kallonsa"Abba da ka yi tafiyar ka ai, wataƙila ba nisa ta yi ba".
Ya jijjiga kansa kafin ta ce da ni"A'a Amatullah ko na fita hankalina ba zai kwanta ba. Zan fi samun nutsuwa idan na ga ta dawo cikin ƙoshin lafiya". Na yi shuru na kasa yin magana don na ga lamarin ya fi ƙarfin kwanyata, tausayin Abba ya cika mini sashin ruhina har ƙwalla suka ciko mini kurmin idaniyata.
"Ya islamiyyarta kun kuwa? Ya batun sauƙanku yaushe ne?".
Na musguta kafin na ce"islamiyya alhamdulillah, Abba nan da sati huɗu ne sauƙar in sha Allah". Ya jinjina kansa"Allah ya nuna mana lokacin, za mu yi magana da Ummanki sai mu ga abin da ya dace ayi".
"Ina godiya Allah ya ƙara girma. Bari na sa maka ruwa a buta an yi ƙiran salla". Na ƙare zancen ina miƙewa na fita waje na sa masa ruwan alwala a buta kana ni ma na yi nawa. Na shiga cikin ɗaki bayan na sanar da shi na saka ruwan.
Ko da na iddar da sallan na daɗe a zaune na gaza gane me ye yake yi mini daɗi. Ƙur'anin da na ɗauko zan yi muraja'a ma na gaza karanta ko aya guda, ganin wankin hula yana son kai ni dare ya tursasa mini tashi na fara shirin tafiya islamiyya, sauran kunun da na dawo da shi na sha kafin na fito har lokacin Abba bai dawo ba. Don haka na shiga ɗakin su Amira na sanar da ita idan Abba bai dawo ba ta ja mana ƙofar falon.
Ina fitowa daga cikin gida na hango Abba yana dawowa na tsaya har ya iso wajen.
"Har kin fito za ki tafi?". Na É—aga masa kaina.
"Kin cin abinci ne?".
"Na sha kunu". Cike da kulawa ya ce"kunu ai ba abinci ba ne Uwata, ga wannan naira darin ki sayi ko awara ce ki ci in kin isa". Cikin girmamawa na amsa ina yi masa godiyar da yake amsawa cikin daɗin rai, muna tsaye a wajen muka hango Umma tafe, jikina ya yi matuƙar sanyi ganin yadda Abba gabaɗaya ya gigice daga ganin ta tun kafin ta iso wajen ya ɗauki hanyar zuwa gare ta da rawar jiki ya amshi jakar da yake maƙale a kafadarta.
Yana ta yi masa sannu ta yi biris da shi har suka iso inda nake, na yi mata sannu ta amsa mini a daƙile tamkar an yi mata dole.
"Ai ke na tsaya jira ki dawo kafin na fita".
Ta gantsalo masa harara kamar ta yi arba da kashi"ko yanzu da na dawo ɗin uban me ye zan tsinana maka?. Yanzu kam ga ni ai sai ka dafa ni ka cinye, babu dama na motsa ko wani wajen sai ka titsiye ni da tambayoyin babu gaira babu dalili". Ya yi shuru tare da sadda kansa ƙasa ba tare da ya ce komai ba. Ta kuma jan wani uban tsaki kafin ta zarce da faɗin"wuce mu shiga ciki yanzu ko". Ta yi zancen lokacin da yaran gidan da iyayensu maza da suka je masallaci suka nufo inda muke tsaye.
Tamkar raƙumi da akala haka Abba ya bi bayanta suka shiga cikin gida, na yi maza na goge hawayen da suka zubo mini ba tare da na shirya musu kafin na ɗauki hanyar bari wajen. A hankali nake tafiya tamkar wacce aka zarewa laka na shawo layin da zai sada ni da islamiyyar kenan na ji an danna mini horn ɗin mota har sai da na riɗime na rasa inda zan yi na tsaya kawai cak na ɗaura hannuna aka na lumshe idanuna ina jiran na ji da inda motar za ta buge ni.
"Ƴan matan buɗe idonki mana".
A hankali na soma buɗe idanuna kafin har na buɗe su tar akan sai da gabana ya faɗi, saboda kwarjinin da ya yi mini a ganin farko da na yi masa. Na yi saurin ja da baya ina dafe ƙirjina dole na yi ƙasa da idona.
"Na razana ki ko? Ki yi haƙora tuba nake yi. Ban lura da ke ba sai na zo dab dake". Shuru na yi ban amsa masa ba sai dai hakan bai hana sa ci gaba da furzar da zancen da ke cikinsa ba.
"Ko sai na durƙusa akan gwiwoyina ne sannan za ki haƙura".
"To ai ni babu abin da ka yi mini ba". Na yi maganar ina ƙoƙarin wucewa ya yi saurin shan gabana.
"Na razana ki mana baiwar Allah. Kuma kin san an ce tsorita musulumi haramu ne. Don Allah ki furta ki yafe min raina zai fi samun nutsuwa, don akan hanyar nake zan yi tafiya mai nisa. Ki taimaka min kar na tafi da haƙƙin wani a kaina".
Na cira kai na yi masa kallo guda kafin na janye idanuna"kamar yadda na gaya maka ba ka yi mini komai ba, amma tun da ka matsa na haƙura Allah ya kiyaye hanya ya kai ka lafiya". Ina gama maganar na wuce na soma tafiya cikin sauri saboda lokaci ya riga ya ƙure kafin na iso har Malam Suleiman ya shigo ajinmu ana karɓan hadda na shiga na zauna na buɗe ƙur'anina, duk yadda na so biya karatun lamarin ya gagara wai cire wando ta kai, ji na yi kamar ba a taɓa karanta mini wajen ba a kaf cikin rayuwata. Ina ta ƙoƙari haɗa kalmomin amma ya ci tura har aka iso kaina na tashi na isa gaban Malam Suleiman, sai dai na gaza karanta ko aya guda sai faman kame-kame nake yi.
"Amatullah anya ki biya karatun nan a gida kuwa?".
Na yi ƙasa da kaina don ni kaina na san duk abin da zai fito daga bakina a lokacin ƙarya ne.
"Malam na yi amma......". Kafin na ƙarisa ya dakatar da ni"koma ki zauna idan an fito salla ki zo ki same ni".
"To Malam". Na amsa da shi ina tashi daga wajen na koma mazaunina na zauna, na kwantar da kaina akan desk ban ɗago ba har sai da aka fita sallan asr Rauda ta taɓo ni na tashi muka fito muka yi alwala, muna iddar da sallan na wuce wajen Malam Suleiman.
Yana zaune a cikin staff room na shigo na zauna, sai da ya gama rubutun da yake yi kafin ya gyara zamansa yana fuskanta na da kyau ya soma magana.
"Amatullah mene ne yake damunki? Me ye ya yi miki zafi a cikin rayuwar nan?".
Kalamansa suka daki ƙwaƙwalwata tare da raunana zuciyata, na ɗau tsawon lokacin wani bai yi mini irin wannan tambayar ba.
"Babu abin da yake damuna Malam".
"Kar ki yi ƙarya don fuskarki ta riga da ta bayyanar da labarin zuciyarki. Amatullah dole akwai wani abun, tun da ga shi har ya fara taɓa karatunki, duk wanda ya sanki a makarantar nan ya san ki ne saboda dalilai guda biyu na farko ƙoƙari da mayar da hankalin da kike da shi akan karatu na biyu kuma ladabi da biyayyarki".
"Babu komai akwai dai matsalolin rayuwa ne na yau da kullum, kuma yanzu a rayuwar nan kowa da irin na shi kalan damuwar".
Ya yi ɗan jim kafin can ya yi magana cikin taushin harshe"na fahimta kuma ina fatan haka ɗin ne. Kar ki saka komai a ranki ki miƙa wa Allah dukkan lamuranki don shi kaɗai ne zai iya magance miki matsalolinki, kin ga rayuwar nan kowa da na shi matsalar idan kika ji na wani sai ki ji na ki ko kashi ɗaya bai kai cikin kashi ɗarin nasa ba. Kar ki bari ki ɓata shekarun da kika yi a baya kuma karatu mussamman yanzu da aski ya zo gaban goshi".