← Book details Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 13 OF 58

Sashe 13

Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Ko kaɗan ba ki ɓata min rai ba Amatullah. Sai dai na ji ciwon ƙaryan da kika haɗa kai da Amira kuka yi min wanda na san ba halin ki ba ne hakan. A ina kuka haɗu da shi? Tsawon wani lokaci ya ɗaura yana zuwa wajenki? Sannan me yasa Amira ta ce ita ya zo nema bayan sunanki aka ambata?".

Tagwayen ajiyan zuciya na sauƙe da ya tafiyar da kukan da nake yi na koma sauƙe ajiyar numfashi akai a kai, tamkar wacce ta fafata a gasar fidda zakaran gwajin dafi na tseren gudu.
Sai da na fizgo numfashina da yake maƙalewa a ƙirji kafin na amsa masa jerin tambayoyin da ya watsa mini a lokaci guda.
"Wallahi ban taɓa ganin sa ba sai yau, ɗazu ne muka haɗu a inda na kai talla shi ne muka sama matsala da wasu ƴan mata har suka zubar mini da kunun kuma suka neme ni da faɗa. Shi ya hana su dukana kuma ya biya ni asarar da suka yi mini ya dage akan sai ya rako ni don tabbatar da na iso lafiya saboda sun yi ikirarin tare ni a wani wajen. Abba na rantse maka har da Sarkin da ya halicci sammai da ƙassai bakwai ba tare da wani ko wata ya kawo masa taimaka ko ba wannan shi ne gaskiya yadda muka haɗu da shi. Kuma ko yanzu ma sai da na roƙe sa akan kar ya ƙara zuwa yana nemana na ƙara tabbatar masa ma ba zan ƙara kai talla inda muka haɗu da shi ba. Amira kawai ta taimake ni ne don ta ga yadda gabaɗaya na rikici na kasa magana".

"Na yarda da ke Amatullah ba ni da shakka ko kokonto akan duk abin da zai fito daga bakinki. Ba da son raina ko aminvewata kike wannan tallan ba amma da iznin Allah na kusa kawo ƙarshen abun. Ki kwantar da hankalinki ki dinga taka-tsantsan da mutane don yanzu duniyar ta lalace".

"In sha Allah zan kiyaye". Kansa kawai ya gyaɗa bayan ya tallafo kaina na tashi daga jinginar da na yi a jikin ƙafafunsa. Ya miƙe zai shige ciki na yi hanzarin riƙo gefen rigarsa.
"Abba kar ka je ka kwanta da tare da bakinka ya furta kalmar yafiya gare ni ba. Hakan zai jefa ruhina cikin ƙunci da rashin nutsuwa".
Kyakykyawar ajiyar zuciya ya sauƙe da har sai da na jiyo sautin fitarsa kafin ya ce da ni wani abun da ya sanyaya sashin ruhina da nake jin kamar ana watsa mini garwashin wuta.

"Ko ban yi amfani da kalmomin baki wajen furta kalmar yafiya a gare ki ba. Zuciya ba za ta yi dogon zango tana dakon fushi da ke ba Amatullah. Na yafe miki kuma daman ba ki ɓata mini ba".
Sakakken ajiyan zuciya na sauƙe ina jin kamar an sauƙe mini wani ajiyan da aka yi mini a ƙirjina na kasa magana sai kuka, lallashina ya yi sosai har na dawo daidai kafin na yi masa sai da safe na cike cikin ɗakin. Lokacin Umma har ta yi bacci, ta kwanta a gefenta sai dai sam bacci ya ƙi kawo mini ziyara sai da na raba dare kafin na sama na iya runtsawa.

Washe gari haka na tashi da matuƙar ciwon kai ko kaina ban son ɗagawa balle na buɗe idanuna. Ina kwance a inda na yi sallan asuba, Umma ta ɗago labulen tana ƙira na na tashi na zauna kafin ta fesar da abin da yake tafe da ita.
"To ki tashi ki zo ubanki yana ƙiranki". Na tashi na rufa mata baya muka fito tare, na zauna a ƙasa yayin da ita kuma ta zauna a kujerar da Abba yake zaune kusa da shi. Shuru ya ratsa wajen kafin Umma ta buga tsaki.

"Ka tara mu ka ce za ka yi magana, mun zo kuma ka saka mu a gaba kana kallonmu. Idan ba ka da abin da faɗa ne ka sallame mu, don ni ina da abin da ya fi wannan zaman muhimmanci wanda zan yi". Wataƙila da Umma ta sama tagomashin kasancewa cikin mata masu lura da karanta ma'anar shuru da rabe-rabensa da ta fahimci shuru da kallon da Abba ya yi mata, yana bayyanar da ɗacin da maganarta ta yi masa ne. Amma sai dai kash! Ko a jikinta wai an mintsini kakkaura ko gizau ba ta yi ba.

"Na tara ku duka ne domin na sanar da ku wani hukuncin da na yanke wannan yake kamar umarni ne a gare ku". Umma ta katse shi ba tare da ya dire zancen ba"to muna jiranka sai ka tafi kai tsaye ga saƙon da kake son isarwa ai, ba sai ka tsaya kana wani kame-kame ba".

"Ina so na sanar da ku a cikin satin nan za mu tashi daga gidan nan. Don haka tun yanzu ku duk shirin da za ku yi".

Tun kafin ya gama zancen Umma ta yi zumbur ta miƙe tamkar wacce aka yi wa alluran doki, ta yi sakeke tana kallon Abba baki sake. Ta toshe kunnuwanta tana cewa"ban gane abin da kake faɗa ba Manniru? Ka yi bayani da harshen da zan fahimta ƙwaƙwalwata ta gaza amsar sauƙon da kake ƙoƙarin isar mata. Mu bar gidan nan mu je ina? Ina muke da shi bayan nan? Ko kuma kawai so kake ka yi amfanin da ikon da kake da shi a kanmu ka tozarta mu a idon jama'a?".
"Yadda kunnuwanki suka jiyo miki haka na faÉ—a Hafsatu za mu tashi daga gidan nan tashi na har abada. Ki fara shirya kayanki tun yanzu".

"Wallahi ba ka isa ba. Ba zan taɓa zuba ido wannan abun ya faru ba, Manniru anya kana lafiya kuwa ƙwaƙwalwarka ba ta sama matsala ba?".

"Zan ga tsakanin ni dake waye yake auren wani. Na yi rantsu ba zan yi kaffara ba ki isa ki sauya min ra'ayi akan wannan lamarin ba, dole ne mu bar gidan nan don ba zan zuba ido ina kallo tarbiyan Æ´ata tana lalacewa ba. Duk gini da foundation É—in da na yi don inganta rayuwarta yana rugujewa ba, ba zan laminta ba".
"Da an yi magana ka ce ƴa ƴa kamar ka fi kowa ƴa ko a kanka kawai aka fara haihuwa. Duk mazauna gidan nan ba su ce tarbiyyan ƴaƴansu zai lalace ba sai kai uban masu ba da tarbiyya. Wai tarbiyyan nan kai ne kake yin ta ko taimakon Allah ne? Manniru kar ka biye zuciyarka ka cutar da mu babu gaira babu dalili, ka sani na sani daga kai har ni duk ƙoƙarinmu wajen tarbiyya ba zai iya sa yarinyar nan ta kasance cikin amintattu ba, face sai Allah ya dafa mana. Iyaye nawa ne wanda suka kasance manyan malaman addini amma ƴaƴansu suka fi kowa kangarewa da lalacewa ba. Ga misali nan Manniru Allah ya buga mana akan Annabi Nuhu wanda shi annabin Allah ne ma amma iyalinsa suka kauce hanyar da yake. Shi kuma sai ya ce me ye a Ubangiji?".

ÆŠan jim Abba ya yi don ta gama É—aure sa da jijiyar jikinsa.
"Ko me ye za ki faɗa barin gidan nan wajibi ne. Saboda gujewa faruwar abubuwa da yawa don haka na gama magana, kina da zaɓi biyu ko ki haɗa kayanki mu tafi tare ko ki yi zamanki a nan ki ci gaba da ɗaukar nauyin kanki kamar yadda kike ikirarin kina yi". Yana dasa aya a nan ya fice ransa a matuƙar ɓace. Ihu Umma ta kurma kamar za ta yi hauka ta zube ta yi zaman ƴan bori.
"Shikenan na shiga uku na lalace! Ni kake yi wa kora da hali Manniru? Dole na tashi tsaye a cikin gidan nan. Na rantse ba za mu taɓa tashi daga gidan nan ba ko za ka haɗiye zuciya ka mutu dare ɗaya......".
Ba ta ƙarisa ba na yi hanzari tashi na je na rufe mata bakinta.
"Don Allah Umma ki yi haƙuri. Ki dinga yi salati zuciyarki za ta yi sanyi, ba daɗe irin wannan maganar ko kaɗan".
Ta ture hannuna kafin ta ce"Amatullah ya ya zan yi da raina? Idan muka bar gidan nan ina za mu dosa? Sanin kanki ne ba mu da wani matsugunin da ya wuce nan, a nan ne kawai asirinmu zai rufu amma ubanki ya dage sai ya tona mana asiri sai ya fallaso sirrinmu ga duniya. Wallahi ba zan taɓa barin hakan ya faru ba tashi ki ɗauko min hijabina na fita".

"Umma ina za ki je a cikin wannan halin da kike ciki?".

"Wajen Malam zan je don shi kaÉ—ai ne zai share min hawaye nan take".
[7/18, 11:05 AM] Maimunatu Iyam: *DAFIN HARSHE*

©️ Maimuna Tijjani Iyam

_______________________________________

Page 1️⃣1️⃣

Ganin tana ƙoƙarin tashi ya sani saurin cafko hannunta ina yi mata magiya"don girman Allah Umma ki rufa mana asiri kar ki je ko'ina. Da bakinki fa yanzu ki ka ce Abba yana so ya tona mana asiri amma asalin tonon silili zai faru ne daga loakcin da kika je kika baje wannan lamarin a wani can da daban da yake bakewa da malunta yake aikata abin da ba shi ne ba". Zafin marin da ta sauƙe mini a gefen kuncina na hagu shi ya sani haɗiye ragowar zancen ba tare da na furzo shi waje ba, kafin na yi aune ta ƙara sauƙe mini wani marin a karo na biyu da sai da ya tursasa mini sakin ƙara. Tsabar azaba da zogin da fatar wajen yake yi mini da nake jin tamkar ruwan tafasasshen ɗanyen dalma aka watsa mini.
Chapter 13 · 0% Book details