Sashe 56
Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"Malama idan har kin san cewa bakinki ba zai furta alkhairi ba, to zai fi dace ki yi shuru". Anty Zulaihatu ta mayar mata da martani a zafafe tana jan hannuna muka shige cikin ɗakinmu, muka tarar da Umma tare da wasu mata biyu muka yi sallama sai dai cikinsu babu wanda ya amsa mana muka shigo muka zauna, ina satan kallon Umma sai dai ko kaɗan ban ga ta yadda na yi tsammanin ganin ta ba. Na yi zaton kamar yadda mutuwar Abba ta girgiza ni haka ita ma lamarin zai taɓa zuciyarta sai dai kash! Ashe kallon kitse nake yi wa ruwa hange dala nake yi wanda ya ke ba shiga cikin birni ba ne.
"Hafsatu ya muka ji da haƙuri?".
"Alhamdulillah". Ta amsa da shi tana yatsina fuska.
"Na zo mu yi magana da ke ne amma na ga ki na da baƙi, na ce ko za mu shiga cikin uwar ɗaka?".
"Babu inda zan motsa daga idan kuka riske don haka duk abin da za ki faɗa ki faɗe ta a nan. In ba za ki iya ba kuma ki wanke ƙafafunki ki koma inda kika fito ba lalle ba dole ai".
Lamarin ya ƙullar da Anty Zulaihatu har sai da ta tanka"Maman Amatullah izuwa yanzu kam ai na yi tunanin komai ya wuce, ya kamata mu bayar da hankali mu fuskanci abin da yake gabanmu. Mu haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen nemawa yarinyar nan nutsuwa da farin cikin ko don daidaituwar rayuwarta". Umma ta gyara zamanta tana fuskantar Anty Sawwama da kyau tare da faɗin.
"Ku yanzu har ku na tunanin cewa a cikinku akwai wanda ya fi ni son Amatullah ne, na fi kowa son ganin rayuwarta ta gyaru shi yasa nake yi duk waɗannan abubuwan. Wallahi duk daren duniya ba na iya runtsawa saboda baƙin cikin abin da wannan yarinyar ta aikata, ni kaɗai na sa irin son da nake yi wa Amatullah ko har kun manta irin wahalar da sha yayin raino da haihuwarta".
Kalamanta ya sanya idanuna kwaranyowa da hawayen da na daÉ—e ban tsiyayar ba, na ja gwiwoyina na gurfana a gaban Umma na É—aura kaina a bisa kan cinyoyinta.
"Umma na tuba ki yafe mini wallahi ni ma shaida ce na san cewa ki na yi mini irin soyayyar da babu wanda zai yi mini kwantan-kwacinta a cikin duniyar nan. Amma zan so ki zauna ni dama na yi miki bayanin abin da ya faru wallahi ba laifina ba ne ƙaddara ce ta faɗa mini Umma kin san da hankali da tunanina ba zan aikata wannan abun ba, don Allah ki sassauta mini ki ba ni mafaka na sama sassauci a wajenki".
"Amatullah na riga da na cire ki daga cikin raina, tun ranar da abin kunyar da kika aikata ya bayyana na sallamar da ke a duniya......".
Da hanzari Anty Sawwama ta katse ta"kar ki yi mata baki Hafsatu ki saurare abin da za ta ce da ke don Allah".
"Babu wani abun da ya yi saura wanda za ta sanar da ni da ban ji shi a bakin al'umman gari ba. Amatullah na sallamar da ke ga duniya daga yau ni Hafsatu ba ni da wata ɗiya a duniya, don haka ki tashi ki bi su kar ki ƙara zuwa inda nake balle ni ma baƙin cikinki ya kashe ni kamar yadda ya yi silar mutuwar ubanki".
"Innalillahi wa inna ilahirin raji'un! Allahumma ajirni fi musibati. Ya Allah ka kawo mana sauƙi wannan lamarin".
Wani irin kuka nake yi mai raunana zuciyar mai saurare babu shiri na É—ago kaina sakamakon dukan da na ji kalaman Umma sun yi mini. Duk yadda na so na yi magana na kasa yin haka sai ma tashi da na yi da sauri har ina haÉ—awa da gudu-gudu na bar cikin É—akin kai tsaye É—akin su Amira na nufa na zube akan kujera ina ci gaba da kukan.
"Innalillahi wa inna ilahirin raji'un! Amatullah me ya faru kuma? Tun ɗazu nake so na je ɗakin nakun sai kuma Ummata ta ce ai da baƙi a ciki shi yasa na dakata". Na tsinkayo muryar Amira cike da kulawa yayin da take zama kusa da ni tare da ɗago kaina. Ta soma goge mini hawayen da suka ɓata mini fuskana.
"Amira me yasa munanan abubuwan suke faruwa da ni? Da farko an yi mini fyaɗe ciki ya bayyana a jikina, Abba ya mutu da baƙin cikin da na yi silar cusa masa sannan yanzu Umma uwar da ta haife ni ta furta cewar ta sallamar da ni ga duniya ba ta buƙatar gani na a kusa da ita. Amira ya ya ake so na yi rayuwata? Allah ma fa da kansa mu na yi masa laifi ya yafe mana to me ya sa Umma ta kasa fahimta na akan wannan lamarin balle har ta dube ni da idon rahama, jin ƙai tare da tausayi. Wallahi zuciyata ta soma saƙa mini wani mungun tunani, duk abin da na aikata kar ku ga laifina wallahi na rasa mafita ne".
Na yi zancen cikin wani irin yanayi mai wahalar fassaruwa cikin kalmomin baki, Amira ma kanta sai da hawaye suka zubo mata daga idanunta. Ta kasa lallashina illan kukan da muka haÉ—u ni da ita mu na yi.
"Duk laifina ne Amatullah ni na fara kawo shawaran zuwa gidan Tasalla. Kuma bayan abin da ya faru ya faru na goyi bayan a ɓoye lamarin. Komai ya faru ni ce sila ina ma a kaina wannan abun ya faru ba ke ba Amatullah ina ma....". Ba ta ƙarisa ba sakamakon kukan da ya ƙwace mata mai ƙarfin gaske muka haɗu duk mu biyun muna yin sa. Ummanta ta shigo ta tsaya a kanmu na tsawon lokaci kafin ta yi magana.
"Haƙuri za ku yi don duk abin da ya faru kuka ko shiga tsananin damuwa ba ya gyara shi. Ƙaddara ce da ta riga fata cikin mu babu wanda zai iya guje mata". Ta dafa kaina kana ta ci gaba"Amatullah ki yi haƙuri na san cewa ke mai haƙuri ce da juriya da kuma tawakkali. Duk layin nan da ke ake buga misali da kwatance idan za yi maganar tarbiyya, kamun kai, hankali da kuma nutsuwa kuma ina da tabbacin kowa zai shaide ki cewar hakan ba halinki ba ne. Ki tashi ki share hawayenki ki fito ku tafi ga su can suna jiranki a waje".
Na kuma fashewa da wani kukan mai tsuma zuciya ni nake yi zuciyata tana yi mini hura. Muka fito har zaure hannuna saƙale cikin na Amira suna fitowa waje muka ga dandazon mutanen unguwa ƙwansu da ƙwarƙwatansu wai duk su zo kallona.
"Dube ta simi-simi kamar na Allah ashe kura ce lulluɓe da fatan akuya. Allah dai wadaranki da kuma mungun halinki, ga shi yanzu ki kashe mahaifinki har lahira Allah sarki! Malam Manniru bawan Allah da ya san irin annobar da zai haifa kenan na tabbatar da ya gwammace ya rayu har ya koma ga Allah babu ɗa babu jika".
Kalaman da suka sauƙa a na'urar naɗan sautina kenan da ya gigita ni numfashina ya soma sama da ƙasa, ashe kowa zargina yake yi da akan mutuwar Abba?. Da ƙyar na isa wajen napep ɗin Anty Zulaihatu ta tsayar na shiga na zauna.
"Amatullah don Allah kar ki aikatawa abin da zai cutar da ke ko ya jefa mu gabaɗaya cikin wani ruɗanin. Ki yi ƙoƙari ki cire damuwa a cikin ranki in sha Allah gobe da sassafe ni ma zan zo, kuma Mansur ma ya ce a yi miki gaisuwa kafin ya zo da kansa". Kaina kawai na jinjina mata muka rabu, ko da muka isa gidan Anty Sawwama su Yaya Alhassan sun hi matuƙar baƙin cikin abin da ya faru Umar sai da ya yi kuka tsabar takaici.
A daren ranar sai da aka ƙara mini ruwa leda biyu aka yi mini allurai da sauran magungunan da na sha. Ina kwance a ɗaki kamar gawa Yaya Alhassan ya shigo ya yi mini sannu na amsa can ƙasa maƙoshina.
"Amatullahi ki cire damuwar komai daga cikin ranki in sha Allahu duk wanda ya yi miki wannan abun sai na nemo sa ko ina ya shiga a cikin duniya sai kuma na tabbatar da cewar an hukunta sa, bisa tanadin doka. In sha Allah farin cikinki zai dawo za ki rayu cikin nutsuwa da walwala kamar yadda kike a baya".
"Yaya Alhassan ni da samun farin ciki mun yi hannun riga".
Ya yi hanzarin katse ni"zan dawo miki da farin cikinki zan tabbatar da cewar duk matsalalolinki sun kau. Amatullahi ki ba ni dama in har kin aminta da ni kuma ki na jin za ki iya rayuwar aure da ni to zan iya ki".
Take na wartsake na tashi na zauna ina kallon sa cikin son tabbatar da abin da kunnuwana suka jiyo mini.
"Ƙwarai da gaske ni zan aure ki don ba zan ba ri aure ya kai ki inda za a wulaƙanta ki ko a yi miki gori bisa ƙaddarar da Allah ya ɗaura miki ba".
"Yaya Alhassan rayuwarka tsarkakkiya ce babu wani mummunan abu a cikin tarihinka. Don Allah kar ka gurɓata tarihinka ta hanyar haɗa jini da ni".
"Hafsatu ya muka ji da haƙuri?".
"Alhamdulillah". Ta amsa da shi tana yatsina fuska.
"Na zo mu yi magana da ke ne amma na ga ki na da baƙi, na ce ko za mu shiga cikin uwar ɗaka?".
"Babu inda zan motsa daga idan kuka riske don haka duk abin da za ki faɗa ki faɗe ta a nan. In ba za ki iya ba kuma ki wanke ƙafafunki ki koma inda kika fito ba lalle ba dole ai".
Lamarin ya ƙullar da Anty Zulaihatu har sai da ta tanka"Maman Amatullah izuwa yanzu kam ai na yi tunanin komai ya wuce, ya kamata mu bayar da hankali mu fuskanci abin da yake gabanmu. Mu haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen nemawa yarinyar nan nutsuwa da farin cikin ko don daidaituwar rayuwarta". Umma ta gyara zamanta tana fuskantar Anty Sawwama da kyau tare da faɗin.
"Ku yanzu har ku na tunanin cewa a cikinku akwai wanda ya fi ni son Amatullah ne, na fi kowa son ganin rayuwarta ta gyaru shi yasa nake yi duk waɗannan abubuwan. Wallahi duk daren duniya ba na iya runtsawa saboda baƙin cikin abin da wannan yarinyar ta aikata, ni kaɗai na sa irin son da nake yi wa Amatullah ko har kun manta irin wahalar da sha yayin raino da haihuwarta".
Kalamanta ya sanya idanuna kwaranyowa da hawayen da na daÉ—e ban tsiyayar ba, na ja gwiwoyina na gurfana a gaban Umma na É—aura kaina a bisa kan cinyoyinta.
"Umma na tuba ki yafe mini wallahi ni ma shaida ce na san cewa ki na yi mini irin soyayyar da babu wanda zai yi mini kwantan-kwacinta a cikin duniyar nan. Amma zan so ki zauna ni dama na yi miki bayanin abin da ya faru wallahi ba laifina ba ne ƙaddara ce ta faɗa mini Umma kin san da hankali da tunanina ba zan aikata wannan abun ba, don Allah ki sassauta mini ki ba ni mafaka na sama sassauci a wajenki".
"Amatullah na riga da na cire ki daga cikin raina, tun ranar da abin kunyar da kika aikata ya bayyana na sallamar da ke a duniya......".
Da hanzari Anty Sawwama ta katse ta"kar ki yi mata baki Hafsatu ki saurare abin da za ta ce da ke don Allah".
"Babu wani abun da ya yi saura wanda za ta sanar da ni da ban ji shi a bakin al'umman gari ba. Amatullah na sallamar da ke ga duniya daga yau ni Hafsatu ba ni da wata ɗiya a duniya, don haka ki tashi ki bi su kar ki ƙara zuwa inda nake balle ni ma baƙin cikinki ya kashe ni kamar yadda ya yi silar mutuwar ubanki".
"Innalillahi wa inna ilahirin raji'un! Allahumma ajirni fi musibati. Ya Allah ka kawo mana sauƙi wannan lamarin".
Wani irin kuka nake yi mai raunana zuciyar mai saurare babu shiri na É—ago kaina sakamakon dukan da na ji kalaman Umma sun yi mini. Duk yadda na so na yi magana na kasa yin haka sai ma tashi da na yi da sauri har ina haÉ—awa da gudu-gudu na bar cikin É—akin kai tsaye É—akin su Amira na nufa na zube akan kujera ina ci gaba da kukan.
"Innalillahi wa inna ilahirin raji'un! Amatullah me ya faru kuma? Tun ɗazu nake so na je ɗakin nakun sai kuma Ummata ta ce ai da baƙi a ciki shi yasa na dakata". Na tsinkayo muryar Amira cike da kulawa yayin da take zama kusa da ni tare da ɗago kaina. Ta soma goge mini hawayen da suka ɓata mini fuskana.
"Amira me yasa munanan abubuwan suke faruwa da ni? Da farko an yi mini fyaɗe ciki ya bayyana a jikina, Abba ya mutu da baƙin cikin da na yi silar cusa masa sannan yanzu Umma uwar da ta haife ni ta furta cewar ta sallamar da ni ga duniya ba ta buƙatar gani na a kusa da ita. Amira ya ya ake so na yi rayuwata? Allah ma fa da kansa mu na yi masa laifi ya yafe mana to me ya sa Umma ta kasa fahimta na akan wannan lamarin balle har ta dube ni da idon rahama, jin ƙai tare da tausayi. Wallahi zuciyata ta soma saƙa mini wani mungun tunani, duk abin da na aikata kar ku ga laifina wallahi na rasa mafita ne".
Na yi zancen cikin wani irin yanayi mai wahalar fassaruwa cikin kalmomin baki, Amira ma kanta sai da hawaye suka zubo mata daga idanunta. Ta kasa lallashina illan kukan da muka haÉ—u ni da ita mu na yi.
"Duk laifina ne Amatullah ni na fara kawo shawaran zuwa gidan Tasalla. Kuma bayan abin da ya faru ya faru na goyi bayan a ɓoye lamarin. Komai ya faru ni ce sila ina ma a kaina wannan abun ya faru ba ke ba Amatullah ina ma....". Ba ta ƙarisa ba sakamakon kukan da ya ƙwace mata mai ƙarfin gaske muka haɗu duk mu biyun muna yin sa. Ummanta ta shigo ta tsaya a kanmu na tsawon lokaci kafin ta yi magana.
"Haƙuri za ku yi don duk abin da ya faru kuka ko shiga tsananin damuwa ba ya gyara shi. Ƙaddara ce da ta riga fata cikin mu babu wanda zai iya guje mata". Ta dafa kaina kana ta ci gaba"Amatullah ki yi haƙuri na san cewa ke mai haƙuri ce da juriya da kuma tawakkali. Duk layin nan da ke ake buga misali da kwatance idan za yi maganar tarbiyya, kamun kai, hankali da kuma nutsuwa kuma ina da tabbacin kowa zai shaide ki cewar hakan ba halinki ba ne. Ki tashi ki share hawayenki ki fito ku tafi ga su can suna jiranki a waje".
Na kuma fashewa da wani kukan mai tsuma zuciya ni nake yi zuciyata tana yi mini hura. Muka fito har zaure hannuna saƙale cikin na Amira suna fitowa waje muka ga dandazon mutanen unguwa ƙwansu da ƙwarƙwatansu wai duk su zo kallona.
"Dube ta simi-simi kamar na Allah ashe kura ce lulluɓe da fatan akuya. Allah dai wadaranki da kuma mungun halinki, ga shi yanzu ki kashe mahaifinki har lahira Allah sarki! Malam Manniru bawan Allah da ya san irin annobar da zai haifa kenan na tabbatar da ya gwammace ya rayu har ya koma ga Allah babu ɗa babu jika".
Kalaman da suka sauƙa a na'urar naɗan sautina kenan da ya gigita ni numfashina ya soma sama da ƙasa, ashe kowa zargina yake yi da akan mutuwar Abba?. Da ƙyar na isa wajen napep ɗin Anty Zulaihatu ta tsayar na shiga na zauna.
"Amatullah don Allah kar ki aikatawa abin da zai cutar da ke ko ya jefa mu gabaɗaya cikin wani ruɗanin. Ki yi ƙoƙari ki cire damuwa a cikin ranki in sha Allah gobe da sassafe ni ma zan zo, kuma Mansur ma ya ce a yi miki gaisuwa kafin ya zo da kansa". Kaina kawai na jinjina mata muka rabu, ko da muka isa gidan Anty Sawwama su Yaya Alhassan sun hi matuƙar baƙin cikin abin da ya faru Umar sai da ya yi kuka tsabar takaici.
A daren ranar sai da aka ƙara mini ruwa leda biyu aka yi mini allurai da sauran magungunan da na sha. Ina kwance a ɗaki kamar gawa Yaya Alhassan ya shigo ya yi mini sannu na amsa can ƙasa maƙoshina.
"Amatullahi ki cire damuwar komai daga cikin ranki in sha Allahu duk wanda ya yi miki wannan abun sai na nemo sa ko ina ya shiga a cikin duniya sai kuma na tabbatar da cewar an hukunta sa, bisa tanadin doka. In sha Allah farin cikinki zai dawo za ki rayu cikin nutsuwa da walwala kamar yadda kike a baya".
"Yaya Alhassan ni da samun farin ciki mun yi hannun riga".
Ya yi hanzarin katse ni"zan dawo miki da farin cikinki zan tabbatar da cewar duk matsalalolinki sun kau. Amatullahi ki ba ni dama in har kin aminta da ni kuma ki na jin za ki iya rayuwar aure da ni to zan iya ki".
Take na wartsake na tashi na zauna ina kallon sa cikin son tabbatar da abin da kunnuwana suka jiyo mini.
"Ƙwarai da gaske ni zan aure ki don ba zan ba ri aure ya kai ki inda za a wulaƙanta ki ko a yi miki gori bisa ƙaddarar da Allah ya ɗaura miki ba".
"Yaya Alhassan rayuwarka tsarkakkiya ce babu wani mummunan abu a cikin tarihinka. Don Allah kar ka gurɓata tarihinka ta hanyar haɗa jini da ni".